Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 5

Chapter 5

Rabo Ajali Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kuďi babu maciyansu sai dai yan uwa da makota, ya kosa matuka yaga yana da ya'ya barin ma ďa namiji dan wani lokaci har mafarkin gashi nan an haifa mishi ďa kuma namiji yakeyi, a wannan yan lokutan ne ya fara tunanin k'aro aure duk da a lokacin ba mazauni bane saboda bai fi yayi sati a nigeria ba sauran kwanakin duk a kasar waje yake yinsu yana turo kaya, Wata ranar asabar ya baro airport cikin tsananin jin yunwar da ta bashi mamaki, nan ya tsinci kanshi da tsayawa a wani restaurant dake Jabi dan bazai iya matsawa ko'ina ba tare da yaci abinci ba, cikin karairaya wata farar ingarmar budurwa ta matso kusa dashi tace alhj me kake bukata, cikin ruďewar ganin jar fata gata a cike gaba da baya ko'ina sai rawa yakeyi a jikinta yace anytn special yanmata dan yunwa nakeji sosai, ta ďan tsuguno kadan tace an gama ranka ya dade, tayi gaba jikinta na girgiza alhj basheer ya bita da ido baki sake yana kallonta har ta bace ma ganinshi, ajiyar zuciya mai karfi yayi sannan ya gyara zamanshi dan ba karamin tafiya da imanin shi tayi ba, cikin yan dak'ik'u ta dawo dauke da plate din fried rice da pepper chicken sai peprsoup din kayan ciki a gefe da drinks, alhj basheer da bai cika cin abincin restaurant ba sai gashi ya tsinci kanshi da cin abincin nan sosai, takardar bill ta kawo mishi yabi kirjinta da ya cika kamar zai faso cikin rigarta da kallo yace yanmata duk wadannan kudin ni zan biya, tayi walll da ido tace alhj yayi kaďan ko, yayi wata kasaitacciyar dariya yasa hannu a aljihu ya ciro rafar dari biyar yace ya daiyi yawa ni kinga abinda zan iya biya nan, tayi murmushi tasa hannu ta karba haďe tsugunawa, tace to an gode yallabai, tayi gaba ya bita da kallo yana lasar baki kamar tsohon maye, tashi yayi bayan ya gama goge bakinshi da tissue yana sakace ya yafito wani yaron da yaji an kirashi da John, da sauri yaron yazo ya tsuguna yace alhj any problm, alhj basheer ya ďagoshi yace no young man ina bukatar taimakon ka ne,, john cikin mamaki yace taimakon me alhj, alhj basheer ya jashi waje yace wannan yarinyar da take kawo abinci nake son sanin sunanta, john yayi dariya yace OYIZA kake nufi, alhj basheer yace ban sani ba wata fara kakkaura, yace yes itace alhj sunanta "Safiya" Oyiza ake ce mata ita y'ar mai restaurant din nan ce, bata cika zuwa nan ba sai in tazo daga lagos kuma I think gobe ma zata koma saboda tafi 1wk anan gurin, ya fara waige2 ya ďan rage murya cikin gulma yace amma fa alhj bat--- maganarshi ta katse sakamakon kiranshi da yaji madam dinshi nayi, da sauri yace alhj bari in tafi sai anjima ya ruga ciki da gudu, alhj basheer a zuciyarshi yace ko bata dame ya ke so ya fada mishi oho? ya ďaga kafadarshi kawai ya dawo ciki dan yayi magana da mahaifiyar oyiza, Guri na musamman maman oyiza ta bawa alhj basheer ya zauna tana yashe hakori cikin murna dan taga gurin ďana tarko, cikin girmamawa suka gaisa, saida shuru ya đan ratsa na kusan 2mins sannan alhj basheer ya fara magana yace madam naga yarinya a gurinki ne kuma inaso, wallhy da aure nake sonta ba yaudararku zanyi ba, ni in kin amince ma a cikin sati biyu a gama komai na maganar aure, maman oyiza tayi ajiyar zuciya cikin gurbatacciyar hausarta tana girgiza kai tace anya kuwa gaskiya bazan iya ba bahaushe oyiza ba, kaiii bazan iya ba alhj hausawa basu cika rik'e mata ba, yayi murmushi yace wasu dai madam ai ba duka aka taru aka zama daya ba, tace ummm haka ne amma gaskiya--- alhj basheer ya katseta yace madam na barki kije kiyi tunani, zan dawo nan da 2days sai inji abin da kika yanke ya ajiye mata wasu kudin a gabanta sannan ya tashi ya tafi.... Mrs tijjani shattima..... [15/12 09:32] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 6⃣ By Aysha Ya'u Kurah Jujjuya kuďin maman oyiza takeyi cikin fargaba dan ita a tunaninta harka kawai zaiyi da ďiyarta su tatsi kudi su bar banza, sai kuma gashi da aure yazo musu, ita kuwa sam bazata iya aurawa ďiyarta bahaushe ba tafi son kabilarta kuma dan garinsu wato OKENE, mikewa tayi ta shiga wani ďan lungu da oyiza ke yawan zama kullum in tazo abuja, waya takeyi tana dariya cikin murnar da uwarta ta kasa gane daga inda murnar ta samo asali, zama tayi kusa da ita tana mata magana, oyiza tayi saurin katse wayar da takeyi ta kalli mamanta, maman oyiza ta dafa ta tace sofy mun shiga cikin matsala, oyiza ta haďe rai tace matsalar me mum, maman oyiza ta share gumin da ya tsatstsafo mata ta labarta ma oyiza duk yadda sukayi da alhj basheer, cikin damuwa tace ni bansan me yasa kika fito har kika kai mishi abinci ba, ke da ko ruwa bakya kai ma customers in kina gurin nan, oyiza tayi dariyar farin ciki a zuciyarta tace thank uu "Chummy lord" ta kalli mamanta tace mum wannan shine matsala? ay wannan is a blessn to us, kinsan irin dukiyar da yake dashi ne, kuma kinsan abun dadin bai taba haihuwa ba, maman oyiza ta saki baki tace a ina kika san bai taba haihuwa ba, gaban oyiza ya fadi amma ta dake tace john ne ya fada min, mamanta tace koma dai menene ni bana son auren bahaushe, oyiza ta dafa mamanta tace mum karki fara wannan maganar ma saboda bazai yiwu ba, kawai in yazo kice mishi eh mun shirya yazo ayi maganar aure, maman oyiza cikin bacin rai tace kina hauka ne, oyiza cikin fushi tace yess am mad in dai akan kuďi ne, kuma duk wanda ya nemi shiga tsakanina da samun kuďi ko waye wil fc d consequences,.. Maman oyiza ta mike tace to zanga yadda za'ayi ki aureshi tunda ke baki da hankali kina zuwa 1yr ya koroki in dai bahaushe ne ki ma cire a ranki dan I swear bazan bari ya shigo ko gate din restaurant dinnan ba bare yazo jin wani feedbk ta wuce tana masifa, Idon oyiza yayi jawur nan da nan fuskarta ma ta rikiďa ta zama jawur gunin ban tsoro, ta mike kamar walkiya ta wuce motarta taja tayi gida, wani jan akwati ta bude ta dakko wani farin kyalle da wata jar baby kamar sassakar laka, wani kirari tayi mai karfi da ya girgiza gidan da take ciki, cikin second uku wata mace ta bayyana a gabanta cikin jajayen kaya, "fitsarin tsoro na saki ganin halittar wannan matar jikina take ya fara rawa idona ya ciko da kwalla a zuciyata nace duk "Badiyya" ce ta sani wannan bin diddigin gashi na kawo kaina inda zan halaka" dakewa nayi na fara karanto adduoin neman tsari, nan na samu kwarin gwiwar kai kunnena da idona gurin abun da sukeyi, oyiza na hango tayi ma matar da naji ta kira da "Chummy lord" sujjada (wa'iyazubillah) chummy tasa ma oyiza wani nannaďaďďen farin yadi a kanta tace "u are safe wit me by ur side",

Table of Contents

Chapters

61 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});