Chapter 37
Chapter 37
shiga tayi wanka ta sauya kayanta tayi sallah ta nufi kitchen, tana cikin aiki Nawaz yace Daddy na kiranta. Ta iske shi zaune yana kallon MBC 2, taje ta durk'usa a gabansa yace ta kawo mishi ruwa, yaso su had'a ido amma kunyarta tayi yawan gaske, ta kawo masa ruwan a cup ya karb'a yasha. "Hibbah" ya furta, yau dai furucin nan yana tsumata, "d'auki wannan kayan naki ne" mamaki yasa ta kasa godiya d'auka tayi ta nufi d'aki. A kan gado ta zazzage, atamfofi ne guda uku da dogayen riguna biyu da hijjabai biyu sai riga da skirt kala biyu, masu daraja don duk 'yan waje ne, da mayuka da turarukan Mata, ta lumshe idanunta tunanin Faheem take da alkharinsa tun sanda suna mota take tuno irin k'amshinsa da kalamansa, Hibbah yadda yake furta sunan a tak'aice a harshensa, wani abu zuciyarta ke zargi don me Faheem yake yi mata wad'annan tambayoyin? Bata yi mamakin wad'annan kayayyakin ba, duk da bai tab'a yi mata kyautar kaya masu tsada kamar wad'annan ba amma dama ya saba yana yi mata kyauta. Ta d'auko takarda da biro, ta soma tunanin me zata rubuta,kawai sai ta fara rubutun. _Daddy_ _Bani da kalmomin godiya a gareka, na gode Allah ya k'ara girma da bud'i na alkhari ya barmu da Nawaz._ _Hibbah._ Ta kira Nawaz ta bashi ya kai masa, yana kwance a parlor ya haye kansa "Daddy gashi inji Aunty Hibbah" ya karb'a ya bud'e ya karanta, yayi nazarin kalamanta wani d'an murmushi yayu yarinyar ta shiga rayuwarsa, yayi ajiyar zuciya yau saboda da ita ne kawai yaji bai son fita ko ina yana hutawarsa. Allah yasa ta fahimci manufarsa, ko tama sanu take sharewa don yayi mata hannunka mai sanda oho, ai ita mai hankali ce zata gano shi a hankali matsalarta dai rashin son sakewa a gidan indai yana gidan, sai tayi ta nuk'u nuk'u bata son ko ganinta yayi har abin ya zame mata tsoro. Da yamma ya samu ya fita don anyi masa waya ana nemansa, yana fita Jabeer yayo mata waya yana waje, nan ta shirya ta ja hannun Nawaz suka fita. Bayan sun gaisa Jabeer yace "Hibbah banji inda shawarar ku ta tsaya ba akan sa ranar nan, sauraronki nake yi na samu Aunty Aysha naji bakinku yazo d'aya itama tace wai zata tattauna da Umma, abinda yasa na dame ki ni mutum ne mai d'aukar abinda nake so da mahimmanci ban son shiririta a al'amurana, idan kina ganin abin bazai yiwu ba ki fad'a min gaskiya kawai kar ki b'oye min" tayi d'an murmushi "kasan ba nike da kaina ba kuma nayi maka bayanin komai bani zan aurar da kaina ba, amma ka samu Alhaji Ku tattauna kaji ta bakinsa," "to naji dad'in hakan, kar kiga zak'ewata ina sonki da yawa shi yasa nake nuna miki damuwata kuma nasan kema kina sona, zan sameshi in Allah ya yarda." Faheem ya dawo ya huce su, Nawaz ya bishi don taryarshi, al'adarsa kenan komai yake yi da yaji motar Daddy'n shi ya dawo to saiya taro shi, Faheem ya saba mishi da hakan yakan ji dad'i aranshi sosai. Tayi ajiyar zuciya Faheem mai sata cikin rud'ani in dai ta ganshi sai komai ya sauya mata in a parlor take ta gudu d'aki, in tana tafiya ne taji kamar anyi mata dabaibayi dole take tsayawa sai ya huce sannan ta cigaba, ya katse mata tunani "ina son mu gaisa da yayan nan namu amma naga kamar bai da son mu'amala da mutane, a k'alla ya sha wucemu anan yasan kuma ina zuwa wajenki ne don na aureki amma ko duban inda muke baya yi bare ko hannu ya d'aga min, ni kuma inason mu gaisa dashi ya sanni sosai don yasan shima yana da ruwa da tsaki a cikin maganar aurenki tunda a hannunsa kike zaune" "gaskiya ne kuma mutumin kirki ne, kawai dai allah ne bai nufa zaku gaisa d'in ba sannan na fahimci bai da wani ra'ayi akan shiga maganar aure na tunda bai tab'a yin magana akan hakan ba, amma nasan idan lokaci yayi zai yi." Ya gyada kansa "shikenan Allah ya tabbatar da alkhari na gode" ya bata wani k'unshi a rufe a takarda. "Kai baka gajiya yau da gobe sai Allah," "Ana gajiya da masoyi ne?" Mutuminta ne ya huce su a mota, Faruq d'an rikicin duniya da da inda zata je data gudu sai ya tafi saita dawo domin zai sa ta a gaba ne kawai sai ya sata kuka. Sukayi sallama ta shigo gida, ta huce shi a cikin motar kamar bata ganshi ba, ya dad'a k'uluwa kishi ke cinsa kamar masifa, wai wannan Jabeer da jaraba tsiya yake duk yadda ya tozarta Hibbah a gabansa bai hakuri ba. Ya fito yana take mata baya ya janyo mayafinta ba shiri ta yo baya kamar zata fad'i ranta a b'axe ta kalleshi zallar masifa ta gani a idanunsa yau ta tab'o Faruq, mai cin zalinta a bulus bare da dalili. Ya nannad'e mayafin a hannusa tana ja ta kasa k'wacewa, ya kuwa murd'e hannunta ta rintse idanunta ji tayi kamar zai b'allata tayi wata 'yar k'ara "wayyo Allah na!" Abinda ta tsana kenan wannan rashin mutuncin da Faruq yake yi mata tana d'aukarsa tsabar tsana ce da rashin galihu. "Zan nuna miki mahaukacin kishi na akanshi zan iya komai tunda kika jawo mutumin nan duk da irin tozarcin da nayi miki a gabansa ashe tsugunno bata k'are ba, matuk'ar na k'ara ganinki dashi sai na miki rashin mutuncin da baki tab'a zato ba, don ji nayi kamar nasa bindiga na harbi k'ok'on kansa." Faheem ne ya fito yaji kuma furucin Faru$q sarai amma yayi kamar bai san su ba yayi wucewarsa, wani bak'in ciki taji ya k'ulleta kamar ta fad'i ta mutu wajen. Babu mutumin da a duniya bata son mutuncinta ya zube a wajensa kamar Faheem tana ganin girmansa, gashi a yau yaji ya gani hujja ce da zai d'ora zarginsa akan gaskiya tana mu'amala da Faruq bawai iyakar soyayya ba, wani tunanin zai yi don Faruq dai bashi da halin k'warai akan 'ya mace, gashi ya rik'e hannunta gam bata da wani sauran mutunci a idanun Faheem, wannan wace irin *RAYUWA* ce............... *#JUMMA'AT MUBARAK TO YOU ALLπππ€* *by* *Mamyn Najmah* [10/26, 9:25 PM] Maman Najma Author P1: πππππππππ *RAYUWA* page3β£7β£ *NA* *MAMYN NAJMAH* πππππππππ *DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION* D.B.W.A *DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA* Wani sambatun banza yake yi mata ta tureshi a fusace "Allah ya isa cin zalina da rashin mutuncin kake min, k'arewar tsana k'in jini ka kashe ni ka huta, babu mutumin da na tsana a duniya irin ka.........." Kuka ya shak'eta, maganar ta shige shi domin alwashin ya daina mata irin wannan abun amma why? Why yaji kishinta haka? Kishinta ne ya tursasashi don abinda yafi wannan ma zai iyayi sai dai duk abinda za'a yi masa ayi masa, ta shige gida, a cikin d'akin ta watsar da kayan ta kwanta kan gado gami da kifa kanta a kan pillow, ta gaji da wannan wulak'ancin da cin zarafin na Faruq wai me ta tsare masa ne a duniya? Burinsa ya sata kuka ya zubar mata da k'ima da daraja a idanun mutanen da suka d'auketa mai mutunci, to
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63