Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 35

Chapter 35

Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

muyi aure." Ta gyad'a kai cike da mamaki don ita wasa ta d'auki abin "aure? Wani banbarakwai nake jin abin na fad'a maka abin da kamar wuya taya ma hakan zai faru?" "Insha Allah za'ayi, ki fad'a min *I love you* zanji dad'i," kamar ta kurma ihu take ji ta rasa wanda zata cewa tana so sai Faruq. "Kinsan halina sai na rumgume ki a nan ni babu ruwana gara ki fanshi kanki kawai kiyi abinda nace," tasan halinsa sarai zai aikata "amma ko na fad'a ka sani tursasani kayi kar kayi tunk'awo dashi *I LOVE YOU*" ya tuntsire da dariya, haushi yasa idanunta sukayi narai narai ya rik'o hannunta ta fizge don zuciyarta zafi take, da sauri tabar wajen yana ta shek'a mata dariya babu abinda yake so kamar yaga yasa Hibbah a gaba har tayi kuka, sai yaji wani sonta da k'unarta na shigarsa. Ranar ya nace mata yak'i tafiya ko zama zaiyi saiya dawo kusa da ita sai ya waske yana yiwa Nawaz wasa, shareshi take yi don bata son Faheem ya fahimci suna wani d'asawa ne da Faruq. Ya shigo fuskarsa a had'e kamar bai gansu ba, gani tayi Faruq ya daina rawar kai, "Faruq Ku had'a kayan nan mu tafi gida sun bamu sallama," Faruq ya kalleta "mene kike wani d'ari d'ari nifa bana jin kunya a gaban Ya Faheem sai na miki kiss kinga daya ga haka sai yasan yadda zai nema min aurenki, su bani abuna ko kuma na ja musu maga na b'allo ruwa." Ta marairaice "ka tabbatar min ka tsaneni shiyasa kake bin duk wanda nake da k'ima a wajensa kake zubar min da mutunci, Allah sai ya saka min," maganar ta shige shi ya janyo Nawaz ita kuma ta had'a kayan suka fito. A nota suka iske shi yana danna ways Sam ya rasa mai yake masa dad'i ransa a b'ace yake, Faruq ya bud'e motar yana sa kayan, Nawaz ya shige gaban motar. Ya kalleta "muje ga mota ta mu tafi tare" ta dalla mishi wata harara ta tsuke baki, ya Sosa sumarshi yana dariya ciki ciki, ta rasa wanda zata bi don tana matuk'ar jin nauyin Faheem d'azu ma da k'yar take numfashi a cikin motarshi, amma da ta hau motar Faruq gara ta hau gara ta tafi a k'asa, gani tayi Faheem yayi tafiyarsa. Faruq yaji wani dad'i a ransa shi yasa Faheem yake burgesa akwai jan girma yasan abu ya gani amma sai ya basar kawai don shi baison shiga sabgar yara. Ta k'urawa danjojin motar idanu har suka b'ace a duhun daren, hannunshi taji cikin nata "my dear," a fusace ta k'wace hannunta ta soma tafiya ko waiwaye bata yi har ta d'anyi nisa don zuwa bakin titi daga asibitin da d'an nisa. Faruq ya shiga motarsa yana biye da ita "Hibbah mene haka wai kinsan halina idan kika b'ata min rai," ko kallon shi bata yi ba, kwatsam sai ga wash d'irka d'irkan karnuka sun sharp a guje suna haushi, turus tayi ta ci wani mugun burki zuciyarta tana harbawa ta k'ame babu abinda tafi tsoro kamar kare, sai kace zakuna haka suka tunkarota ta kasa gaba ta kasa baya, gashi sun nufota gadan gadan ai batasan sanda ta bud'e motar ta rufe ba, ta tusa kanta tana ambaton Allah. Faruq ya kwashe da muguwar dariya mai ban haushi yana kad'a kai don wak'ar Machel Jackson yake saurara yana ya fara tuk'insa cikin nishad'i, ya d'ago kanta "my baby kin fiya tsoro, idan munyi aure da kin b'ata min rai police dog zan d'auko su yayyaga ki" tayi banza dashi "Hibbah" ya Kira sunan a hankali, ta kalle shi "gaskiya kin fa tashe ni daga aiki wai sai kimin shiru kin mai dani mahaukaci wato nayi ta sambatun sonki ni kad'ai, ki tausayamin wallahi da gaske nake aurenki zanyi" ta mishi kallon nutsuwa sai yanzu taji zuciyarta ta gamsu da gaske yake amma kuma yafi buk'atar jikinta akan komai, Allah mai yadda yaso gata dai a hannun Faruq duk abinda yaga dama yayi da ita. See Sweet suka iso yayi parking ya fita yaje ya siyo ice cream da fresh milk yana tahowa ta k'ura masa ido handsome bakinta ya furta, ya k'araso cikin motar. Ya mik'a mata ledar, ta kalle shi "gaskiya ba zan karb'a ba na gode in don nice da bakayi asarar kid'inka ba," ya had'a rai ya jefa mata jikinta "sai ki jefar tunda baki so," ya tashi motar bai sake magana ba har suka gida, ta fito ta bar masa kayansa a mota. Ya d'auko ya bita da shi, Faheem yana ta lallab'a Nawaz yayi barci ya dameshi bashi kansa ciwo yake masa. Hibbah tayi sallama yana jinta ya tashi, Faruq ya shigo ya zauna yana kallon news, yana tambayar Faheem kanun labaran Nawaz ya haye jikinsa yana tambayarsa me ya kawo musu a leda, ya mik'a masa wai ya kaiwa Hibbah. Hibbah kuwa kitchen ta nufa tana zuwa ta hango Kausar tana aiki a ciki "aunty sannu da aiki," tayi mata wani kallo dama tana jin haushinta a dalilin tafiyarta yaronta ya samu matsala har ta kaisu ga yin 'yar hatsaniya da Faheem don har yanzu basu shirya ba, "Kama aikinki donni bazan iya ba dama na gaji" tayi ficewar ta. Taji babu dad'i abinda Kausar take yi mata yayi yawa ka d'auki d'an Adam kamar dabba a wulak'ance, ta duba abincin ashe ma indomie ce take dafawa sai kuma dankali da ta soma ferayewa, ragowar mata shikenan abincin da ta iya. A bayanta ta ji shi ta juyo suna kallon juna, surarta ta ja hankalinsa duk da ba yau ya fara ganinta ba, ta juya amma ta kasa ci gaba da aikin don ita bata son kallo da takura. Nawaz ya shigo "aunty yunwa nake ji" ta zobo masa indomie dayake tayi ta bashi, Faruq ya kuma matsowa "Hibbah yaya zan kwatanta soyayyarku da Nawaz ne, gashi shi kad'ai ne a wajen ya Faheem daya bamu shi nasan bazai bamu ba don shi yana son yara, amma wannan Matar tashi ta fini yahudanci wai bata son haihuwa" ita dai feraye dankalin take bata ce masa komai ba "kin San abinda na tsana kenan kiyi min shiru ina magana ko?" Tayi shiru, kawai yatsunsa taji a gefen cikinta yana mata cakulkuli, wata zabura tayi ta zille gefe tasa kuka "Wallahi zanje na fad'awa Daddy'n Nawaz wannan wulakanci da kake min ya ishe ni," "ni d'in mahaukaci ne zaki k'yale ni ina magana ni kad'ai?" Kausar ta shigo tana wani muzurai "ke dalla ki bawa mutane abinci muna jin yunwa" taja tsaki, Faruq yayi mata wani kallo ya had'a rai, sim sim ta fita tana mita don tana shakkar Faruq. Yayi tsaki "stupid kawai 'yar rainin hankali ce matar nan, sai Yaya ya dinga min wa'azi ga rubbish nan a gidansa ya kasa sarrafata, dama ina ciki da ita" "to kai ina ruwanka da shiga tsakanin miji da matar sa haka yake son matarsa don gani yayi zai iya zama da ita" ya harareta "Allah ko uwar iyayi kin fini sanin hakan ko?" Tayi d'an murmushi "kaima ai ba kanwar lasa bace" "Wai ni na rasa girman lefina da ake gani har kuna hangen nauyin zunubi na bazai kankaru

Table of Contents

Chapters

63 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});