Chapter 47
Chapter 47
take..........." Wayarta ce ta katseta ta lalubo wayar a cikin jakarta sunan da ta gani ne a kan screen d'in wayar yasa zuciyarta bugawa ta kalli Faheem, yace "waye yake kiranki?" Tayi ajiyar zuciya bata amsa sa ba ta d'aga wayar don taga ta kusa katsewa. Bai ma Bari tayi magana ba ya hauta da fad'a "kun kyauta Aysha wato saboda bakwason Faruq ya auri yarinyar da yake so shine kuka had'a baki keda Faheem kuka k'ulla tuggunku yaje ya aureta kafin naje nema masa ko, to kuzo yanzu Ku sameni a gida ina jiranku," "kayi hakuri Daddy Allah ya huci zuciyarka, amma Daddy wallahi bawai don bama son Faruq ya aureta bane dama tuntuni Faheem yake sonta kuma yaje ya sami mahaifiyar yarinyar ta bashi ita.........." Cikin fad'a Daddy ya katseta "rufe min baki munafukan banza kiyiwa shi Faheem d'in waya kuzo tare tunda ni na kirashi yak'i d'auka" Aunty ta kwantar da murya "kayi hakuri Daddy ba k'in d'auka yayi ba muna asibiti ne bashi da lafiya kuma na kira Abba da su mamy na fad'a musu" "ba wata rashin lafiya da yake yi duk k'arya ne kuzo yanzu ina jiranku idan ba haka ba ranku zaiyi mummunan b'aci" yana gama fad'in haka ya kashe wayar. A sanyaye ta sauke wayar daga kunnenta, Faheem ya kalleta "me Daddy yace miki?" Ta sauke ajiyar zuciya "Yaya Daddy yak'i saurarata yace muje yanzu yana nemanmu, na fad'a masa muna asibiti baka da lafiya yace k'arya ne idan bamu zo ba ranmu saiya b'aci" Faheem ya yunk'ura ya tashi zaune "kije ki Kira min Dr Umar yazo ya sallame mu muyi sauri muje," "a'a Yaya baka jin dad'i fa har yanzu ka bari ni naje ni kad'ai" ya kalleta "haba Aysha so kike na sab'awa su Daddy ne? Ai rashin lafiyata ba komai bace akan sab'a musun da zanyi don haka kiyi abinda nace ki Kira min Dr" ta kalleshi tana tausayawa Yayanta, lallai ba k'aramun so yake yiwa Hibbah ba a dalilinta ya samu ciwon zuciya, gashi kuma ya d'aukarwa kansa hukuncin barinta. Ta mik'e da niyyar zuwa kiran Dr sai gashi ya shigo, suka gaisa ya shiga duba Faheem d'in bayan ya gama yayi 'yan rubuce rubucensa ya juya zai fita, Faheem yace "Dr inason ka sallameni yanzu pls" da mamaki sosai akan fuskar Dr Umar yace "saboda me? Kasan illar ciwon da kake tattare dashi kuwa? Kayi hakuri ka zauna a nan zaka fi samun kulawa" Faheem yad'an dubeshi "kayi hakuri Dr Daddy ne yanzu yayi min waya yana son ganina da gaggawa, pls ka taimaka ka sallameni yanzu karna sab'a umarninsa" Dr yayi shiru yana yaba biyayyar Faheem ga jyayensa "to shikenan Aysha biyoni office" Ya fita Aunty tabi bayansa suka je office ya bata takardar sallama da ta wasu magunguna da ake buk'ata tayi masa godiya ta dawo d'akin ta had'a kayansu suka fito daga asibitin. Wata bak'ar mota ce mai bak'in glass tayi parking a gabanta aka bud'e gidan baya tare da fizgota cikin motar aka rufe motar ta fita a 360. Cikin tsoro Aunty ta kalli Faheem tace "Yaya wannan ba Hibbah bace?" "Itace yi sauri mubi bayan motar" da sauri suka shiga motar Aunty ta figi motar a 360 suka bi bayan motar sai dai ina motar................... *by* *Mamyn Najmah* [10/26, 9:26 PM] Maman Najma Author P1: 📝🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *RAYUWA* page4⃣4⃣ *NA* *MAMYN NAJMAH* 🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION* D.B.W.A *DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA* Motar tuni ta b'ace suka kalli juna ita da Faheem wanda hankalinsa ya mugun tashi, ta karyar da kai "Yaya pls ka kwantar da hankalinka kaga baka da lafiya, insha Allah ba abinda muke zargi bane zai faru da Hibbah" ya gyad'a kai "muyi sauri Daddy yana jiran mu" Aunty ta juyar da kan motar suka nufi gidansu. Babu kowa a babban parlor direct parlor'n Daddy suka nufa Faheem ne a gaba Aysha tana biye dashi suka shiga cikin parlor'n, dukkanin ilahirin gidan ciki manyan gidan iyayen nasu kenan. Faheem ya shigo da sallama Abba da su momy da mamy ne suka amsa Daddy ko kallonsa baiyi ba yana zagaye parlor'n, Faheem ya gaishesu Aunty ma haka nan ma Daddy bai kallesu ba. Faheem ya matso kusa da inda Daddy yake "don Allah Daddy kayi hakuri wallahi bani da niyyar.............." Katse shi yayi ta hanyar yarfa masa wani mugun mari cikin fad'a ya fara magana "Faheem ni zaka wulakanta ka nuna ban isa da kai ba, saboda kuna yiwa d'an uwanku bak'in cikin karya auri yarinyar da yake so shine kuka zage kai da Aysha kuka k'ulla makircinku har ka aureta ko? To baka isa ba tunda shima ya rasata dole kaima ka rasa, aikin banza da wofi yara sai bak'in cikin tsiya ni banma yarda da wannan auren ba tunda shi Abban Janan shine walilinku kuma ba zama yake yi ba za'ayi aure ne babu waliyyi?" Faheem ya sunkui da kansa yanaji rad'ad'i mai zafi a zuciyarsa baya so yaga ran iyayensa ya b'aci sam. Abba dake zaune ya kalli Daddy cikin kwantar da murya yace "Daddy'n Faruq ka tsaya kayi bincike akan abinda ya faru kafin ka yanke hukunci, ni d'innan nine nayiwa Faheem waliyyi aka d'aura auren nan, ya kirani a waya yake fad'amin damuwarsa nasan Faheem akwai shi da zurfin ciki tunda har ya fad'amin damuwarsa to abin ya dameshi, ni na bashi shawarar yaje wa mahaifiyar yarinyar da maganar Allah bashi nasara daya fad'awa mahaifiyarta ta bashi aurenta a lokacin tace a d'aura, ya kuma kirana a waya ya fad'amin cewa ta amince kuma tace ya turo yanzu a d'aura auren Allah yasa ranar na shigo kano naje aka d'aura auren, don nima ina sauri ban ma shiga mun gaisa nayi mata godiya ba saidai na barwa mijinta sak'on gaisuwar. Bayan an d'aura auren mai makon naga Faheem yana farin ciki sai naga ya shiga damuwa na tambaye shi menene kuma yake damunsa, yace min yana tunanin yadda zaka d'auki zancen k'aro auransa bada saninka ba ga kuma Kausar da yayowa itama abokiyar zama ba shiri, na nuna masa karya damu indai Kausar ce, kai kuma zanyi maka bayanin komai Allah bai bani ikon kuma dawowa kano ba sai jiya da kayi min waya mukazo yau. To kaji abinda ya faru Daddy'n Faruq tun kafin ka fad'a min Faruq nason yarinyar nan Faheem yake dakon son ta a dalilin maganar da kayi musu jiya shi kuma ya yankewa kansa hukuncin sadaukarwa da Faruq ita bayan irin son da yake yi mata, sonta ne da fargabar rabuwa da ita ga kuma dakon sonta da yayi yasashi kamuwa da ciwon zuciya" daddy yayi shiru yana sauraronsa yace "naji kuma na fahimta amma yarinyar nan Faruq ya shaida min shi take so kuma ita ta amince da aurensa, don haka ke Aysha kece mai number ta ki kirata yanzu tazo ta shaida mana wa take so a tsakaninku, oya Aysha kirta kisa muna ji" Abba ya kuma kallonsa "haba Daddy wai sai yaushe ne zaka daina nunawa yaranka bambanci? Ka dinga yi musu adalci mana" "kayi hakuri Abba ka kyaleshi ai dama yayi niyyar barwa d'an uwan nasa ita to Dan nace a kirata ta zab'i zab'inta ai ba lefi bane" Abba ya gyad'a kai kawai dama
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63