Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 14

Chapter 14

Rabo Ajali Book 1 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

saidai fa akwai azabar kuka da masifaffen kwuiya, banda mamarta da hajja babu wanda take yarda ya ďauketa a duniya sai jabeer, shima dan tana ganinshi kullum a dakinsu kuma yana fita da ita yawo, sam bata yarda da affan dan ko ya miko hannu zai ďauketa in ta soma tsala ihu bata taba yin shuru har sai taga baya gurin, wannan dalilin yasa kullum ya shiga gidan sai yasan yadda akayi yasa ta kuka ta hanyar daukanta ta karfin tsiya,, Afeeya na da shekara biyu jabeer yasa babanshi yasata a makarantar da suke zuwa lokacin suna js2, dakyar ma'u ta yarda dan gani takeyi kamar wata hidimar ta ďaura musu, tare suke zuwa makaranta in sun dawo ya wuce gidansu da ita sai can yamma yake mayar da ita gida, duk wani kuďin break da ake bawa jabeer akan afeeya yake karewa, gata sosai takesha gurin yan samarin biyu duk da har lokacin bata cika yarda da affan ba, salma da farida ba karamin tsanarta sukayi ba, in suna cikin mota ta kallesu sai su sakar mata harara, turo baki takeyi a tsiwace irin na yara itama ta rama sai tayi lamoo a jikin jabeer ta runtse idonta dan kar su daketa, haka a skul ko takata yaro yayi bai sani ba ko yafi karfinta sai ta bishi ta rama in ya daketa taje ta faďa ma jabeer, in kuma tafi karfinshi to ta samu nama dan sam bazata raga mishi ba.... Mrs tijjani shattima.... [15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 1⃣6⃣ By Aysha Ya'u Kurah ★ bayan shekara 6★ Jabeer ne ya fito daga makarantar (buk) cikin motarshi "vibe pontiac" da L a jikinta saboda har lokacin bai kware sosai ba, waya sukeyi da Affan da ya tafi karatu egypt wata uku da suka wuce, hira sukeyi sosai cikin jin dadi da kewar juna, saida yayi parking dai2 skool din su Afeeyah sannan sukayi sallama, can ya hangota cikin yara suna dambe ita da wata yarinya yara na ihu suna musu waka, da sauri ya karasa gurin ya raba fadan ya riketa tana kuka saboda yarinyar tafi karfinta karfin hali ne kawai irin nata, fisge2 ta shiga yi ita dole sai an barta ta buga ma yarinyar dutse, tsawa jabeer ya daka mata ya rike hannunta da karfi yace wuce mu tafi ko in zaneki a gurin nan, ta kalleshi cikin mamaki dan bai taba mata magana mai karfi ba bare tsawa, yace baki ji abinda nace bane, ta saki wani razanannen ihu tana buga kafa tana kuka sosai kamar wacce ake yanka ta, tsaki yayi ya ďauketa tana tirjewa ya turata cikin mota, Safna kawarta ta miko mishi school bag da L.B dinta yasa aciki ya zagaya ya shiga, dago kanta tayi tana kuka ta hango wasu yara suna mata gwaloo, haba nan ta fara kicin kicin bude kofar tana bugawa tana ihu kamar zata tsaga motar, kashe motar yayi ya janyota jikinshi yana rarrashinta tana zillewa,. dakyar ya rarrasheta yace ta faďa mishi abin da ya haďa su, kumburo baki tayi tace dukana tayi wai dan ban sani ba na yaga mata littafi shine har da cire min beets din da mama tasa min, kuma taja min gashi da karfi, murmushi jabeer yayi dan yasan tana sane ta yaga littafin yace banason karya fadamin gaskiya tsokanarki tayi kika yaga mata ko? ta turo baki ta gyaďa kanta, yace nasani ay, kuma shine dan rashin gaskiya kika fito kuna dambe ko, bana hanaki faďa ba? idonta ya fito waje tace to ay sune suke fara neman fada na, ya zaunar da ita kan kujera ya tada mota yace munyi faďa yau babu ruwana dake, dama na siyo miki cake kuma na fasa baki, ta rike mishi hannu tana kuka tace zan daina, yace bazaki daina ba kullum haka kike faďa, ta kwantar da kanta kan hannunshi tace Allah zan daina gobe, yayi dariya yace to naji in kika kara me zan miki, ta boye fuskarta tana dariya tace hakuri zakayi mana, ya kwashe da dariya yace yarinyar nan kin raina ni da yawa, yaja motar suka wuce.. Tsayawa yayi ya siyo ma Ma'u dake fama da ciwon 'koda' tun wata biyar da suka "fruits da rake" dan shi take yawan sha ance yana wanke infection din 'koda', sannan suka wuce gida, Tun kafin ya kai kofar gidan ya hango cikowar mutane, karasowa yayi jikinshi a mace yayi parking a gefe can ya hango maza sunata alwala ana jimami, bai bi takan fruits din da ya siyo ba ya dauko schl bag da lunch box din Afeeyah ya kama hannunta zasu shiga ciki, ta dinga waige2 tana cewa yaya jabeer baka dakko ma mama raken ba,. bai kulata ba ya jata suka shiga ciki, a tsakar gida ya tarar da taron mata cikin hijab kowacce tayi tagumi, dakin Ma'u ya shiga nan ya tarar da tashin hankali, kallon mutanen dakin yakeyi ya karasa kusa da mamanshi yace ummi me ya faru, ina mama,? Abida ta share hawayenta ta nuna mishi ma'u kwance cikin likkafani, matsawa kusa da ita yayi da sauri ya bude fuskarta ya fashe da kuka sosai yana kiran sunanta, Afeeya ta matso kusa dashi jikinta a sanyaye ta rikeshi itama tana kuka, rungumeta yayi sunata kukan da ya kara sa mutanen gurin kuka, Abida cikin kuka tace ya tashi ya wuce gida, kin tafiya yayi ya haďa Asiya da Afeeya suka wuce gidansu shi kuma ya zauna akayi mata sallah tare dashi aka kaita gidanta na gaskiya,, mutuwar ma'u ta girgiza jabeer sosai saboda ba karamin shakuwa sukayi ba, ita taci kashin shi tun yana karaminshi har yasan kanshi saboda mahaifiyarshi ba mazauniya bace.. Tun daga lokacin rikon Afeeyah ya koma gurin hajja dama acan take rabin zamanta ko sanda mamanta ke da rai, jabeer kuwa wata sabuwar kulawa yake bawa Afeeyah wacce take mantar da ita rashin uwa, gaba ďaya ya daina mata faďa kuma ya hana kowa yi mata faďa, ko an kawo kararta saidai ya basu hakuri yace ay yarinyace, sosai ya shagwabata, basu rabuwa ko da na kwana ďaya ne in kuwa tafiya ta kamashi in har ya tafi to ranar ba cin abinci babu bacci, wani lokaci ma har ciwo takeyi, shiyasa yake tsoron duk wani abu da zai sa yayi tafiya ya barta, haka su zeenatu da Abida ba karamin kula sukeyi da ita ba dan sun ďauke mata komai duk da malam atiku shima yana iya kokarinshi yaga ya debe mata kewa, suwaiba kuwa mutuwar ranar ne ya taba ta amma anayin uku shikenan ta sake tama manta da wata ma'u a rayuwarta, ganin Afeeyah da kuma jarabar rashin hakurinta su kadai suke tuna mata da ta taba yin kishiya... Mrs tijjani shattima.. [15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 1⃣7⃣ By Aysha Ya'u Kurah Yar Kyakyawar budurwa ce zaune cikin bakar doguwar riga mai adon jaa a parlon ummi, duka shekarunta baza su wuce 14 ba amma in ka ganta zaka rantse ta kai 16 saboda kayataccen jikin da makerin yammata ya fara kerashi, bazan iya fadin kyawun fatarta ba saboda ya zarce misali, ita dai ba fara bace kuma sam bata dauko hanyar bakake ba, wani irin colour ne

Table of Contents

Chapters

61 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});