Chapter 1
Chapter 1
Copied By YAYA HAYAT (admin Hayat hausa novels Hausa novels and fashion Cool novel, makeup and kitchen1⃣ Cool novel, makeup and kitchen2⃣ AND Cool novel, makeup and kitchen3⃣) WHATSAPP NO:+2349030159301 [10/26, 9:21 PM] Maman Najma Author P1: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RAYUWA* page1⃣ *NA* *MAMYN NAJMAH* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA* *BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM* *INA GODIYA GA ALLAH SWA DAYA BANI IKON RUBUTA WANNAN LITTAFIN. SALATI DA AMINCI SU KARA TABBATA GA ANNABI MUHAMMAD SAW, ALLAH YA KARA MANA SON SA AMEEN.* *NA SADAUKAR DA WANNAN LITTAFIN DUNGURUNGUM GAREKI MASOYUYATA AYSHA ALIYU GARKUWA. ALLAH YA KARA BASIRA DA DAUKAKA, ALLAH YA RABAKI DA SARRIN MAI SARRI YA TSAREKI DAGA DUKKAN MAKIYANKI. YA ALLAH INA ROKANKA KA DAUKAKA AYSHA ALIYU GARKUWA KASA TAFI KARFIN DUK WANI MAKIYINTA AMEEN* *INA TAYAKI MURNAR KAMMALA LITTAFINKI BANDIRAWO DA KIKAYI ALLAH YA SANYA ALKHARI YA KARA BASIRA DA BAIWA MAI TARIN YAWA AMEEN.* Kauyan *katsalle*wani karamin kauye ne dake cikin kauyen *bunkure* dake jahar *kano*. Malam Mukhtar da iyalinsa na daya daga cikin mazauna cikin kauyen. Matan malam Mukhtar biyu lami itace uwargida sannan Aysha amarya. Tun auran malam Mukhtar da lami shekara goma allah bai basu haihuwa ba hasalima ko bari lami bata taba yi ba. Malam Mukhtar ya damu kwarai da rashin haihuwa da bai samu ba, wannan dalilin yasa shi Karo aure. Allah ya hadashi da Aysha yar mokocinsu ya aureta, bakaramin tashin hankali lami ta shiga ba jin wai mijinta zai Karo aure sannan kuma yarinya karama zai aura wadda bata fi yar cikinta ba, wannnan dalilin yasa lami shiga ta fita na ganin ta hana wannan auran amma sam abu yaci tura duk wajen malamin da taje magana iri daya suke fada mata dole ne sai yayi wannan auren, Wannan dalilin yasa ta hakura da bin malaman ta daura damarar yiwa malam Mukhtar da Aysha tijara da rashin mutunci Sam ta hanasu sukuni da kwanciyar hankali kullum cikin neman masifa take. Wata tara da auran Aysha da malam Mukhtar allah ya a zurtasu da 'ya mace kyakykyawa sak ta dauko kamannin Aysha, kasancewar ita Aysha kyakykyawace tamkar balarabiya. Haihuwar da Aysha tayi ya kuma daga hankalin lami, ranar da akayi haihuwar ta wanke kafarta ta tafi gidan aminiyarta delo ta fada mata abinda ke zuciyarta ba bata lokaci delo ta zari mayafi suka kama hanyar gidan bokansu. Suna zuwa suka fada masa bukatarsu nan ya bata kullika da wanda zatayi turare dana tsarki da wanda zata zubawa malam Mukhtar a abinci ya tsani Aysha da 'yar ta ta. Bayan ya gama yi musu bayanin kumi lami ta kunce gefen zaninta ta kunto kudi ta zubewa boka sukayi godiya suka tawo cikinsu fal murna. Tun daga wannan ranar malam Mukhtar ya juyawa Aysha baya, baya shiga dakinta ko magana ma bayi mata yakeyi ba saidai idan lami ta zugoshi yazo ya balbaleta da fada, KO sunan jaririyar ma ita ta sama mata *HIBBATULLAH* _gift of Allah_. Haka rayuwa ta juyawa Aysha da 'yarta cikin lokaci kankani, shekarar Hibbah daya allah ya bawa lami 'ya mace so kuga rawar kai wajen malam Mukhtar da lami, tunda lami ta haihu Aysha takoma tamkar yar aiki komi ita takeyi wankin kashi kirki komai ita keyi. Ranar suna yarinya taci sunan mahaifiyar lami wato Rahmatu, akasha shagalin suna duk da kauyene amma malam Mukhtar ya kashe kudi. Rahmatu ta taso cikin sangarta da shagwaba sabanin Hibbah data taso cikin tsangwama da kyara da tsanar da mahaifinta yake nuna mata. _wannan kenan_ "Ke Hibbah! Hibbah ina kike ne? kina jina ina kiranki ayeh?" Lami dake zaune a tsakar gida ta fada tana karasa jera abincin siyarwarta a faranti, Rahmatu na taya ta. "Na'am Inna gani nan zuwa" Hibbah ta fada tana fitowa daga wani dan karamin daki rike da hijjab dinta a hannu tana kokarin sakawa. A hankali ta karaso ta tsugunna a gaban Inna lami tare da cewa "gani Inna". Murfin dake hannun innan ta kwada mata aka tana cewa "ubanki kikeyi a dakin kina jina inata a kwada miki Kira amma kikari burus kika k'i amsawa koh? Saboda kin rainani koh?" Cikin tsantsar masifa da daga murya take magana. Da sanyin murya tace "Dan allah Inna kiyi hakuri wallahi hadda nakeyi,gobe malam zai ansa hadda kuma duka zaiyi idan ban iya ba...........". "Ni zaki fadawa karatu don ubanki ko don ba waccan tambadaddiyar uwar taki bace take kiranki, ayeh?" Cikin masifa da bala'i ta katseta. Kasa Hibbah tayi da kanta ta kuma cewa "kiyi hakuri inna" "Bazanyi hakurin ba shegiya munafuka sai anyi magana kice ayi hakuri da hakurin ta mutu sadakar nawa kika bada? Nace sadakar nawa kika bada? Kuma wallahi wannan makarantar gaf kike da daina zuwanta don bazai yuyu ba ki dinga yimin cikas acikin Sana'a taba tashi ki dauka ki fitar min dashi kuma saura ki dawo min da saura kiga yarda zanyi lasalasa dake a gidan nan". Magana takeyi ko numfashi bata saukewa. Matsawa tayi kusa da farantin ta dauka ta Dora a kanta data Fara tafiya taji Rahmatu Na cewa "wallahi Inna bakin cikin Hibbah take miki, kullum sai sale driver yace takai masa amma taki ta Kai masa, tun rannan dayace zai siye duka shine tace bazata saida masa ba." Rike baki Inna tayi tanajin Rahmatu sannan cikin tsantsar masifa tace "ke Hibbah zonan yar bakin ciki" jikinta ne ya fara kyarma ta juyo cike da tsoro ta tsugunna a gabanta. Wata maka Inna ta kaimata a fuska tace "bakin ciki kike yimin kar a siye kwantai kike so nayi? To wallahi kika dawo min da kwano data wallahi sai naga mai kwatarki a gidan man shegiya Mai zubin aljannu, tashi ki bar min gaba." Tashi tayi hawaye nabin gefen fuskarta tayi hanyar zaure da niyyar fita ji tayi an dafa kafadarta ta San ko wane hakan yasa cikin sauri ta goge hawayenta, sannan ta kakaro murmushi ta juyo Umma ce a gabanta wadda a gabanta akayi komai, dauke da murmushi a fuskarta tace "kiyi hakuri hibbatullah wata Rana sai labari kiyi ta hakuri *RAYUWA* mai canji ce wata Rana ma bama duniyar baki daya." Murmushi tayi tace "wallahi Umma babu komai a raina nasan haka allah ya kaddara min tawa *RATUWAR*" Umma ta shafa gefen fuskarta tace "yauwa Hibbah allah yayi miki albarka". "Ameen "Hibbah ta fada tana kokarin fita daga gidan. "Hibbah" Umma ta fada tana karasowa kusa da ita. Juyowa tayi tare da cewa "na'am Umma" kuma dafa ka fadarta tayi tace "don allah Hibbah....." Katseta... *Idan kuna bukatar Na cigaba sai naga comments naku ta wannan number 07088301840* *by* *Mamyn Najmah* [10/26, 9:21 PM] Maman Najma Author P1: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RAYUWA* 2⃣ *NA* *MAMYN NAJMAH* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA* *Masoyana na samu sakonnin ku kuma in allah ya yarda zan cigaba da wannan littafin na gode da kauna da kulawa da kuka nunamin.* Katseta Hibbah tayi da cewa "na kula da kaina karna kula kwayan banza, karna biyewa wani namiji muyi hira kuma na zama mai kamun kai da nutsuwa a wajen sana'ata na girmama mutane, duk wanda ya zomin da wata magana dabai dace ba karna kulashi ko ba haka ba Umma?" Hibbah ta jero mata wadannan kalaman. Umma kuwa tsayawa tayi tana mamakin yarda d'iyar tata tasan abinda take son fada mata. Cikin mamaki
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63