Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 49

Chapter 49

Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

a kaina ashe duk yaudarace yana sone ya aure ni daya samu abinda yake so sai ya rabu dani, don yaga bani da gata bani da galihu yanson ya wulakanta min rayuwa don kawai ya cika burinsa akaina." Sai kuma ta fashe da wani kuka mai ban tausayi, Aunty ta janyota jikinta "Hibbah kiyi shiru Allah yana tare dake shine gatan mu kuma nima ina tare dake" da hawaye tab a kan fuskarta ta d'ago tana kallon Faheem dasu mamy sannan ta dubi Aunty "na gode Aunty da kulawar da kika nuna min Allah ya saka da alkhari, Aunty wai da gaske ne Daddy ne mijina yaushe aka d'aura auren?" "Waya fad'a miki Hibbah?" Ta d'anyi shiru "Faruq ne ya fad'a min, don Allah Aunty idan da gaskene ki rok'a minshi ya sake ni don wallahi Aunty bazan iya auren mijin Aunty Kausar ba kuma na d'auki Daddy kamar uba taya zan iya zaman aure da mutumin da nake jin nauyinsa nake bashi girma fiye da kowa a duniyar nan Aunty kuyi hakuri don Allah bazan iya zaman aure bashi ba" maganar Hibbah ta d'aga hankulansu duka musamman ma Faheem da yaji wani abu ya tokare shi, Aunty ta dubeta duk tayi sanyi "Hibbah ki tausayawa rayuwar d'an uwana wallahi Yaya yana sonki sosai wannan rashin lafiya da kika ganshi duk a sanadinki yake yi saboda Daddy yace lallai saiya rabu dake......" Nan Aunty ta kwashe komai ta fad'a mata, Hibbah ta kafa ta gumi ta ma kasa cewa komai tana tunanin wannan hukuncin na ubangiji, wato abinda baka tab'a zato ba saikaga ya sameka, matsayin da baka tab'a tunanin zaka taka ba sai Allah ya baka shi. K'ofar aka bud'e Kausar ce rik'e da kwandon abinci Saudat ta rik'o hannun Nawaz ita da Safiyya suna biye da ita, da gudu Nawaz yaje ya rumgume ta "Aunty kinga daddy bashi da lafiya baki zo kin dubashi ba kin gudu gidan ummanki, Aunty nima bazan kuma zama a wajen momy ba idan zaki tafi ki tafi dani zan biki" ta k'ank'ame Nawaz tana shafa kansa tace "Nawaz ba inda zan kuma kowa ina tare da kai" yayi tsallan murna "da gaske Aunty Hibbah?" Ta gyad'a masa kai ya kuma rumgume ta. Kausar ta ajiye kayan ta tsaya tana kallon su cike da tausayin kanta tabbas tayiwa kanta da yanzu duk wannan soyayyar da Nawaz yake yi Mata da ita zai yiwa. Ta kalli Faheem shima kallonsu yake yi yana murmushi, yaji dad'in kalaman Hibbah hakan na tabbatar masa data amince zata zauna dashi kenan, su Aunty ma dasu momy sai murmushin jindad'i sukeyi. Hibbah kuwa ta kasa d'aga ido ta dubi Kausar saboda nauyinta da take ji, kuma bazata iya kallon idanun Aunty tace bata son d'an uwanta ba hakan zai zama kamar butulci da cin fuska shiyasa bata da wani zab'in daya wuce ta amince da auren, ikon Allah kenan wai akanta har Faheem yake da ciwon zuciya gashi a gadon asibiti a kwance yana ciwon so. Saudat ta k'araso kusa da Hibbah tana murmushi cikin sigar tsokana tace "Aunty Hibbah matar Yaya" dukansu suka sa dariya banda Kausar da duk abin duniya ya isheta duk danasani da nadama ta addabi zuciyarta, yayin da Safiyya take bak'in cikin faruwar wannan abun take kuma jin tsanar Hibbah a zuciyarta sai wurga mata harara take yi. Hibbah tayiwa Saudat hararar wasa, Saudat tayi kamar bata gani ba ta cigaba "mamy da Aunty nasan kune akan komai don momy ba shiga zatayi ba, yanzu yaushe ne zamu sha bikin babban Yaya kusan mune manyan k'awaye" wani bak'in ciki ya tsayawa Safiyya ji take kamar taje ta doki Saudat, Hibbah tayi k'asa da kanta cike da kunya da kuma jin wani iri don gani take kamar cin fuska ne abinda Saudat take yi, tana yi ne saboda Kausar wanda ita tana ganin rashin dacewar hakan. Aunty tace "Kai Saudat irin wannan zumud'i haka ki bari su Daddy su dawo sai su tsaida mana rana" Saudat ta gyad'a kai "sai mu fara shiye shirye kenan." Tsayuwa ta gagareta ta samu gefen gadon Faheem ta zauna kanta a k'asa tana tunani yanzu shikenan Faheem ya zama nasu su biyu, ta d'ago kai ta dubeshi shima ita d'in yake kallon yana tausaya mata don yasanta akwai zafin kishi yayi mamaki ma da bata wani tashi hankalinta ba sosai yayi mata murmushi, ta kawar da kanta gefe. Su Abba ne suka shigo da sallama suka amsa musu tare da yi musu sannu da zuwa, Abba ya dubi inda Hibbah take Nawaz yana zaune akan cinyarta kanta yana k'asa yana murmushi yace "surikarmu ki d'ago fuskar taki mu gani mana kinsa mana yaro kwanciya ciwon so, naga ma ya samu lafiya saboda ya ganki" cikin sigar barkwanci Abba yake maganar saboda Abba akwai shi da barkwanci, Hibbah ta kuma k'asa da kanta cikin kunya, su Daddy dasu momy sai murmushi suke yi Faheem kuwa shima k'asa yayi da kansa don jin nauyin maganar Abba. Saudat tace "surikar su Abba ki d'ago kanki su ganki" ta fad'a tana mata dariya, mamy tace "kai Saudat kin takurawa surikata fa, zan fara rama mata" momy tace "gaskiya kam Saudat kin takurata da yawa ke a haka ake Matar Yayan?" Daddy yayi dariya "nifa na k'osa naga fuskar wannan mai sa'ar data sace min zuciyar Faheem haka har ya kasa nutsuwa saboda rashinta" su aunty suka kwashe da dariya. Gaban Hibbah ne ya shiga fad'uwa jin muryar da bazata tab'a mantawa ba zuciyarta ta shiga harbawa da sauri ta d'ago kanta don tabbatar da muryar da taji, a hankali ta d'ago kanta ta zubasu akan Daddy cikin mugun hargitsi da rikici ta tashi tsaye tana kallon daddy murya na rawa tace "baa.......baa? Baba kaine?" Jin muryarta ya hargitsa Abba muryar da yafi so a duk duniya kuma bazai tab'a manceta ba har *Abadan* ya jiyo cikin fargaba yace "Aysha....." Hibbah ganin fuskar Daddy yasata zubewa a k'as............... *by* *Mamyn Najmah* [10/26, 9:27 PM] Maman Najma Author P1: 📝🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *RAYUWA* page4⃣6⃣ *NA* *MAMYN NAJMAH* 🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA* Aunty ce tayi saurin tarota ta fad'o jikinta, Faheem besan sanda ya diro daga gadon ba yayi wajenta da sauri yana ambaton sunanta su momy ma suka matso suna jijjigata, mamy ce ta d'auko ruwa ta fara shafa mata a fuskarta. Abba kuwa da hanzari ya fita ya kira Dr, suna shigo Hibbah tana farkawa Dr ya k'araso ya shiga dubata ko da wata matsala, ya gama dubata ya tabbatar musu da lafiyarta sannan ya fita. Hibbah tayi shiru kawai kallon Daddy take yi tana son ta gano wani abu game da Daddy tana kuma tambayar kanta, me ya kawo babanta birni dama babanta yana da aure a birni amma bai tab'a gayawa su Inna ba kuma akace bai tab'a haihuwa ba sai akanta idan haka ne su Aunty Aysha kuma 'ya'yan waye? Bata da amsoshin wad'an nan tambayoyin nata ya zame mata dole ta tambayi daddy don shi kad'ai ne zai iya amsa mata wad'annan tambayoyin. Daddy da Abba sun shiga tunani Daddy ya tafi wani tunanin akan Hibbah yana son yasan wani abu game da wannan razanar da tayi ta ganinshi don ta bashi tsoro, yayin da Abba kuma ya tafi tunani

Table of Contents

Chapters

63 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});