Chapter 34
Chapter 34
tana rawa tace "daddy kayi hakuri bazan k'ara ba, Allah ya huci zuciyarki Umma," ta fad'a tana share hawaye. Tausayinta yaji sosai ko da yake yaji dad'i umman ta burgeshi don shi mutum ne Mai son a bashi girma da girmama na gaba dashi don haka bai son reni ko kad'an shi yasa Hibbah ta shiga ransa don tana da biyayya da ladabi Sam bata kiransa da Yaya kamar yarda k'annansa suke kiransa saidai tace masa Daddy kamar yadda taji Nawaz yana fad'a. Ta tashi ta d'auko Jakarta, ya ajiyewa Umma kud'i ba yadda batayi ba ya d'auke abinsa amma yak'i yaji dad'in karramawar da akayi masa da sanin ya kamata irin na iyayen k'warai, suka yiwa Umma sallama suka fito. Ya bud'e mata gaban motar don yasan halinta sai ta zauna a baya, ta kalleshi gani tayi ya had'a rai babu alamar wasa a tattare dashi shiyasa ba musu ta shiga. Ya dad'e bai ji annashuwa ba kamar a yanayin nan ya kunna wakar Celine Dion yana sauraron baitukan wak'ar, yana tuk'i cikin nutsuwa, Hibbah ko numfashi bata yi k'wak'wk'wara ji take yi tamkar ta nutse, kunya ce nauyi ne rashin sabo ne, duk sunyi Mata dabaibayi don basu tab'a had'uwa haka gata gashi ba. Ya dubeta a nutse domin duk damiwarsa babu ita ashe Hibbah ce ta hana zuciyarshi nutsuwa, "Hibbah ta Nawaz ya kikayi shiru ne na takuraki ko? Banji dad'i bane akan abinda ya faru ashe fushi ne dake haka, ki sani nayi miki fad'ane don kawai na damu dake ina kishinki tamkar k'annena su Safiyya ya d'auke ki badon haka ba babu ruwana da ra'ayin wani, ina data dai kin huce ko?" Bata ce komai ba, ya dubeta idanunta sunsha kuka kuwa, zata kuma iya ci gaba da yinsa idan har ya takurata sai yaji maganarta don a takure take ya Sani, shi kuwa so yake ta saki jiki dashi ta daina jin tsoranshi haka don haka ya rabu da ita, da haka har suka k'arasa asibitin. Yana gaba tana binsa a baya, sama suka hau basuyi wata tafiya ba suka isa d'akin, suka shiga ta gaishe dasu momy lokacin Nawaz yana barci momy ta mik'e zata tafi wai dama shi take jira ya dawo yamma tayi sukayi sallama tayi masa fatan samun sauk'i suka tafi. Jimawa kad'an Nawaz ya tashi yana ganinta ya mak'aleta yana k'yalk'yala dariya kamar zata sake gudu ta barshi, ta shafa kansa tana dubansa yayi 'yar rama ta share k'wallar data taru a idanunta. Nawaz ya rik'e hannayenta "aunty Hibbah shine kika gudu wajen Ummanki kika barni kinga inda doctor yayi min allura," ta tab'a wajen "sannu Nawaz Allah ya baka lafiya," "Aunty Hibbah nima zan biki wajen Umma." Ta gyad'a Kai "to naji amma sai ka ji sauk'i zamuje," ta ja hannunsa suka fice barandar suna kallon titi dayaga abinda ya bashi sha'awa sai ya dinga nuna mata suna dariya, yana ta bata labarin abinda ya faru bayan tafiyarta. Yana tsaye ya hard'e hannayensa a k'irjinsa yana kallonsu sun burgeshi da Bashi tausayi "Hibbah" ya ambata a zuciyarsa sunan mai dad'i, ga mamakinsa ashe maganar ta fito fili har tabi iska ta isa kunnenta kawai gani yayi tad'an juyo ta kalleshi, suka had'a idanu cikin wani yanayi a hankali ta d'auke kanta, wani sanyi take gani cikin idanunsa sai taji abin yana mata yawo a k'wak'walwarta. "Hey! My boy," duk suka dubeshu, yayi zanzaro da hula Hana sallah a kansa, da siririyar sark'a tana k'yalli a wuyansa har taso ta shak'e sa, "Yaya ya jikin boy d'in?" "Alhamdulillah yaji sauk'i sosai," hankalinsa yana kan Hibbah bai ko damu da ganin Faheem ba, ya d'auki Nawaz ya rumgume shi tare da yi masa kiss a kumatunsa, shi kuwa ya mak'ale hannayensa a wuyansa tare da zagaye k'afafunsa a jikinsa, Faruq kenan yana k'aunar Nawaz shiyasa shima Nawaz yake k'aunar uncle d'in nasa. Hibbah kuwa kallo d'aya tayi masa ta d'auke kanata don har yanzu tsoransa take ji............... *by* *Mamyn Najmah* [10/26, 9:25 PM] Maman Najma Author P1: 📝🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *RAYUWA* page3⃣5⃣ *NA* *MAMYN NAJMAH* 🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION* D.B.A.W *DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA* Ya kalli inda Faheem yake a tsaye bashi ba dalilinsa, ya matso kusa da ita abinda bata so kenan, shi a wajensa ba wani abu bane don ji yake kamar ya rumgume ta, wutar k'aunarta yana faman huruwa a zuciyarsa duk sanda ya d'ora idanunsa a kan idanunta baya iya sarrafa kansa, ya matso sosai kusa da ita, bata da niyyar kulasa, "Hibbah kinsan kuwa irin sonda nake miki? Kada ki maida hannun agogo baya bana so ki dinga tuna baya ban tab'a tsintar kaina a irin wannan love d'in ba Hibbah." Ya dafa kafad'arta, a taorace ta kalleshi suka k'urawa juna kallo na d'an wani lokaci abinda ta gani a idanunsa tad'an tsorata don tabbas binda ke zuciyarsa ya fad'a, ta ture hannunsa. Yayi murmushi "wannan gangar jikin mallakina ce sai nayi yadda nake so da ita in munyi aure, don haka ki dena guduna , ni d'in nan zan baki mamakin yadda zaki yi dadi indan na zama mijinki," murmushi tayi don ita a ganinta wauta kawai yake tace "abinda kamar wuya, naji zancen kamar almara ta Yaya zaka aure ni? Ka tuna fa kaso k'unsa min b'ak'in cikin da har na mutu bazan manta shi ba, kuma badon komai ba kawai don zalinci da son Kai, karma ka Fara yaudarar kanka don yarda ba yadda za'ayi dakai wai kai masoyina ne, don Allah na rok'eka saboda girmanasa ka k'yale ni ka k'yale min rayuwa haka." Ya kad'a kanshi "duk abinda kika fad'a gaskiya ne ni kaina ina cikin mamaki da tuhumar kaina Yaya akayi na samu kaina cikin sark'ak'iya har na fad'a tarkon sonki, banji haushi ba ai na fad'a miki kyauta kika sadaukar min da kanki wallahi zuciyata bazata iya daure wani abu dake ba matuk'ar ba aure mukayi ba," "ni kana bani mamaki to wai taya zamuyi aure? Wannan shirmen tunani ne abinda bazai yiwu ba." Yaji zafin maganarta ya take k'afafunta da takalmin k'afarsa, ta runtse ido saboda zafi, Faruq mugune yasan takan mugunta. Ya tallafo tallafo hab'arta yana wannan murmushin nasa na k'eta "dube ni sai na aure idan yaso in na aure ki ki hak'a rami ki binne ni da raina ko kuma kii gunduwa gunduwa da nama na saboda tsabar k'iyayyar da kike min," ya k'ura mata idanu tak'i bud'e idanunta, ji yayu tamkar ya lashi kumatunta, ya hurawa idanun iskar bakinsa duk da a rufe suke. Ta bud'e idon tana dubansa shed'anin mutum kenan gani take kamar baya hankalinshi, Anya ma Faruq baya shan k'waya don abubuwan da yake yi kamar bashi da tunani a k'wak'walsa, duk inda ake neman namiji mai kyau Faruq ya kai sai bashi da hali. Ya lakuce mata hanci, ya matso da kansa kusa da ita sosai ya sassauta murya "ke d'innan yadda kika shiga raina, ni sonki nake Hibbah kamar nayi hauka don Allah me kika yi min ne?" Ta juyar da kanta gefe, ya sa dariya "kin mai dani dodo ko Hibbah?" Yayi k'wafa "wata rana sai kin rumgume ne kinmin kiss, ni kuma shagwaba zan tayi miki," ya d'an ja da baya "ki samu cikin addu'a Allah yasa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63