Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 15

Chapter 15

Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel 1,207 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

had'a abubuwan da wasu manyan babies din ma basu dashi duk da cewa yanxu suka fara tasawa abubuwan nata, amma tana da diri mai kyau da d'aukar hankali, ya tuno yadda ya ganta d'aure da towel sai ya kuma matse pillow gam a jikinsa, haka yayi ta tunaninta har dare ba mafita daya rufe idanunsa ita yake gani ga wata muguwar kasala da sha'awar kasan cewa da mace data saukar masa kasa jurewa yayi, ya tashi ya shiga toilet ya sakarwa kansa ruwa na wani lokaci kafin ya fito ya tsala wanka cikin k'anan kaya ya feshe jikinsa da turaruka masu kamshi ya zari key din motarshi ya nufi club. Su kuwa su Hibbah sunje sun kaiwa tailor d'inkunan yace nanda kwana biyar zai kawo, daganan Aunty tace zasu wuce super market zasuyi siyayya, wani babban shop na kayan mata suka shiga Aunty ta yiwa Hibbah siyayya ta had'a da kud'in hannunta duk tayo mata siyayya haka suka d'auko hanyar gida da kaya nik'i nik'i. Suna shigowa gida ana kiraye kirayen sallah don haka kai tsaye Aunty tabi Hibbah bangarensu suka ajiye kayan anan ma sukayi sallah sannan Aunty ta shiga nuna mata yadda zatayi amfani da komi har pad tace mata wannan idan kina al'ada shi zaki dinga amfani dashi ta nuna mata yadda ake sakawa. Sai bayan isha'i malam Jamil yazo bayan sun gaisa dasu momy ya tashi ya nufi d'akin da suke karatun a ciki, su Saudat suka mike kowa ya d'auki kayan karatunsa suka bi bayansa dayake hadda sukeyi a wajensa suna zuwa suka shiga Bashi hadda. Aunty tazo tayi kiran Hibbah suka tafi d'akin, bayan sun gaisa da malam Aunty tayi masa bayanin komai yace "ba matsala Aysha insha allah za'ayi yadda kikace kuma gobe in allah ya kaimu su tafi tare dasu Safiyya makarantar sai ayi mata komai zan karbi sunanta yanzu", Aunty tayi masa godiya ta koma ciki. Su Saudat sai harararta suke yi suna jin haushin yayar tasu wai akan me zata dinga had'a su da 'yar aiki. Malam Jamil ya kalli Hibbah yace "mene sunanki?" Hibbah tace "sunana *Hibbah Mukhtar Muhammed*" malam ya girgiza Kai alamar gamsuwa yace "izufinki nawa?" "Izufina sha bakwai" Hibbah ta Bashi amsa yace "hadda kikayi ko kuma biye?" Hibbah tace "hadda nayi," malam ya kalleta yace "zaki iya karanto min naji?" Kai ta d'aga, ya kalli Safiyya da take shirin fara Bashi haddarta yace "kiyi mana hakuri Safiyya bara ta biyamin naji," Safiyya tace "to malam" ya kalli Hibbah yace "bismillah" nan Hibbah ta shiga biya masa har ta gama yayi mamakin karatunta yarda take da tajwidi take fidda kowane hukunci ya jinjina mata, ya kuma yi mata k'arin karatu, saida ya tambaye ta shafi take so ko rabin shafi tace yadai biya mata kawai shafi d'aya ya biya mata, saida yaji ta iya sannan ya k'arbi haddar Safiyy........... *by* *Mamyn Najmah* [10/26, 9:22 PM] Maman Najma Author P1: 📝🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *RAYUWA* page2⃣2⃣ *NA* *MAMYN NAJMAH* 🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION* D.B.W.A *DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA* *Idan kaji ana a marmatsa giwa ce ta iso, gaba dai gaba dai uwar gayya karo da karo sai rago waye zai bada tauranshi _AYSHA ALIYU GARKUWA_ ke kad'ai kike baki da sa'a.* *D*a haka malam Jamil ya gama biya musu karatu ya tafi. Hibbah tana zuwa d'akinsu tayi ta bibiyar karatun batayi bacci ba sai da ta tabbatar ta haddace sannan ta samu tayi bacci mai dad'i cike da mafarkin ummanta, tunda take bata tab'a yin barci akan abu mai taushi ba kamar nayau don katifar tana da taushi. Ta Saba k'arfe hud'u da rabi take tashi, haka yauma ta tashi, ta d'auro alwala tazo ta rik'a jero nafilfili tana godiya ga allah bisa wannan ni'ima dayayi mata. Kiran sallah assalatu ne ya d'agata daga wajen ta tada sallar asuba, bayan ta idar ta tashi Hadiza tayi itama sallah bayan ta idar ta zauna tana jan carbi, ita kuwa Hibbah karatunta ta bibiya sannanta d'ora da azkar na safiya dayake ta haddace su. Sai gari ya fara haskr suka fito da Hadiza ta nunnuna mata inda zata share bayan tagama shara ta nuna mata yadda ake mopping da goge kayan kallo, ita kuma ta shiga kitchen don had'a breakfast. Bayan ta gama gyara ko ina ta koma nasu d'akin ta gyara ta wanke toilet, Hadiza ta bata turaren wuta tace tasa a parlor kafin su tashi ta gyara musu can saman, Hibbah ta amsa tasa tuni parlor ya d'auki k'amshi. Kasan cewar yau weekend ne da wuri yaran gidan ke tafiya islamiyya don k'arfe takwas na safe suke tafiya, hakan yasa bayan sun gama breakfast suka shirya zasu tafi. Hibbah tasan tare zasu tafi don haka tayi wanka da wuri ta shirya, powder ta shafa tasa kwalli kamar yadda taga jiya aunty tayi mata, bata da hijjab d'in sakawa, ta d'auko nata tasa ta fito tayiwa Hadiza sallama. A parlor taga aunty Aysha dayake yau sunday bata da lectures, a zaune tana kallo, taje tace "aunty barka da safiya kin tashi lpy?" Murmushi aunty tayi tace "lafiya lau Hibbah ya kwanan bakunta?"murmushi Hibbah tayi tare dacewa lpy aunty" gani tayi aunty tad'an harareta tace "kinyi kyau amma kin bata kwalliyarki da wannan hijjab d'in, cireshi kizo muje sama na baki wani," tana gama fad'in haka taja hannun Hibbah suka hau sama Hibbah na binta a baya, Saida suka Fara zuwa ta gaishe da momy sannan aunty ta bata wani Hibbah Mai hannu tasa yayi mata mugun kyau, sannan ta sauko suka tafi. Safiyya tayi gaba tace "nifa wallahi bazan jera da 'yar k'auyen nan ba haka kurin ajina ya zube," Saudat tace "ai kuwa adai yanayin dressing d'in datayi babu Wanda zaice Mata 'yar k'auye, kuma ni wallahi ma k'awance zamu kulla da ita naga tana ja," kamar wadda aka zabura Safiyya tace "ke dawa zaku kulla k'awancen?" Saudat tayi dariya tace "da Hibbah mana" tsaki Safiyya ta buga tare dayin gaba abinta. Su Hibbah kuwa suka jero da Saudat, Hibbah ta rikee Hisham suna tafiya Saudat tana ta janta da hira har suka isa makarantar. Anyiwa Hibbah komai kuma an kaita ajinsu Saudat, ta Fara d'aukar darasi. Haka *RAYUWA*r Hibbah ta cigaba a gidan su Auntyn tata cikin kulawar Auntyn ta, mommy da kuma Hadiza. Sosai take jin dad'in zama a gidan, malam Jamil ma ya Fara koya Mata karatun boko kuma yaga kwazonta don idan ya biya mata nan da nan k'wak'walwarta take d'auka, makarantar islamiyyar tasu malamai nata yabon k'wazonta. Yau saura kwana biyar Faruq ya koma school, kuma yau ya kama ranar Friday, gidan ya kasance babu kowa sai Hadiza da Hibbah. Wannan al'ada ce tar 'yan gidan duk ranar Friday suke tafiya family house nasu dake zoo road, tun safe suke tafiya basa dawowa sai dare, Aunty Aysha kuwa bata zuwa sai yamma saboda yanayin karatunta. Da misalin k'arfe hud'u na yamma bayan sallar la'asar kenan Hibbah da Hadiza sun shiga kitchen zasu fara had'a dinner dayake tare sukeyin komai na girki kuma alhamdulillah Hibbah tana k'ok'ari wajen ganin ta fahimci komai, Faruq ne ya shigo fuska a tsuke sai wani muzurai yake kamar gaske ya kalli Hibbah wanda tunda ya shigo jikinta ya Fara kyarma, yayi mata duban wulakanci yace "keh!!" Da sauri

Table of Contents

Chapters

63 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});