Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 60

Chapter 60

Rabo Ajali Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

minti ďaya kafin ta iya daga kafarta, rubutu da magunguna sosai take shansu dan kaka liman musamman yake mata jarkar rubutu tun cikinta na wata, a wannan lokacin ne wani dare ta farka da nakuda mai zafin gaske, cikin gaggawa suka kaita asibiti, likitoci sun fi karfin awa biyu akanta ana abu ďaya, Affan kuka ya fita waje yakeyi saboda jin irin kukan azabar da takeyi, ganin har lokacin ba improvement doctor ya yanke shawarar yi mata c.s saboda service dinta bai buďe ba,, alhj basheer da kanshi yasa hannu saboda yadda yaga ta galabaita, a gaggauce suka shiga da ita dakin theater suka fara aikinsu cikin kwarewa, cikin farin ciki doctr ya fito musu da jarirai mata manya manya guda biyu, da sauri zeenatu ta mike ta karbi ďaya alhj basheer ya karbi daya sunata ma doctor godiya, Affan kuwa bai bi takansu ba dakin da aka kai Afeeyah ya shiga ya zauna gefenta yana shafa kanta yana mata addu'a yana jin sonta na kara ratsa ko ina jikinshi... Kwananta hudu a asibiti aka sallameta suka koma gida aka cigaba da kula da ita da yaran dan jikinta har lokacin baiyi kwari ba,, Ranar suna yara suka Amsa sunan Asma'u (Nuwairah) da Zeenatu (Nawwarah), anyi shagalin suna cikin kwanciyar hankali dangi kowa ya halarci sunan harda su suwaiba da akayi nadamar gaske... Mrs tijjani shattima.... [15/12 09:38] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 6⃣7⃣ By Aysha Ya'u Kurah ★ 7yrs ltr ★ Tsaye take a kofar islamiyya tana jiran fitowar yara su tafi gida, tana tsaye jikin motarta da ďan cikinta na wata hudu tana siyan tsamiyar biri, ihun fitowar yara ne yasa tayi saurin mika ma mutumin kuďi ta bare daya tasa a bakinta ta fara hangen yara, can ta hango rabon faďa cikin taron yara malaman na rabawa yaron na kara tusa kanshi yana kuka yana fadin shi sai ya rama, da sauri Afeeyah ta jefa ledar hannunta cikin mota tayi gurin yaron tana faďin Oh my Word JABEER again, ta kamo hannunshi da karfi tace wuce mu tafi, ya tsala ihu yana magana cikin kuka ta make bakin tace rufe min baki masifaffe kawai, ta kalli Nawwara dake kwaso mishi takalmi tace kuna tsaye ku bazaku iya kamo hannunshi ku fito ba kun tsaya kuna kallonshi yana fada, Nuwaira tace wallhy mummy mun hanashi yaki har haurin Nawwara yayi, tsaki tayi ta bude motar ta wurgashi baya su Nuwaira suka shiga ta ja motar ta wuce tana masifa shi ko sai tsala ihu yakeyi, shop rite ta wuce dasu tayi siyayyarta ta sai musu ice cream suka fito suka wuce gurin mota, tana buďe motarta taji ihun wani yaro cikin motar kusa dasu, da sauri ta rufe kofar ta nufi gurin taga jabeer tsaye yana huci, cikin bacin rai tace me yayi maka ka dukeshi, jabeer ya turo baki cikin maganarshi ta yara yace tun da muka shigo yake kallona, Afeeyah ta dauke keyarshi da mari tace uban me zai kalla a jikinka, dan kaga bana dukanka shiyasa kake iskanci san ranka ko, ta ja hannunshi yana ihu ta turashi cikin mota ta koma ta rarrashi yaron taja mota suka wuce gida, a bakin gate suka tarar da Affan, tun kafin a bude gate din jabeer ya balle motar ya fito ya ruga gurin shi yana kuka ice cream din hannunshi duk ya zube a kasa, kwace robar yayi ya wurgar ya dagashi sama yace waye ya taba min kai, jabeer yace ba mummy bace tun a islamiyya take dukana har mukaje chopurite tana dukana tana zagina suna ta min dariya, Affan ya hade rai kamar gaske yace tun a islamiyya take dukanka har a chopurite, jabeer ya gyada kanshi, Affan yayi kwafa yace muje gidan yau sai ran kowa ya baci, suna shiga ya tarar da ita a kitchen tare da Amirah ya kalleta yace me babyna yayi miki kika dukeshi, Afeeyah tayi tsaki tace nidai dan Allah gobe ka siyo min rago wallhy canjin suna za'ayi wannan ba jabeer bane, jarabar tayi yawa, kullum sai yaro yayi dambe a islamiyya, sai shegen tsaurin ido ko kallonshi akayi sai ya daki yaro in yafi karfinshi, Amirah tayi dariya ta dungure kanshi tace gaskiya yaya Affan ka siyo mana ragon suna wannan bai amsa sunanshi ba, jabeer ya kai ma Amirah duka yana kuka Affan yace har da ke ko Amirah, to zanga mai canza mishi suna, ya kalli Afeeyah yace ke meye bakiyi ba, tace naji nayi amma bankai wannan mai katon kan ba, kuma canza suna ya zama dole in na haifi salihi sai insa mishi jabeer amma wannan JAZULI zan sa mishi, Amirah dasu Nawwara suka fita suna dariya sosai, Affan ya share ma jabeer hawaye yace rabu dasu yanzun nan zamu fita yawo ko mutum daya bazai bimu ba, jabeer ya shanye kukanshi yana ma Afeeyah gwalo, tsaki tayi ta cigaba da abinda takeyi tana mita.... Washe gari da safe suna zaune suna shan tea, kowanne jikinshi da skool uniform gwanin ban sha'awa, jabeer na zaune yana shan tean shi yana daukar bread baya ko kallon su Nuwaira, kallonshi sukeyi suna dariya dan yaci slize bread fin shida kuma ya cinye kwan gabanshi, yana jin dariyar da sukeyi kasa2 bai tanka musu ba, yana gamawa ya mike yana mika ya zagayo gefen da suke ya ďauki kofin tean Nawwara ya kwara musu a jiki ya dauke kwan plate dinta ya ruga cikin daki da gudu yana dariya, mikewa sukayi baki bude ga zafin tea ga haushin yasa sai sun canza kaya, Nuwaira da idonta ya ciko da kwalla tace wallhy sai na ma yaron nan dukan tsiya, Nawwara tace ki kyaleshi sai munje skool, Nuwaira tace wallhy a gida zai daku ji yadda ya bata min jiki, cikin fushi tayi hanyar dakin ta murďa kofar, wayar av din jikin game ta cire ta fara tsuga mishi, nan ya dinga ihu yana shigewa jikinta Nawwara ta fincikoshi tana dukanshi da hannu yana ihu yana ramawa, a gigice Afeeyah ta diro a gado ta fito tana kiran me aikinta taji ko lafiya, kafin ta kai ga shiga dakin Affan dake parlor yana jiransu har ya shige yana ta ma su Nuwaira masifa, cikin fushi Afeeyah ta kwace wayar hannunta tace dukanshi kukayi har da waya, Nuwaira ta fara kuka tace mummy ruwan zafin tea fa ya watsa mana a jikinmu kalli kayanmu, Affan yace me kuka mishi ya watsa muku nasan haka kawai bazai watsa muku ba, Nawwara tace wallhy babu abinda muka mishi, jabeer yayi saurin cewa karya takeyi dariya suke ta min, Afeeyah ta kalleshi a hassale tasa hannu zata janyoshi ya sa ihu ya shige bayan Affan yana fadin wayyo mummy kiyi hakuri, Afeeyah ta rike kanta tace wallahy yaron nan zai iya haukatar da mutum, na kusa daukar ka in mayar dakai bolar da na tsinto ka kaje can cikin yanuwanka spiders, coacroach da sauransu, jabeer ya leko yace wai haka daddy, Affan ya daukeshi suka fita yace eh mana tunda baka jin magana, Afeeyah ta kalli su Nuwaira tace tsayuwar me kuma kukeyi, ko inzo in shiryaku ne, sukayi saurin fita daga dakin suka je suka canza kaya suka wuce skool... Bayan yan kwanaki, Afeeyah na zaune

Table of Contents

Chapters

61 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});