Chapter 37
Chapter 37
tana kuka sosai tana fada mata abinda ya faru tsakaninta da Affan da su oyizah, a hankali ta ďago kanta tace hajja ni tsoro Affan dinnan yake bani wallhy, sai yayi magana kamar me hankali kuma sai ya juye mahaukaci, sannan hajja mahaukaci ma na iya yin abinda yayi min, hajja ta share hawayenta tace zai iya Afeeyah tunda yanada duk wata halittar da muke dashi kwakwalwa ce kadai ta samu matsala, Afeeya ta koma ta kwanta tace hajja to ya zaiyi yayi wanka yayi sallah, hajja tace wannan ne kuma bansani ba, tashi muyi magana kuma ki share wannan hawayen ki saurareni sosai, Afeeyah ta mike zaune tana share hawayenta tace ina jinki hajja, hajja ta kalleta sosai tace Afeeyah kuka yanzu ba naki bane, daga yadda kika bani labarin abinda safiya tayi muku ke da Affan na ďago wasu abubuwan da ke yarinta ya hanaki dagowa, tabbas rayuwar yaron nan na cikin haďarin da bashi da mataimaki sai Allah sai kuma ke da Allahn ya bashi a matsayin garkuwa, "Hajara" yau na kiraki da ainihin sunanki saboda inason in karfafa miki gwiwa dan naga kin shagwaba kanki da sunan da jabeer ya shagwaba ki dashi, dole ki jajirce kiyi amfani da damar da Allah ya baki gurin kwatowa wannan yaran yancinshi, dole kisa shi a hanya ki dinga nuna mishi hanyoyin bi masu kyau da marasa kyau, dole ko yaya ne ki fara koyawa kanki sonshi dan sonshi bashi zaisa ki manta da jabeer ba, dole duk inda yasa kafarshi kema kisata saboda kuyi shakuwar da duk abinda kika ce mishi yayi zaiyi ba musu, sannan Addu'a, dole ki jajirce ki yawaita addu'a domin itace makaminki a yanzu, dole kuma kiyi hakuri da duk abinda za'ayi miki saboda mai hakuri shi keda nasara a ko da yaushe, kina jina ko, Afeeya ta gyada kanta tace ina jinki hajja, kafin hajja ta buďe baki ta sake wata magana sukaji an tokari kofar dakin da kafa, da sauri Afeeya ta ďago tana gyara dankwallin kanta, hajja ta kalli oyizah dake musu kallon raini tace ina kwana safiya, oyizah ta kirne fuska tace bamu haďu dashi a hanya ba, hajja ta kauda kanta, salma ta karaso tace ma Afeeyah kee, kinsan karfe nawa yanzu, Afeeyah tace a'a, salma tace dan ubanki jiya me mummy tace miki, oyizah tace ai ta manta da abinda nace mata tunda ta kauda budurcinta a gurin tababbe, salma tace hmm lallai, naga alama mummy, ta kalli Afeeya tace wallhy kafin 11 ki tabbatar kin kammala komai na gidan nan in ba haka ba na rantse da Allah sai jikinki yayi tsami, oyizah tace ay ni bani da bakin magana ki ji da ita dan in har nace zan sauke fushi na akanta to wallhy dakyar zan barta da rai, salma tace ay dama mummy bai kamata ki dinga kulata ba mun isheta dan tasan babu sa'anta a gidannan, ko shi garan mijin nata bai isa ya hanamu yin komai akanta ba, Afeeyah ta mike dakyar tace ma hajja tana zuwa, hajja tace muje in tayaki, Afeeyah tace haba hajja zauna yanzu zan gama, hajja ta maida kwallar idonta tace to Afeeya, hijab ta ďauka tabi ta gefensu ta wuce ta barsu tsaye sunata habaici suna zaginta, kitchen ta shiga ta tarar dashi kaca2, nan ta shiga gyarashi ta haďe kayan wanke2 tayi ta gyara ko'ina tayi mopping, tana gamawa taji muryar farida a bayanta, da sauri ta waiga ta kalleta tace na'am me kikace, farida ta harareta tace ance ki daura rice nd stew 4 lunch akwai komai na amfani ki duba zaki gani sannan ki haďa min corslw,, salma kuma tace ki soya mata plantain ki kawo mata yanzu, Afeeyah ta gyada kanta ta wuce store din da ta hango kayan abinci, saida ta daura white rice sannan ta bare plantain, ta daura shi a wuta ta soya, ba karamin wulakanci sukayi mata ba da ta kai ma salma plantain din, Ko kallansu batayi ba ta juya ta koma kitchen ta cigaba da aikinta, sai sha biyu saura ta gama komai ta gyare ko'ina sannan ta wuce parlor da niyyar gyarawa, Zaune ta sameshi a parlon yana buga game yana ihu shi kaďai, bata kalleshi ba ta fara gyara cikin parlon, buruntu yaji ya waigo ya kura mata ido yana dariya, sam bata lura ya ganta ba tana can tana kakkabe kujeru, rungumeta taji yayi ta baya yana faďin yeeeee na ganta, Afeeyah tace dan Allah sakeni aiki nakeyi, ya saketa ya zagayo yana kallonta yace har yanzu fushi kikeyi dani, ta dauki remote ta kaishi mazauninshi ba tare da ta kalleshi ba, binta yayi a baya yace ki yi hakuri ni bansan zaki ji ciw-- dan son annabi ka kyaleni kaje ka cigaba da game dinka haba ta fadi da karfi rai a bace, hanyar waje yayi kanshi a kasa kamar zaiyi kuka, Kallo ta bishi dashi har ya fita sannan taja tsaki a hankali ta cigaba da aikinta cikin kwanciyar hankali dan har ta gama bai dawo ba, ďaki ta koma tana haki saboda yunwar da takeji ta samu hajja a kan dadduma ta idar da sallah, zubewa tayi a jikinta tana maida numfashi tace hajja yunwa nakeji, dan Allah ki samo min wani abu inci a gida, hajja ta shafa addua tace ke kuwa duk girkin nan da kikayi bakici ko kadan ba, Afeeyah tace umm banason abinda za'a kira uwata da ubana a zaga, hajja tayi murmushi a zuciyarta tace lallai mutuwar jabeer ta kashe zuciyar yarinyar nan, ta kalleta tace kinyi dai2 kici gaba da hakuri wata rana sai labari, bari inje in kawo miki abinci a gida, Afeeyah tace to hajja bari inyi sallah kafin ki dawo, Ta windon bayi ta hangoshi zaune yayi tagumi yana kallon ramin kifi, da ganinshi kasan baya cikin walwala, tsaki tayi ta cigaba da alwalarta ta fito tayi sallah, tunanin maganganun da hajja tayi mata ta dinga yi sannan ta tuno da abinda tayi mishi dazun da kuma bacin ran da ta karanta a fuskarshi, mikewa tayi ta naďe daddumar ta fito tana neman hanyar da zata sada ta da gurin kiwon kifin, da kyar ta gano hanyar ta karasa gurin ta zauna, sam baisan tazo gurin ba ta waiga gurin da taga abincinsu ta ďiba ta watsa musu, da sauri Affan ya waigo suka haďa ido ya kauda kanshi ya juya mata baya, murmushi ta kirkiro tace kayi hakuri, dazu banaso ka hanani yin aiki ne shiyasa, ya noke wuyanshi yace naki yin hakurin, ta kamo hannunshi a hankali tace Niko? yayi murmushi haďi da fari da ido kamar yana kallonta sannan ya kara haďe rai yace eh ďin, tace to juyo kaga wani abu, ya juyo yana turo baki yace meye? tayi murmushi tace fushin fuskarka zan nuna maka, ta nuna bakinshi da hannu tace kaga yadda bakinka yayi babba, sannan fuskarka tayi katuwa saboda fushi, ya kara turo bakin yayi kasa da idonshi yace to bake bace kike min ihu, tace to ai zan daina nace maka, yayi murmushi kadan yace yaushe zaki daina, tace yanzun nan, ya wangale baki ya rungumeta yana dariya sosai yace yauwa barbie na, to tashi muje can ki tayani buga kwallo, tace a'a yanzu
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61