Chapter 50
Chapter 50
wacece wannan mai irin murya da kamannin k'anwarsa Aysha kodai 'yar Aysha ce? Ya tambayi kansa sai kuma ya girgiza kai a'a, a iya saninsu Aysha tun tana k'arama ta b'ata kuma baya tunanin yanzu tana raye, lallai ya zame masa dole yasan ko wacece ita. To amma me ta sani game da Daddy da har zata suma don tagansa mene a tsakaninsu? Dukkansu su biyun basu da amsoshin tambayar su don haka Daddy ya d'ago Kai ya dubi Hibbah dake kwance itama duk tunani ya dameta. "Hibbah ki fad'a min mene dalilin da yasa don kin ganni kika tsora har kika suma?" Hibbah tayi shiru tana nazari kenan baba bai ganeta ba kodai ba babanta bane kama ce? Ta dubi su momy duk jira jira sukeyi tayi magana, cikin yanayin tsoron da bai saketa ba tace "Baba, baba baka gane ni ba Hibbah ce fa, Hibbah 'yarka daka kora" sai kuma hawaye ya fara bin fuskarta. Daddy cikin yanayin nuna damuwa yace "Hibbah kiyi hakuri bani bane Wanda kike fad'a" Hibbah ta rik'e kanta don ya fara mata nauyi wannan wace irin *RAYUWA* ce ka haifi 'yarka amma ka kasa gane ta? Me ta canza da baba zai kasa ganeta? Faheem dake kusa da ita ya dubeta cikin kulawa "Hibbah kiyi mana bayani yadda zamu fahimce ki, kinsamu a cikin hargitsi" Hibbah hawaye nabin fuskarta damuwarta ta k'aru "babu komai Daddy zan cigaba da rayuwata ba tare da babana ba dama tun tasowata nafi sabawa da ummana akan babana saboda baya sona bai damu da rayuwarmu ba........." Sai kuma ta saki wani irin kuka. Daddy ya kasa fahimtarta ya kasa gane maganganunta, balle kuma Abba da idan tayi magana yake jin gabansa yana bugawa. Faheem kam wannan kukan da take yi jinsa yake har cikin ransa, Aunty ta janyo Hibbah jikinta tana rarrashinta. D'akin yayi tsit sai sanyin AC dake ratsa d'akin, Abba ne ya katse shirun da cewa "Hibbah dukkanmu nan bama gane abinda kike fad'a, amma ko zaki fad'a mana sunan mahaifin naki may be mu ganeshi," da kamar ba zatayi magana ba saboda kukan da yaci k'arfinta, dak'ar ta iya rage kukan cikin muryar kuka tace " *MALLAM MUKHTAR MUHAMMAD*" da hanzari Daddy ya nunata "kina nufin kice min Mukhtar yana raye!?" Daddy ya fad'a cike da rud'ewa, kansa ne ya fara juya masa a hankali ya kama gefan gadon ya zauna yana jin k'aunar d'an uwansa tana kuma ratsa zuciyarsa. Abba ma gefen Aunty ya zauna yana kuma tuno rayuwarsu ta baya gefen zuciyarsa kuma cike yake da rud'ani don ya k'osa yaji wacece Hibbah so yake yaji asalinta don kamar da suke yi masa da Aysha k'anwarsa ta b'aci. su mamy da momy ma suna cike da rud'ani ashe Hibbah'yarsu ce basu sani ba. Faheem, Aunty, Kausar dasu Hibbah sun kasa fahimtar komai game dat abinda yake faruwa, Faheem cikin damuwa ya dubi su Daddy "Daddy don Allah kuyi mana bayanin abinda yake faruwa mun kasa gane abinda kuke nufi" Daddy yayi shiru k'aunar d'an uwansa na kuma ratsa zuciyarsa ya dubi su Faheem "Faheem yau zan bayyana muku komai game da rayuwarmu." Kowa ya maida hankalinsa kan Daddy, ya cigaba da cewa "Kamar yadda kuka taso a garin kano muma a cikinsa muka taso iyayenmu mu uku suka haifa sab'anin yadda kuka sani, nine babba sai mai bina Mukhtar sai kuma mamynku Rukayya, mun taso cikin so da k'aunar iyayen mu sun jajirce wajen ganin sun inganta rayuwarmu ta hanyar bamu ilimi na duka b'angarorin. Ni da Abbanku mun taso tare kamar tagwaye komai tare mukeyi, haka ma Mukhtar da abokinsa Ibrahim sam ba'a jin kan d'aya daga cikinmu, muna level 4 a jami'ar bayero university kano inda muke karantar business administration dukanmu, Allah yayiwa mahaifinmu rasuwa mutuwar data gigitamu dukkannin mu, munyi kukan rashinsa sanadiyyar mutuwarsa ya janyowa hajiya hawan jini. Bayan rasuwar mahaifinmu duk wata d'awai niya ta gidan ni da Mukhtar ne muke yinta da yake dama mahaifinmu kafin ya rasu ya d'oramu akan kasuwancinsa da yakeyi a kwari sai muka cigaba da juya dukiyar. Shekarar mahaifinmu d'aya da rasuwa muka kammala degree d'in mu, hajiya kuma ta matsa mana akan muyi aure dama duk muna da wad'anda muke so yayinda Abbanku kuma yake son Rukayya, ba'a d'au wani dogon lokaci ba akayi bikinmu. Auran da mukayi sai Allah ya kuma hab'b'aka arzik'in mu, don haka hajiya tace mu raba gadon da Alhaji ya bar mana idan yaso kowa saiya tada jarinsa munyi na'am da abinda hajiya tace don haka aka raba gadon aka bawa kowa hakkinsa muka cigaba da juyawa. Kafin shekara arzik'in mu ya kuma burink'asa amma duk cikinmu Mukhtar ya fimu iya business don a lokaci k'ank'ani yayi suna a cikin garin kano har ya fara fita k'asashe babu wanda baisan *Alhaji Mukhtar Muhammad shagari* ba kowa ka tambaya zai nuna maka. Shekarar mu d'aya dayin aure Allah ya azurta matanmu nida Abban Ku da samun haihuwa kuma duk maza, sab'anin Mukhtar da matarsa Aysha Allah bai basu haihuwa ba. Ranar suna nasawa Faheem Muhammad sunan mahaifinmu kenan shima Abban ku yasa sunan haifinsa Ishaq shine suke kiransa da Haisam. Haka yaran suka taso cikin kulawa musamman ma Aysha da Mukhtar sunfi kowa basu kulawa. Cikin ikon Allah shekarar su Faheem uku allah ya azurta Aysha da samun ciki, kowa ya tayata murna sai d'auki akeyi da murnar wannan cikin, cikinta yana da wata shida Rukayya ma ta kuma samun nata rabon, a lokacin ne kuma Ibrahim abokin Mukhtar yayi aure. Kasuwanci yana cigaba da bunk'asa yayinda mak'iya suke yiwa Mukhtar bak'in ciki da d'aukakar da Allah ya bashi. Ranar wata laraba da bazan tab'a manta wa ba a rayuwa ta rana mafi muni a garemu ranar dana rasa d'an uwana na kuma rasa mahaifiyata ga kuma Aysha matar Mukhtar itama mukayi rashinta. Mun saba kullum da daddare bayan sallar isha'i muna zama da iyalanmu mu tattauna matsalolinmu, ranar tunda muka zauna Mukhtar yake cewa kansa yana masa ciwo Aysha ta kawo masa magani ta bashi yasha duk da cewa a lokacin tayi nauyi, bayan d'an wani lokaci kawai muka ga Mukhtar yana yi mana wasu abubuwa tamkar wani mahaukaci lokaci d'aya ya canza ya koma yana yi mana hauka tuburan sam ya fice a hankalinsa, hankalinmu ya tashi duk muka hargitse musamman ma Aysha wadda tsabar tashin hankali a lokacin nak'uda ta kamata, hajiya kuwa hawan jininta ya tashi muka rasa ya zamuyi kawai nida Abban ku muka samu dak'yar muka tura Mukhtar d'aki muka kulleshi hankali a tashe mukayi asibiti dasu hajiya. Muna zuwa cikin gaggawa aka karb'e mu sakamakon wahalar da Aysha ta sha wajen nak'uda yasa ta rasa duk wani k'arfinta suka ce saidai ayi mata aiki, a lokacin lafiyarta kawai muke da bukata ba tare da tunani komai ba na saka hannu, Ana shirin yi mata aikin ta haifo 'yarta sai dai tana haihuwa Allah ya karb'i ranta munyi kukan rashinta don Aysha macece mai kirki da sanin darajar d'an Adam, don haka Ana kawo yarinyar nayi mata hud'uba da sunan mahaifiyarta. Hajiya kuwa dak'yar likitoci suka samu hajiya ta farfad'o har ta d'an ware likitoci suka bamu damar shiga mu dubata, hajiya tayi murna da ganin yarinyar da Aysha ta haifa,
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63