Chapter 36
Chapter 36
ta mika mishi tayi hanyar kofa, Alhj basheer yace wai ina zaki je ne kiketa sauri haka, juyowa tayi tace umm na manta ban bawa Affan maganinshi ba, yayi murmushi yace karki damu dazu da kuna gurin Amarya na shiga na bashi, oyizah tace ka tabbatar dai2 ka bashi, alhj basheer yace kwarai kuwa dawo kiyi min tausa, oyizah ta dawo ranta a bace ta fara mishi tausa tana tunanin abinda ya kai Affan dakin da aka kai amarya, wasu irin tunani ta dinga yi dan tasan illar kebantuwar mace da namiji a guri, wani irin ihu tayi ta diro a gado tana fadin alhj na daura ruwan zafin tea a gas na manta ban kashe ba, sakkowa yayi jiki na rawa yace innalillahi wa inna ilaihir rajiun, bari inje in duba, tace koma ka kwanta alhj ka riga kasha magani, hanyar kofa yayi yace wani irin magani ay gara inje in duba kar kije wani abun ya sameki, dafe kanta tayi lokacin daya fita tana sake tunanin hanyar da zata bi, waya ta dauko da sauri ta shiga kiran salma, numbr busy aka dinga sa mata tayi tsaki ta kira farida taji a kashe, wurgi tayi da wayar tace wadannan tambadaddun kuma wayarsu taki shiga, yanzu ni ya zanyi, muryar alhj basheer taji akanta yace safiya kin tsoratani wallhy, gas a kashe yake, ta dafe kanta tace lallai tsufa ya fara zuwa min sai naga kamar ban kashe ba, yayi murmushi ya zauna haďe da rungumeta yace baki ma kunna ba a flask kika dibi ruwan, tace hakane shaff na manta ne wallhy, nan alhj basheer ya shiga faranta ranshi a jikin oyizah sakin jikinta tayi suka faranta ran juna duk da bataso hakan ba... Asubar fari oyizah ta farka a gigice sakamakon mafarkin da tayi, ko wanka batayi ba ta fita tayi dakin Affan, buga kofar takeyi kamar zata ballata tana kiran sunanshi, cikin bacci Afeeyah taji bugun kofar ta mike a hankali ta fara ture Affan da ya cikwikwiyeta hawaye kwance a gefen idonshi, kara matse jikinshi yayi da nata yana sheshekar kuka haďe da ajiyar zuciya, ba karamin tausayi ya bata ba duk da itama abar tausayin ce saboda irin azabar da tasha, bugun da mummy kema kofar ya karu muryarta ta cika cikin gidan tana masifa tana fadin in Affan bazai bude ba dan uwarki da ubanki ke bazaki bude ba, Afeeyah ta fara kokarin yi mishi dabara ta cire hannunshi ta dan turashi tasa pillow a gurin ta daura hannun kan pillown taja bargo ta rufa mishi, hijab dinta taja tana tafiya dakyar ta karasa kofar dakin da oyizah ke jijjigawa kamar zata ballata, murda kofar tayi taja ta tsaya, da karfi oyizah ta hankado kofar har saida ta sameta, kallon Afeeyah ta tsaya yi daga sama har kasa tana hararrta, ta janyo hijab dinta da karfi tayi wurgi dashi tabi duk jikinta da kallo, cikin fushi tace a ina kika kwana, Afeeyah baki na rawa tace a-a-a- -- sambatun Affan ya katseta yana kiran sunanta yana fadin wasu kalmomi na shauki haďe da matse pillow a jikinshi, oyizah tayi saurin kallon inda yake ta karasa ta cire bargon da Afeeyah ta rufa mishi, wani irin ihu ta saki hade da mayar da bargon tace na shiga uku, me kikayi mishi naga babu kaya a jikinshi, Afeeyah ta sunkuyar da kanta kasa hawaye na tsere cikin idonta, oyizah cikin hassala ta shakota tace yau sai kin fada min abinda kikayi mishi, yaudarar mahaukacin nan kikayi kika mishi fyade ko me, Afeeyah ta kara sautin kukanta tace wallhi babu abinda na mishi, oyizah ta tsinka mata mari tace karya kikeyi dan uwarki, ga shi nan babu wando a jikinshi kema kuma kalli yadda kike kin kasa tsayuwa da kyau, Afeeyah ta kasa magana sai kuka kawai takeyi, nan mummy ta cigaba da magana cikin ficewar hayyaci tana dukan Afeeyah, ihun Afeeyah ne ya tada Affan daga bacci ya mike da sauri ganin oyizah tana dukanta, baibi takan daukar wando ba ya diro daga kan gadon yasa duk iya karfinshi ya turata ta faďi kasa ya dago Afeeyah yace yi hakuri barbie me kikayi mata, Ta runste idonta da sauri ta dakko wando ta mika mishi ya karba ya fara sawa, oyizah na huci ta mike ta karaso gurinshi ta daukeshi da mari har sau biyu tace dan ubanka ni zaka ture saboda wannan kodadiyyar matar, Affan ya rike kuncinshi ya kumburo baki yana hawaye yace mummy ni kika mara, tace zan maka abinda yafi mari indai har kace zaka fara bijire min, ta kalli Afeeyah tace Affan bai taba min musu ba, bai taba bata min rai ba kullum yana kaffa2 dani amma gashi daga zuwanki Affan har tureni yayi na fađi kasa, yau sai na miki dukan tashin hankali inga uban da ya tsaya miki, da sauri Affan ya shiga tsakiya yana kuka yace mummy ni ki dukeni dan Allah ki kyaleta jiya fa naji mata ciwo, wayyyyyo oyizah ta faďi ta hankaďashi gefe tayi kan Afeeyah dake ja da baya da kyar, tana cimmata ta daga hannu zata fara dukanta alhj basheer ya shigo da sauri yace lafiya me yake faruwa anan, Da gudu Affan yayi gurin daddy yana kuka yace mummy ce zata duki barbie na daddy dan Allah ka hana ta bata da lafiya jiya muna wasa naji mata ciwo a---- alhj basheer yayi saurin toshe bakinshi yace ya isa haka, oyizah ta kirkiri dariya ta sauke hannunta kan Afeeyah tana shafawa tace wa yace maka dukanta zanyi, alhj yarinyar nan taji ciwo sosai shine nake son in kaita bayi in mata wanka shine fa take kuka shi kuma ya dauka dukanta nakeyi, alhj basheer cikin mamaki yace sannu Afeeyah, tashi kije bayi dan Allah kiyi hakuri kinga yanayinshi komai baya yinshi a hankali, Afeeyah ta kara fashewa da kuka tace dan Allah ka kaini gurin hajja, alhj basheer yace kiyi hakuri zan je in kira miki ita in gari ya waye kinji, yanzu tashi kije mummynku ta miki wanka, Afeeyah tayi saurin girgiza kanta tace wallhy zan iya, alhj basheer yace to safiya zo muje ki hado mata abinci, ya tura keyar Affan dake kallon Afeeyah shima yana kukan.. Toilet Afeeyah ta shige da sauri tasa key ta sirka ruwan zafi ta shiga ta zauna tana kuka sosai tana kiran hajja da jabeer, saida tafi minti talatin a bayi sannan ta fito a zuciyarta tana tunanin to yanzu waye zaisa Affan yayi wankan tsarki, Ďaga kafadarta tayi tasa ma dakin key tayi sallah tayi adduo'i sannan ta hau gado ta kwanta tana tunano alamuran da suka kasance tsakaninta da tababben mijinta.. Alhj basheer kuwa bayan ya je ya dauko hajja ya kaita har dakin Afeeyah da kanshi, ya fito waje yana mamakin alamarin da ya kasance tsakanin mahaukacin danshi da matarshi,, shin dama mahaukaci wanda ke da matsala a kwakwalwarshi yana iya saduwa da mace ko dai ita Afeeyar ce ta sadu dashi, tambayoyi marasa amsa ya dinga yi wa kanshi sai daga karshe ya samo mafitar yaje gurin doctr musa ya tambayeshi yadda abin yake,, [15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI◆◆ 42 By Aysha Ya'u Kurah A can gida kuwa Afeeyah na kwance kan cinyar hajja
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61