Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 42

Chapter 42

Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel 1,204 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

cup d'in yak'i taruwa, ta dinga yi masa dariya ya shammaceta ya ture nata bokitin ruwan ya zube, sai ya hau shima yi mata dariya harda tsalle yana k'yak'yata mata dariya k'ya k'ya k'ya. Ta lura da motar Faheem don basu ji shigowarsa ba saboda ruwan da akeyi a tunaninta bazai fito ba saboda ruwa karya jik'asa, ga mamakinta fitowa yayi abinsa, Nawaz ya dinga d'aga masa hannu "Daddy Daddy ruwa zai dokeka ka gani ya jik'a ka" ya karb'e lemar daga hannunta yana kallonta, ta sunkui da kanta "Hibbah" wannan lafazin na Faheem sai taji.muryar tashi ta canza "baki kawo min lema ba kin Bari ruwa ya jik'a Daddy'n Nawaz." Ya ilahi, ita dai wani abu take ji tamkar zata fad'i k'afafunta suka d'auki rawa, ya zuba Mata idanu kawai yayi nisa ya tafi da yawa ikon Allah haka so yake Allah ya had'aka da Wanda baka tab'a tunani ba. Kamar bata motsi kunya da nauyinsa sun rutsa da ita. Shi da kansa ya samu damar da yake jira yasa Hibbah ta fad'a tarkonsa yau k'wauron baki ya k'are zai fasa k'wai. "Hibbah" da sauri ta juya da gudu cikin gida, yayi d'an murmushi yana Mai jinjina wannan irin kunyar ta Hibbah. D'akinta ta shiga ta d'ora kanta a bisa pillow zuciyarta kamar tana harbawa idanunta Faheem kad'ai take gani kamar cikin cikin film wannan abu yak'i goguwa nauyi ne tsoro ne ko kuma kunya me yasa haka? Faheem dodo ne? Tsabar cika ido da kwarjini ne ta bawa kanta amsa. "Hibbah" yadda yake futawa take tunawa a tausashe sai taji kamar yafi kowa iya furtawa. "Aunty Hibbah kizo inji Daddy" zumbur ta tashi zaune ta kad'a kanta "to ina zuwa" Ta jima tana sak'a da kwancewa me ya hanata fita kiran Faheem don fa ya rud'ata nauyinsa ya k'aro. Ya bud'e k'ofar ya shigo, ta dubeshi ya jingiba bayansa da k'ofar ta saci kallonshi wata k'atuwar rigar sanyi sanyi ya Santa mai taushi kamar gashin jikin mage, ya cire hular jikin rigar daga kansa gami da Santa hannayensa cikin aljihun rigar. "Hibbah" sai da ta kad'u sassanyan kiran ya ratsa zuciyarta "Hibbah ni gani nazo tunda na aiko ki zo kin k'i fitowa ni d'in............ *by* *Mamyn Najmah* [10/26, 9:26 PM] Maman Najma Author P1: 📝🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *RAYUWA* page4⃣0⃣ *NA* *MAMYN NAJMAH* 🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION* D.B.W.A *DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA* "Hibbah ni gani nazo tunda na aiko ki so kink'i fitowa ni d'in abin tsoro ne? Ni fa mutum ne kamar ki idan kuma kunya ce gaskiya tayi yawa" tayi shiru ta kasa magana "ok to ki saurareni ina so ne muyi wata mahimmiyar magana, kinsan so wani abu ne dake faruwa da mutum ba tare da zato ko kuma tsammani ba, munyi amanna da fad'ar Allah ta'ala shike jefa so a tsakanin d'ayanmu, na tsinci kaina a cikin wani hali mai wuyar fad'uwa may be ma kin fahimce ni kika basar, na nuna miki alamomi da dama ke mai hankali ce kinsan me nake nufi. Ina nufin kalma guda aure, idan banda shi bani da wata manufa a gareki, ni zan aureki amma da sharad'in abu biyu kina sona kuma kina ra'ayina don wad'annan abubuwan suke Gina aure." Saura kad'an numfashinta ya d'auke wani abu taji ya harba a zuciyarta, duk lissafinta ya wargaje , wata sabuwa inji d'an caca ko da wasa bata tab'a tsammanin wannan furucin daga bakin Faheem ba, ikon Allah wai ita Hibbah 'yar aikin gudansa ba kazar kowa ba ita yake so? Ta yarda wani wajen Ana gudunka ana tsanarka wani wajen kuma sonka da k'aunarka ake yi, duk mutumin da ake yiwa hassada da k'yashi sai hassadar ta zama kamar taki ake barbad'a masa Allah abin godiya wai ita ke da matsayin da Faheem yace yanaso tabbas idan Allah bai wulakanta ka ba babu mai wulakantaka a duk fad'in duniyar nan, Inna lami taso lalata rayuwarta amma da yake Allah gafuru rahim ne sai yayi hanyar zuwanta birni don wasu su gyara mata *RAYUWA* mai makon a lalata, Allah ne ya bata wannan baiwar bamai iya ja da ikon sa. "Ni zan aureki" kalmomin da suke mata yawo kenan, to me za tace abubuwa sun sark'e, "Hibbah" ya katse mata tunani, sai taji kamar ta fita da gudu don bayyana son nata gareshi zai dad'a nauyi da kunyarsa a tare da ita "Hibbah ya dai sai kin bani amsa ko muyi ta zama anan" Ya rud'a mata k'wak'walwa ta rasa Kalmar da zata d'orata a harshenta. Ya zauna gefen gadon nan fa taji daddad'an k'amshin dake manne a jikinshi ya kuma tsumata, a yanayin da take jin Faheem ranta shi d'inne tsagwaronsa kamar yadda take ji a yawan lokuta idan sun had'u abin na yi mata yawo, ko me kenan? Zata iya fassara shi da kalmar "so" to amma anya wannan so ne, idan sone me yasa bata jinsa ga Jabeer ko Faruq, tunda suma suna sonta kuma dasu ne ta Saba mu'amalar soyayya musamman ma Jabeer. Yau dai gata ga Faheem mutumin da take d'ari d'ari dashi, hanyar da yabi ma bata so ta bi don kar suyi arangama saboda mutuncinsa da k'imarsa da take gani fiye da kowane mutum a rayuwarta. "Haba Hibbah nifa bana son nayi ta magana a k'yale ni ni kad'ai bana jin dad''i, na jima a cikin k'alubalen sonki nayi k'ok'arin barin abin saboda wasu dalilai amma Hibbah na kasa jurewa, ba irin wannan son bane ake dak'ileshi yafin k'arfin hakan, na yarda da shi na kuma daina wani inkari cewa zan iya hakuri dashi domin ya wuce tunani na. Na sani kina ganin k'imata da girmana inason mu tafi a haka ki cigaba da ganin mutunci na, don ni hakan bazai hanani nuna miki k'auna ta zahiri ba tunda bawai wasa nake ba magana ce ta gaskiya ta aure, lokaci na k'urewa ko yaushe na k'ella ido na ganki sai abin ya tab'o min zuciya, bai kamata na b'oye miki ba don sai da amincewarki za muyi aure, kinga kuwa dole na nemi had'in kanki." Yayi murmushi gami da tsagaitawa ya maida numfashi "hmm Ana min rowar eyeball d'in nan har b'oyewa kikeyi don karna gani, Hibbah kinsan saboda ke nake dawowa gida da yamma, ko muryarki kawai naji sai hankali na ya kwanta, to ina zankai sonki bazai yuwu na iya daurewa ba ko kuma na cigaba da k'wauron baki ba, kinsan halayena nasan naki abinda na sani tuwo na maina za'ayi ki auri mai gidanki bana son tsaiko ki tare nan da sati biyu" ya dubeta "zuciyarki ta gamsu dani da shawarata?" Ta rufe idanunta da hannayenta magana dashi tana mata wahala. Hmm shidai ya sani akwai sanshi a tare da ita, sai dai ta kasa fahimtarsa ko ta san itama tana sonshi d'in domin kunyar da take mishi ai alamune na akwai wani abu a can k'asan zuciyarta dake tirsasa jin kunyar. "Hmm amma dai Hibbah nan zansha wahala dake wannan kunyar taki tayi yawa amma akwai lokacin da zan rad'a miki wani abu sai kin manta da komai banda ni d'in nan" ya mik'e "inason tuwon masara da k'ashin rago miyar kukan nan, ga wannan ki bawa Isah ya siyo miki abinda kike da buk'ata." Kud'i ne ya

Table of Contents

Chapters

63 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});