Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 41

Chapter 41

Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

tuna ka kusa illata yarinyar nan tun da ka d'ana mata tarko Allah ya tserar da ita, shine ka b'ullo ta wannan sigar to babu kai babu auren Hibbah 'yar mutunci bata cancanta da kai ba, kawai kaje ka cuceta da zalincinka na 'yan bariki, nasan bazata soka ba koda bata fito k'arara ta nuna maka k'iyayyarta ba don tana jin nauyi a matsayinka na k'anina, bazan goyi da bayanka ba don nasan daka gama cin moriyar gagga zaka yarda k'wauronta, tayi miji mai sonta don Allah Jabeer iyayenta sunsan da maganar auren bazan tab'a yadda ka dagula zancen ba wallahi, babu kai babu ita zan ganta itama sai naci ubanta shashashar banza kawai bata San inda yake mata ciwo ba, wato ita bata tausayawa kanta bata nemawa kanta 'yanci." Ya mik'e yana wani irin huci iyakar fusata ya fusata fuskar nan tayi jawur "Ashe ke mak'iyiyata ce a yau na tabbatar ni ba jininki bane ai hannunka baya rub'ewa ka yanke ka zubar duk lalacewata ni naki ne, kince ni d'an iskane uban bariki ne ni ba d'anta ba, wallahi saina auri Hibbah idan yaso ki dinga yankar naman jikina kina k'onawa ko kuma ki fad'i ki mutu don bak'in ciki. Wallahi zamusa k'afar wando d'aya dake koda zamu k'ulla gaba ta har duniya ta nad'e, aurena da Hibbah ba fashi don ra'ayi nane kuma babu abinda kika isa kiyi." Yayi awon gaba da center table d'in dake parlor'n glass cups d'in dake kai suka fad'o suka farfashe, ko juyiwa baiyi ba yayi tafiyarsa don ya d'au zafi. K'ofar fita sukayi karo da Sagir mijin Aunty Aysha saida ya gogi kafad'arsa, yaja baya yana kallon Faruq da mamaki, gaba yayi ko waigowa baiyi ba bare ya kula sa, ya kad'a kansa ya shiga ciki yana mamakin Faruq, ya zauna tayi masa sannu da dawowa. Ya gano tana da damuwa cikin sigar rarrashi ya matsota "haba amarsu na kiyi hakuri nasan fad'a kukayi da d'an uwan naki, kinsan su sai ana hakuri dasu a hankali zai canza" ta numfasa "kayi hakuri naga har bangajeka yayi, Faruq fitinannen yaro ne ya damu family'n mu, kullum bama shiri jituwa dashi sai fad'a don na fad'a masa gaskiya ni kuma bazan fasa fad'a masa ba sai dai muyi ta fad'a dashi" Ta fad'a mishi abinda ke faruwa. Yayi murmushi "ku mata wani lokacin tunaninku kamar na k'aramin yaro yake, Aysha ai ba'a fad'in abinda ba alkhari ba a lamarin aure idan ita kuma yarinyar tace shi take so sun had'a kansu fa, yaya zakiyi sai kiji kunya kuma har abada zai ta kallonki da wannan abin tunda bake kika haifeta ba na dai gane abinda kike hango mata, kina sonta kuma ke kin fita sanin halin d'an uwanki amma kamata yayi ki nuna goyan bayanki ki tayashi murna, ba yadda zakiyi dashi naka nakane saidai kiyi masa ta masa add'a da fatan auren ya zama sanadiyyar shiryuwarsa." Aunty ta numfasa "my dear abinda ka fad'a hakane amma karka manta fa akwai maganar aure a tsakanin yarinyar nan da Jabeer kuma har manya sun shiga sa rana kawai za'ayi sai yanzu zasu zo min da maganar banza daga ita har shi, ai itama zan sameta ne saina ci mata mutunci" "kibi abin a sannu, kum idan ita Hibbah tace bata son Jabeer ai dole ya hakura ko zakiyi mata dole ne?" Ta girgiza "to kingani kawai saidai muyi fatan Allah ya zab'a abinda yafi alkhari" "to ameen muje ka watsa ruwa ko?" Suka mik'e a tare suka shiga ciki. Faruq kuwa yana fita daga gidan Aunty cikin b'acin duk inda ya wuce sai an dube shi kamar mai shirin barin garin, gudu yake sosai a mota bai tsaya a ko ina ba sai a night club, idanuwannan a hargitse banda masifa babu abinda yake ji ransa a mugun b'ace yake ji yake kamar ana tsigar gashin kansa, tabbas da yana da bindiga da sai yayi gangancin harbin Aunty Aysha mene amfanin mak'iya a duniya ya tabbatar yanzu bashi da makiyi kamarta. Kid'a ne yake tashi kamar zai tsaga ginin wajen, ya zauna yana muzurai kamar wani kumurcin maciji, ya d'auko sigari ya kunna mata wuta wai ko zai rage zafin abinda yake ji, ya dubi mashaya barasa kala daban daban yakanji a wajen abokansa wai giya na gusar da mummunan tunani da kauda bak'in ciki ga d'an karan dad'i amma shi bai tab'a sha'awar Shanta ba, ya kansha ganye da wasu kwayoyin shima tun lokacin yana secondary school tare da tak'adiran abokansa da suke kiran kasu bad boys, amma tuni ya manta dasu shidai burinsa yaga macen da yake ra'ayi kawai yayi mu'amalarsa da ita. Hankalinsa ya kasu biyu ya kalli barasar yana kwad'ayin lasawa ya wurga idanunsa yana kallon kangararrun matan dake shawagi wurin duk baiga Wanda ransa ya biya ba don haka ya yafito hadimin wajen da hannunsa. Da harshen turanci ya gaisheshi cikin ladabi "barka da dare me kake buk'ata" ya mik'a mishi wata takarda da jerin nau'ikan barasa, ya karb'a yana d'an nazari sai ya yatsuna fuska "kowanne ka kawo" don bai san wanda xai zab'a ba. Ya dire tray da manyan kwalaban giya masu sanyi, ya d'auki guda d'aya idanunsa sun shige ciki ya k'ura mata idanu, yana tunani zuciyarshi yasha ko karya sha, ya sha kawai koya huce zuciayarsa ta raya masa. Yana kaiwa bakinsa ta karb'e kwalbar, ya cira ido da k'yar ya dubeta, siririya ce doguwa Fara Sol, tana sanye da wani bulun skirt iya cinyarta da wata 'yar figigiyar riga data manne a jikinta. Ta zauna gami da rik'o hannayensa da wani asirtaccen murmushi akan fusakarta tuni tayi awon gaba da tunaninsa, Rita kenan yana son yarinyar don tasan ta kanshi sosai da ranshi ya b'aci zata sauko da fushinsa. Ya kewaya hannunsa a k'ugunta suka mik'e suka hau sama don cin karensu babu babbaka. **** Bak'in hadarin daya taso da wata iska mai k'arfi, sannan ruwan ya sauko yana tarwatsewa bisa glass d'in motar yana sauraron wak'ar Dr Mamman shata, yau dai yana cikin annashuwa yana tunanin maganganun Umman Hibbah sun sashi farin ciki har yana hangen wata *RAYUWA* a gaba da zasuyi dole ne yayi azumin godiya ga Allah daya cika masa burinsa ya mallaka masa abinda yake matuk'ar so,shikenan ta zama mallakinsa. "Karka damu komai nufi ne na Allah, nayi farin ciku da jindad'i tsakaninku da yarinyar nan amanace, wannan ita ce k'auna domin Allah sai addu'ar alkhari, Allah ya tabbatar da alkhari zan fad'awa Alhaji yanzu daya shigo ayi komai a yau d'in nan a gama." Yayi ajiyar zuciya ya tuna maganganun masu dad'in sauraro, wannan wani sirri ne daga shi sai Allah sai kuma Umma data share masa hawayensa, tura ce takai bango har yaji bazai iya zama da kashi a ciki ba don baya maganin yunwa, don haka ita kad'ai tasan maganar ya dad'e da gamsuwa da halin dattako irin nata, don yasan zata taka rawar gani ta magance masa matsalar data addabeshi shi, shiyasa ya kai mata ziyarar gaisuwa da rok'on iri kamar uwa ya d'auketa ba suruka ba. Yana parking ya k'ura mata idanu ta cikin glass d'in motar, tana rik'e da lema tana tarar ruwan saman a wani bokitin roba shi kuma Nawaz yana Tara nashi

Table of Contents

Chapters

63 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});