Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 7

Chapter 7

Rabo Ajali Book 1 Complete Hausa Novel 1,198 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Allah dan annabi ku maida mu gurin mammi ta waiga ta kalli mahaifinta tace papa kaji tsoron Allah, Oyiza cikin Fushi tace chummy lord yaran nan na bata mana lokaci gashi har asuba ta gabato ga kuma mum can daure gara ayi mata abinda za'ayi in wuce gida, Fanne ta waigo ta kalleta a hankali tace mum? U mean mum dinki kika bayar saboda--- wannan karan chummy ce da kanta ta kai mata duka a baki, chummy tace bazan kashe yaranka yanzu ba alhj sambo dey wl be under my control, zan watsasu duniya saboda naga za'a dama dasu, fanne tace karya kikeyi jininmu ne yafi karfin ki,,, chummy tayi murmushi tana girgiza kai,, Alhj sambo cikin tsoro yace my lord ina tsoron kar suyi min illa, chummy tace babu kai babu su saboda zaku binne gangar jikinsu a grave so ka kwantar da hankalinka, yayi ajiyar zuciya yana kallon hararar da fanne take musu shi da oyiza,,, dafa kansu chummy tayi da wata sanda mai kyalli nan da nan suka bace,, Mum din oyiza kuwa kuka ta dingayi ganin ďiyarta ce ta bada ita, gaba daya magana ma kasa fita tayi a bakinta sai girgiza kai kawai takeyi tana tunano rayuwar da tayi da yarta, cikin minti goma aka gama da maman oyiza suka gama shaye shayensu sannan kowa ya bace, ,, Kuka oyiza takeyi a bakin gadon da mum ke kwance tana ihu makotan da ta aika mai gadinsu ya faďa musu suna kanta suna bata hakuri, ta kira can kauyensu ta fada musu suma suka dinga ihu suka shirya suka kamo hanyar abuja, Guraren karfe biyu akayi mata sutura da kyar dan yan uwanta sunce saidai su kaita can okene a binneta ita kuma oyiza ta kafe saidai a binneta anan saboda tsoron kar asirinta ya tonu dan tasan kakarta na ganinta zata san abin da ya kasheta dan itama mayyar kanta ce, saida malamai sukayi ma yanuwanta nasiha sannan suka yarda akayi mata sutura aka kaita gidanta na gaskiya... Washe gari ta kira john a waya tace yaje ya buďe shago in alhj basheer yazo ya kawoshi gidansu, haka kuwa akayi yaje ya bude shago amma har dare babu alhj basheer, washe gari ma haka, oyiza hankalinta in yayi dubu ya tashi tana ta kai kawo saboda rashin zuwan alhj basheer gashi har an kusa sati daya, a daren ranar ta bayyana gaban chummy da matsalolinta, chummy ta gama incantation dinta tana girgiza kai tace yana karkashin kulawar matarshi, ta nuna mata wata kwarya, bakar mace ta gani a ciki sanye da hijab tsaye gefen gadon mijinta dake bacci tana sallar dare in ta idar sai tayi adduoi ta tofeshi dashi sannan ta mike ta kara tada kabbara, chummy tace kin gani da idonki ko? Oyiza ta haďe rai tace na gani amma ay ni babu ruwana da wannan, mum na bayar saboda haka so kisan duk yadda zakiyi, chummy tayi dariya tace dadina dake wutar ciki, trust me Oyee cikin satin nan za'a daura miki aure da alhj basheer, cikin farin ciki oyiza tace yanzu naji magana..... Mrs tijjani shattima..... [15/12 09:32] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 8⃣ By Aysha Ya'u Kurah Alhaji basheer tsugune yana gyara canvas din kafarshi cikin shigar blue nd white track suit, mikewa yayi bayan ya gama ya kalli matarshi zeenatu dake gyaran gadon da ya tashi yace to ni na fita training, tace to a dawo lafiya yallabai, yace Allah yasa sannan yasa kai ya fita, Zagaye ya dinga yi yana jogging cikin farin ciki saboda yadda sanyin safiyya ke kaďashi, yayi zagaye na tara yana yi yana hutawa, a zagaye na goma ne ya hango wani shima jogging din yakeyi dai2 gurin wata katuwar kwata kafarshi ta gurďe ya tafi zai faďa alhj basheer yayi saurin rikoshi yana fadin subhanallah sannu, mutumin ya ďago yana gyara kafarshi yace yauwa nagode sosai gaskiya ka taimake ni, alhj basheer yayi murmushi yace mu gode ma Allah, mutumin ya mika ma alhj basheer hannu yace sunana Bara'u ina nan zoo road, "BB close" opp gidan alhj Basheer Balarabe, Alhj basheer yayi dariya yace ni kuma sunana Basheer Balarabe (BB) nima ina zaune a zoo rd BB close cikin gidan Alhj Basheer balarabe, Alhj Bara'u yayi dariya sosai yace ikon Allah alhj basheer, kaga yadda Allah ke abunshi ko, . alhj basheer yayi dariya yace kai gaskiya bamu fitar da hakkin makobtaka in ba haka ba ga gida ga gida ace bamu san juna ba,, Alhj bara'u yace ko 1week banyi da tarewa ba kuma nasa ayi min magana da duk makota na kai kaďai ne Allah baiyi zamu hadu ba saboda ance min baka gari, alhj basheer yace kwarai kuwa ban daďe da dawowa ba, to ya unguwar tamu da fatan dai baka samun matsala, Alhj bara'u yace walhy babu matsala unguwar cike take da mutanen kwarai naji dadin kasancewata cikin ku, Alhj basheer yayi murmushi suka fara tafiya yace to ya iyalin fa, Alhj bara'u yace tukunna dai har ansa rana jiranta nakeyi ta karasa skull zuwa nan da 3monts sai ayi in shaa Allah, Alhj basheer yace Allah ya nuna mana kai kadai ne a cikin gidan kenan, alhj bara'u yace eh ni kadai ne amma weekends a daura nakeyi saboda rashin iyali, alhj basheer yace hakan yayi Allah ya taimaka yace ameen har suka karaso gida suna hira cikin kankanin lokaci suka saba da juna, a dai2 kofar gida sukayi sallama kowa ya shiga gida, kanshi tsaye yake tafiya cikin gidanshi yana amsa gaisuwar masu musu hidima, yazo gab da shiga parlo yaji wata muguwar faďuwar gaba, juyawa kanshi ya fara yi sosai ya dafeshi ya karasa parlon dakyar ya zauna kan kujera, zeenatu na can kitchen bata san halin da mijinta yake ciki ba, runtse idonshi yayi siffar Oyiza ta dinga mishi yawo a cikin kwakwalwar kanshi, buďe idonshi yayi da sauri da ya tuno da oyiza gaba daya yaji wani abu ya tokare mishi kahon zuciyarshi, ga wutar son ganinta da ta ruru a zuciyarshi kamar wacce aka iza da petur, mikewa yayi da sauri ya shiga bayi yayi wanka sharp2 ya fito ya shirya da gaggawa ya feshe jikinshi da turare ya debi kudi a sv dinshi na gida masu yawan gaske sannan ya wuce kitchen ya sami zeenatu, Cikin rashin fahimta tace tafiya weekend kaiko ina zaka, yace abuja zeena alheri ne yake kirana, tayi murmushi tace to Allah ya kawo mana alkhairin tare, yace ameen yar matata sai na dawo, tace to Allah ya tsare ya kuma kiyaye hanya, yace ameen ya fita da sauri, biyoshi tayi da gudu tace na manta ban fada maka ba, dan Allah zan shiga gidan Malam atiku gurin Ma'u tayi min kitso, yace to adawo lafiya tayi miki mai kyau fa, tace karka ji komai in dai kitson ma'u ne, yayi murmushi ya fita ya tafi... Da kyar ya gane restaurant din, yana isa ya fito cikin farin ciki,, tsayawa yayi turus saboda ganin gurin da yayi a rufe, jingina jikin motarshi yayi ya rasa me ke mishi daďi yanzu wa zai fara tambaya inda take anan gurin, ya kusa 30mins kafin ya shiga motarshi da niyyar tafiya, kamar daga sama ya hango john

Table of Contents

Chapters

61 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});