Chapter 16
Chapter 16
mulki akayi kenan, ke Amirah koma gurinki itama ta dawo gurinta, Amirah ta buďe kofar zata fita Afeeya tace saidai fa mu zauna tare a baya, amirah tace kaji ko yaya, wallhy tun ďazu nake ce mata ta dawo nan taki, kallonta yayi ta mudubi yayi dariya yace amirah shigo muje, suna isa kofar gida ta buďe motar ta shige ba tare da tabi takan kayan da ya siyo musu ba, Amirah ta kwashi nata kayan ta shige gida itama, jabeer ya gyara parking ya kwaso kayan ya fito dasu ya shiga gidansu, kwance ya sameta can karshen gadon hajja tayi ruf da ciki hajja na mata magana tayi banza da ita, jabeer ya zauna bakin gadon ya gaida hajja ta amsa tace yau kuma me kayi ma mutuniyar taka, jabeer yayi dariya yace wallhy babu abinda nayi mata rigima ce kawai, Afeeya ta ďago idonta a kankance tace har kana wallhy, ya kalleta yace to me akayi, tace nima bansani ba, ta mayar da kanta kan katifar ita kanta bata san me zata ce ya mata ba ita dai tasan taji masifaffan zafin ganinshi da tayi da wata, juyin duniya yayi ta faďa mishi abinda yayi mata amma sam taki ďago kai ma bare ta bashi amsa, hajja taja tsaki tace tashi ka tafi ka rabu da ja'ira da kanta zata nemeka, in ba iskanci ba babu abin da aka ma mutum ya hau fushi, to in kin ga dama ki fashe,, jabeer zaiyi magana ya ji wayarshi na ringing, ya mike da sauri yace hajja dan Allah ki rarrasheta kafin na dawo tun dazu Affan ke jira na, hajja tayi tsaki tace ni ban iya wacce ka iya ba, ya fita yana dariya. .. Sai bayan isha suka rabu Affan ya wuce gida, ya na sa kafarshi cikin gidansu yaji muguwar faduwar gaba, wucewa ciki yayi a hankali jikinshi a mace ya shiga dakin mahaifiyarshi, zama yayi ya dafe kanshi yana jiranta dan a tunaninshi tana bayi ne,, wani irin ihu yaji mai firgitarwa ya mike da sauri yana kasa kunne yaji daga inda ihun ya fito, kafa kunnenshi yayi a jikin toilet yaji ba alamar mutum a ciki, umma... umma.. ya kira sunanta sau biyu yaji shuru ya tura bayin, juyawa yayi da sauri da yaga bata yana kwala kiranta, muryoyin mutane ya dinga ji a can saman gidansu gurin shan iska, a hankali ya karasa gurin yana leke a tsorace saboda muryoyin da yaji harda ta maza a ciki, wani razanannan ihu ya saki haďe da faduwa kasa sumamme sakamakon abinda idanuwanshi suka gani..... Mrs tijjani shattima.... [15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 1⃣9⃣ By Aysha Ya'u Kurah A gigice oyiza da wasu maza suka saki zeenatu da babu alamar numfashi a tare da ita ta faďi timm a kasa, kan Affan sukayi da gudu oyizah ta ďago shi cikin tashin hankali tana faďin shikenan asirina ya tonu, na shiga uku na lalace, wani bakin kato ya yarda wuka da farin kyallen hannunshi yace yanzu ya zamuyi kenan, dayan cikin dakewa yace mu gama da mamanshi sai mu dawo kanshi, oyiza ta girgiza kanta tace Nooo mu fara dashi tukunna saboda kar ya farfaďo ya tona min asiri, bakin katon da naji sun kira da "BULADUNA" yace yanzu me kike so mu mishi, oyizah ta runtse idonta a zuciyarta tace "help me my lord", cikin mintina uku dabara tazo mata ta mike da sauri tace ku kama min shi, cikin rashin fahimta sukace ina zaki kaishi, ta nuna kasa da hannunta tace anan zai karasa, kunga babu wanda zai zargeni za'a ayi tunanin faďowa yayi by mistk,, A tare suka haďa baki sukace Good idea, gaskiya oyee u are very sharp shiyasa kungiya take ji dake, tayi murmushi tace "Lts make it snppy", kar wani yazo ya cim mana thou nasan ba kowa a gida, cikin rashin imani da rashin ganin tsawon ginin bene hawa huďu suka wurgo Affan ta kai,, su kansu saida suka runtse idonsu saboda ganin tsayin gurin amma dayake zuciyarsu a kangare take nan da nan suka sake suka juyo gurin farin kyallen da zeenatu take, a firgice suka haďa baki suka ce ina ta shiga, oyizah ta kwalalo ido tana duba ko ina a gurin amma basuga koda sawun kafar zeenatu ba bare ita,, hankalinsu yayi masifar tashi suka shiga duba ko'ina na cikin gidan amma basuga zeenatu ba, oyizah ta buga tagumi tace to ina ta shiga, bana tunanin da kafarta ta tashi saboda ko sanda Affan ya ganmu Kurwarta na gurin chummy, to waye zai dauke gangar jikinta? Buladuna yace oyee kin tabbatar babu kowa a gidannan, tace babu kowa, su farida sun fita sannan na aiki mai aikinta guri mai nisa I don't think ta dawo kuma ko ta dawo ay baza ta hawo nan ba, dayan cikin kosawa yace mu tafi kawai tunda mun samu abinda mukeso me zamuyi da gangar jiki, buladuna yace hakane, lets go oyee, cikin rashin kuzari ta bisu kan buzun tsafinsu suka bace daga gidan.. Ba karamin tashin hankali suka shiga ba da chummy tace kurwar zeenatu ko 5mints baiyi ba ta nemeshi ta rasa, oyizah idonta yayi jawur tace to ina yaje,? kodai ya koma jikinta ne, shikenan asiri na ya tonu,,, Chummy tace calm down oyee, duk inda take yanzu hankalinta baya jikinta, saidai tana tare da wacce take mata addua yanxu haka, wannan dalilin ne kadai ya hanani dawo da ita, amma zansa suyi nesa sosai kuma zanyi mata abin da har ta mutu bazata taba motsi ba bare ta tashi ta dawo ta tona mana asiri, oyizah ta dafe kanta tace my lord wacece wacce suke tare yanzu ďin, chummy tace na kasa gane ko wacece, but koma wacece tanada kusanci da gidan, oyizah ta shiga kogin tunani, a zuciyarta tace to wacece wannan za ta dauke zeenatu, ita dai tasan babu wacce keda kusanci da zeenatu sai Abida to ko Abida ce ta dauke ta, wata zuciyar tace to ta ina abida ta shigo gidan da daddare, ta dinga tunanin da baida amsa ta kara kallon chummy cikin tsananin damuwa tace my lord ya akayi har ta samu damar guduwa,, Chummy bata iya bata amsa ba ta kalli wani katon glass din da ta tura Fanne da Fanna tayi kwafa cikin takaicin abinda sukayi mata, dariya fanne tayi tace munci dubu sai ceto, sai dai ki rufemu anan dan wallhy indai muna bude babu wani rai da zai kara salwanta a gurinku, oyizah taji kamar zata shakesu sabo takaici amma babu hali, ta kalli chummy tace my lord ya kamata a gama da yarannan if not zasu dinga bata mana aiki, chummy tayi murmushin mugunta tace very soon oyee,,, saida suka gama tsaface tsafacensu sannan kowa ya bace itama '"chummy" ta tafi gurin jigajigan matsafa na gaba da ita dan samo sababin lakanin tsafi... Mrs tijjani shattima... [15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 2⃣0⃣ By Aysha Ya'u Kurah Tsaye take cikin zauren gidansu tana leken kofar gidansu jabeer ko zata hango shi, tun bayan magriba take tsaye a gurin amma har bayan isha'i bata hango inuwarshi ba, juyawa tayi zata koma ciki kamar zatayi kuka taji an rike hannunta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61