Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 56

Chapter 56

Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

fad'i jin muryar Hibbah cikin rud'ewa ta mik'e tsaye tayo kan Hibbah Wanda itama tuni tayi kan baba da masifa take magana "muryar wa nake ji kamar ta Hibbah me ya dawo dake garin nan baki ji gargad'in da nayi miki ba ko?" Kausar dake gefenta tace "itace Hibbah ce kuma ta dawo ne don ceto rayuwar mahaifinta daga hannun azzalumar mace irinki" cikin d'aga murya Inna tace "ke Kama kanki ki nutsu ban kasa dake ba da zaki d'auka" ta kalli Hibbah da tayi tsuru tsuru ta fizgota ta d'aga hannu zata mareta Faheem ya rik'e hannun "karki sake ki tab'a min mata, kina tab'ata sai dai a kwashi gawarki" "idan ba'a kwashi gawata ba za'a kwashi gawarta yanzu ba sai gobe ba, wallahi alkawarin da na d'auka saina cika shi na indai Hibbah ta dawo garin nan sai na kasheta" Faheem ya tura Hibbah kusa da Inna "gata nan don Allah ki kashe ta ki kasheta nace" Inna ta buga mai wani mugun kallo "ku jirani nan da mintuna kad'an" ta zari mayafinta ta fita tana masifa. Hibbah ta kuma saka kuka Kausar ta janyota jikinta "kiyi shiru Hibbah babu abinda Bawa ya isa yayiwa d'an uwansa Bawa wanda Allah bai nufa zai same shi ba ki kwantar da hankalinki babu abinda ta isa ta yi miki" Rahmatu dake d'aki jin fitar Inna ta fito don Inna hanata fitowa tayi ta d'auko kwano cike da ruwa ta mik'awa su Abba, Abba ya amsa ya d'iba a hannunsa ya safa a fuskar baba, baba baiyi motsi ba ya kumayi nan ma shiru har sai da yayi sau uku baba bai motsa ba nan hankali su ya mugun tashi har sun yanke shawara d'aukar shi zuwa asibiti sai kuma.............. *by* *Mamyn Najmah* [10/26, 9:27 PM] Maman Najma Author P1: 📝🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *RAYUWA* page5⃣1⃣ *NA* *MAMYN NAJMAH* 🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA* *Kulawarku da damuwa da littafina ya sani cikin farin ciki na gode sosai, masu kirana a waya basu samu ba da masu min magana ta what's up kuyi hakuri ina busy ne.* Sai kuma baba ya ya sauke wata sassanyar ajiyar zuciya a hankali ya fara bud'e idanunsa ya sauke su akan na Daddy shima da Daddy kallon sa yake zuciyarsa duk ta karaya hawaye na zuba a idanunsa. A hankali baba ya d'ago hannunsa ya d'ora a saman fuskar daddy ya shiga goge masa hawayen yana masa murmushi "ka daina kuka d'an uwana ban Sonka da zubar hawaye" Daddy ma murmushi yayi "ai dole ne Mukhtar munyi kewar rashinka munyi kuka har mun gaji munsa a ranmu ka rasu sai yanzu muka sami Labarin kana raye kaga kuwa dole mu zubda hawaye farin ciki" baba yayi murmushi yana kallon duk mutanan wajen babu Wanda ya Sani a cikinsu banda momy da mamy sai kuma Faheem da yake ta kallo yana son gano waye? Ya dubi momy da mamy da suke ta matsar k'walla "autar hajiya da matar Yaya ku daina kuka Dan Allah ku matso gare ni" a hankali suka matsa kusa da baba ya rumgume su tamkar yara suka fara kuka yana d'an bubbuga bayansu. Baba ya d'ago kansa yana kallon Abba suna yiwa juna murmushi da kuma hawaye a fuskokinsu, baba ya d'an saki su momy ya kuma duban Abba "babban Yaya wai wad'annan duk 'ya'yana ne?" Abba ya d'aga masa Kai "naka ne duka Abban Aysha" mamaki ne ya bayyana a fuskar baba yace "Abban Aysha wace Aysha? Ni banga Aysha ba da hajiya suna ina?" Da sauri daddy ya d'ago kansa jin mutanen da k'anin nasa yake tambaya hawayensa suka tsananta zuba, Abba shima hawayen yake yi yace "kayi hakuri Abban Aysha sanadin cutar da ta sameka a wannan daren Allah yayiwa hajiya rasuwa sanadiyyar hawan jininta daya tashi, Aysha kuma tashin hankali ne yasa ta nak'uda a lokacin ta haifo 'yarta mace shine aka saka mata sunan Aysha saboda ita ma Aysha bata rayu ba." Inna lillahi kawai baba yake furtawa zuciyarsa na masa zafi a sannu rayuwar da sukayi da mahaifiyarsa da matarsa ya Fara tunowa sai kuma hawaye suka fara sauka a saman fuskarsa yasa hannu yana gogewa yana mai yi musu addu'ar samun rahamar ubangiji. Su Kansu su daddy hawayen suke yi saboda tuno mutuwar da sukayi sai filin tsakar gidan yayi shiru sun d'auki wasu lokuta a haka kafin baba ya katse shirun da cewa yana murmushi "wace Ayshan a cikinsu? Duk sun d'auko kama iri d'aya" daddy ya dubi Aunty "Aysha matso Gare shi zo ga mahaifinki" Aunty ta taso ta zo wajen baba, shi kuwa baba cikin happy ya rumgume ta k'aunarta na ratsa duk ilahirin jikinsa ita kuwa Aunty kuka take ga k'aunar mahaifinta na shigarta sun d'auki lokaci k'amk'ame da juna baba ya d'ago yana kallon su Kausar "yarana ku matso gare ni kuzo naji d'umin jikin yarana" ya fad'a yana bud'e hannayensa, matsowa su duka suka yi banda Hibbah dake gefe kusa da Umma tana ta kuka zuciyarta cike take da tsoron abinda inna ta fita yi shima Nawaz bai tashi ba yana jikin Hibbah yana goge Mata hawaye wai tayi shiru . Su Saudat kuwa baba had'asu yayi ya rumgume su yana mai jin k'aunar 'ya'yan 'yan uwan nasa na ratsa shi, sun dauki lokaci kafin ya sakesu ya kalli Faheem "babban Yaya kar dai kuce wannan ne Faheem nawa" da murmushi Abba t?yace "shine Abban Aysha" baba ya dubi Faheem yana dariya "lallai na dad'e rabona da ku dubi fa yadda ka zama babban mutum, ina Haisam kuma?" "Haisam yana Abuja acan yake aiki" "to Allah ya bada sa'a ina dai fatan yanzu kun ajiye iyali ko?" Faheem ya d'an Sosa k'eya yana duban Abba. Cikin dariya Abba yace "ka fad'a masa mana" Faheem ya kuma sunkui da kai daddy yayi dariya "duk sunyi aure dashi da Haisam d'in shi ya auri k'anwarsa Kausar da ka tafi Rukayya na da cikinta har ma da d'ansu Nawaz yanzu kuma ya kuma k'aro wata a sanadiyyarta ne muka gano inda kake." Baba ya dubeshi da mamaki "wace ita?" "Hibbah ce 'yar wajenka" mamaki ne ya kuma bayyana a fuskar baba gumi ya fara keto masa "Hibbah ina kike matso gare ni kiyi min afuwa ki yafe min muzgunawar dana miki ke da mahaifiyarki, kinga Rahmatu yadda mahaifiyarta ta cutar mata da *RAYUWA* ko?" Hibbah ta matso kusa da baba Nawaz ya biyota tace "baba baka yi min komai ba na yafe maka" "ina Ummanki Hibbah?" Ta nuna masa Umma. Ya yunk'ura zai tashi daddy ya ruk'oshi, baba yayi murmushi don ya gane dalilin rik'eshin da daddy yayi "nafa samu sauki babu inda ke min ciwo" daddy ya sake shi ya k'arasa gaban Umma "kiyi hakuri Aysha ki yafe Min lefin da nayi miki don Allah" "nasan ba lefinka bane na yafe maka Allah ya yafe mana" baba yaji dad'i tace "na gode Aysha" ya dubi Nawaz "wannan ne abokin nawa?" Ya fad'a yana janyo Nawaz jikinsa ya kalli Faheem dake ta sunna Kai "Faheem wai kunyata kake ji ne? Ni ba surukinka bane fa" Faheem yayi murmushi yana kuma k'asa da kansa. Baba yayi murmushi yana mamakin yadda Faheem shi bai yadda ba kunyar shi yake ji. Abba ya d'anyi gyaran murya "k'aramin k'anina

Table of Contents

Chapters

63 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});