Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 20

Chapter 20

Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ALIYU GARKUWA* *Wannan page d'in naku ne DA BAZARMU WRITERS allah ya k'ara had'a kanmu cikin k'aunar juna* Mamaki fal a fuskar Aunty ta b'alle murfin motar suka fito Hibbah ta kalleta tace "Aunty kinsan gidan ne?" Aunty tana kallon gidan tace "gidan Alhaji Sani ne, shine babban yaron daddy," Hibbah ta kalleta Auntyn ta kawai bata ce komai ba, aunty ta cigaba "idan har Alhaji Sani shine mijin ummanki, to ta more don Alhaji sani mutum ne mai kirki shekarun baya matarsa ta rasu da d'ansa guda daya mallaka sanadiyyar accident da sukayi a hanyarsu ta dawowa kano daga Abuja, shi kuma a lokacin sunyi tafiya da Abba," Hibbah ta karyar da kai yanayin jin tausayi tace "allah yayi masu rahma." Suka nufi gidan, gida ne madaidaici, mai gadin ya gane sa'idu don haka ya barsu suka shiga dayake ma irin almajiran nan ne yara, direct parlor'n gidan sa'idu yayi dasu suka shiga da sallama Umma tana zaune tana kallon sunnah TV suka shigo. Umma ta kalli k'ofa da sauri ta mik'e tsaye tare da zaro ido waje tana nuna Hibbah tace "Hibbah? Kece ko mafarki nake," Hibbah tana murmushin farincikin hawaye nabin fuskarta ta k'araso kusa da Umma ta rumgume ta, sai kuma ta saki kuka Umma ma hawaye nabin fuskarta, bata tab'a tunanin zata had'u da Hibbah a nan kusa ba. Ta d'agota daga jikinta tana share mata hawaye tace "kiyi shiru Hibbah ki daina kuka kinji," ta d'ago ta kalli Umma sannan ta maida kallonta ga Aunty tace "Umma ga Auntyna ita ce ta gyara min *RAYUWA*, inna lami da inna delu sunso b'ata ni sai allah ya taimake ni kuma aunty da momy suka taimakeni," Umma tana murmushi ta k'arasa kusa da Hibbah tana cewa "Auntyn Hibbah kiyi hakuri ban tare ki ba koh? Wallahi murnar ganin Hibbah ne yasa," ta k'araso ta rik'o hannun Aunty suka shigo cikin parlor'n aunty tace "lahh babu komi Umma ai tsakanin d'a da haifi sai Allah," ta zauna a kusa da Hibbah tace "Hibbah na yau sai kwana tare da Umma ko," Hibbah ta rufe fuska tana gyad'a kai. Shi kuwa sa'idu dama suna shiga ya nemi wajen zama. Umma kuwa kitchen ta shiga ta d'ebo musu dangin su snacks da drinks ta cika musu gaba dashi, suka d'an ci suna ta hirar yaushe gamu, Hibbah ta Saki jiki sunata hira da umma ita kuwa aunty mamakin Hibbah take yadda ta Saki jiki tana ta zuba surutu tana bawa Umma labarin abinda ya faru tun bayan tafiyarta har taimakon dasu aunty sukayi mata. Aunty ta kasa jurewa tace "Hibbah wai dama haka kike da surutu?" Hibbah ta tad'an rufe fuska tace "Kai Aunty," aunty tace"eh mana gashinan sai hirarki kike da ummanki," Hibbah tayi murmush. Umma ta kalli aunty tace "mun gode Auntyn Hibbah allah ya saka da alkhari, gaskiya naji dad'in abinda kuka yiwa Hibbah bamu da bakin yi muku godiya Allah ya bar zumunci." Aunty tace "ameen Umma dama na kawota ne zatayi hutunta anan idan sun koma zan turo driver ya d'auketa," Umma tace "to shikenan nan auntyn Hibbah Allah ya kaimu," aunty ta mik'e tana d'aukar jakarta tace "Umma ni Zan tafi sai yazo d'aukar Nata" ta kalli Hibbah tace "Hibbah ni Zan huce sai Adamu yazo d'aukarki idan kuma na samu time zan zo" Hibbah ta mik'e tace "to aunty na gode allah ya saka," aunty ta d'an harareta. Umma tace "mun gode fa Aysha kiyiwa momyn naku godiya kafin muzo, ki gaida gida allah ya tsare" umma ta rakota har bakin k'ofar parlor tana ta yi mata godiya Aunty har ta Fara jin nauyi ma. Har wajen mota Hibbah ta rako Aunty, sannan sukayi sallama cike da kewar juna. Hibbah ta koma suka cigaba da hira shima sa'idu yace zai tafi, umma ta Bashi kud'in mota ya tafi. Da umma zatayi girki ma tare sukayi da Hibbah, umma tayi mamaki Gannin yarda Hibbah ta iya girki haka. Lokacin da mijin umma ya dawo Alhaji Sani ya taya umma murnar ganin Hibbah kuma yace zai d'auketa ya rik'eta tamkar 'yar da ya Haifa. Haka Hibbah ta cigaba da zama wajen ummanta, kullum cikin bawa ummanta labarin gidansu aunty take, har umma taji bazata iya karb'ar Hibbah a hannunsu ba, dan sunyi shawara da Alhaji akan zasu karb'eta yace zai rik'eta, a haka har hutun Hibbah ya k'are aunty tazo ta d'auki Hibbah tare sukaje da umma tayiwa momy godiya. ***** *RAYUWA*r Hibbah ta canza daga k'unci ta koma farinciki, Hibbah ta kuma gogewa ta waye, ta kuma zama budurwa idan kaga Hibbah sai ka rantse tafi shekaru sha bakwai, ta kuma cika ta ko ina ta zama cikakkiyar budurwa. Yanxu suna shirin shiga SS 2, Hibbah ta kuma maida hankali akan karatunta don tana cikin d'aliban da malamai keji dasu a makarantar. lokacinne kuma aunty ta kammala makarantar ta *BAYERO UNIVERSITY KANO*, zata tafi service d'inta, da farko Enugu state aka turata, sai da Abba ya shiga ya fita suka dawo da ita arewa inda aka tura Aunty Abuja, taji dad'in turata Abuja da akayi don a gidan Abba zata zauna. Matsalarta d'aya Hibbah bata so tabar Hibbah a gidan saboda tasan any time Faruq zai iya dawowa kuma tasan k'udirinsa akan Hibbah, idan kuma tace zata tafi da ita Abuja momy bazata ji dad'i ba ga kuma karatunta zata fara lalata mata shi. Haka Aunty Aysha tayi ta tunanin mafita daga baya ta yanke shawarar kaita gidan ummanta, ta fad'awa momy shawarar data yanke kuma momy tayi na'am da hakan, Ana gobe zatakai Hibbah, Hibbah ta tattara kayanta suka tafi gidan umman nata, aunty ta yiwa umma bayanin komai sannan ta tafi suka rabu cike da kewar juna. Kafin aunty ta tafi saida ta bawa Hibbah waya wai su dinga gaisawa. Haka Hibbah ta cigaba da zama a wajen ummanta cikim kula irin ta uwa tare da taimakon mijin nata Alhaji Sani, umma ta samo mata mai adaidaita da yake kaita makaranta yana dawo da ita, da haka har aunty ta dawo daga service d'inta lokacin da ta dawo ana hutun makarantu shiyasa bata je d'auko Hibbah ba kuma bata fad'a mata ta dawo ba. Sai Ana saura one week su koma school da yamma aunty taje ta d'aukota, tun a bakin gate Hibbah ta fara ganin taron Jama'a amma mafi yawansu mata ne, ta kalli Auntyn ta tace "Aunty me akeyi a gidan naga taron mutane," aunty tayi murmushi tare da cewa babu komai Hibbah," ita dai Hibbah bata yarda ba duba da k'unshin dake hannun Auntyn, driver ya shiga cikin gidan tare da yin parking, suka fito duk harabar gidan 'yan mata ne 'yan gayu masu ji da Kansu gefe guda kuma ga manyan mata a zazzaune akan fararan kujeru. Suna doso cikin gidan 'yammatan suka shiga ihun Amarya Amarya, kan Hibbah ya kuma d'aurewa ta kalli Auntyn ta sai taga ta kawar da kai tana murmushi taja hannunta suka shiga cikin gidan, a parlor ta kuma ganin tawagar wasu matan ta kuma gani nan ma suna shiga suka shiga yi mata ihun Amarya, daga can gefe ta hango Saudat, Safiyya da wata da bata Santa ba sai wani yaro da bazai huce shekaru uku ba d'an kyakykyawa yana ta

Table of Contents

Chapters

63 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});