Chapter 48
Chapter 48
uku a gurin ta hango tanimu mai Guga rike da bokiti a hannunshi, da karfi ta kwala mishi kirah ya taho da sauri ya tsuguna yace hajiya gani, Afeeyah tace dan dan Allah a ina zaka samo fatanya inason a shiga cikin nan ne ayi min digging dinshi naga kamar ana gyara sauran kullum banda nan, tanimu ya rike baki yace wallhy hajiya ko katakon gurin nan ba'a yarda mu taba bare ganye bare kuma har mukai ga hakeshi, Afeeyah tace to saboda me, yace wallahu aalamu, nima ban sani ba, Afeeyah tayi tsaki tace kira min mati naga shi ke kula da flowers din gidan, da sauri ya mike yaje ya kira mati suka taho tare, dakyar da yaudara tace ma mati yazo ya hake mata saboda alhj yace za'ayi shuka ne a gurin, jin alhj ne yace yasa mati zuwa dauko fatanya ya bude gurin ya fara haka tun karfi, gefe ta koma tana addu'a tana kallonshi, yana tsakiyar hakan ne ya jiyo taurin wani abu, da sauri ya dago shi da fatanyarshi ya fara girgijeshi kasar na kakkaba, Afeeyah na hango kafar ta gane ta dabba ce, da sauri tace mati ajiye dan Allah ka samo min ruwa in dauraye hannu na, dasauri ya ajiye yayi gurin pampo, cikin azama ta karasa tayi bismillah ta dauko wannan damon tayi cikin dakinta dashi ta naďe shi cikin wani zani ta turashi karkashin gado, tana komawa gurin ta tarar da farida na balbale mati da masifah, Afeeyah ta karaso da sauri ta kalli fuskar mati gwanin tausayi tace ya akayi ne mati, mati yace hajiya saida na faďa miki ba'a taba gurin nan kika dage sai na hake shi, gashi yanzu hakan na min barazana da aikina, Afeeyah ta kalli farida dake harararta sannan ta maida kallonta ga mati tace dama wannan ce ta dauke ka aiki, ya girgiza kanshi yace a'a, Afeeyah tace to dan me zatayi sanadiyar aikinka, naga dai wannan aikinka ne, ko alhj yasan baka gyara wannan flower, mati yace a'a bai sani ba, Afeeyah tace to maza ka cigaba da aikinka tunda dama dan albashi kakeyi, farida tace ke kuma asuwa dan uwarki, Afeeyah tace ni as uwarki dan ita uwar taki, fareedah ta rike baki cikin mamaki tace mummy kike zagi, Afeeyah tace uwata ce ita ko kuma kina tunanin uwa tafi uwa ne, kai mati cigaba da aikinka in ka gama kayi watering din gurin ka rufe ni ina da abin yi, farida ta hassala ta finciko Afeeyah da karfi tace wallhy yau sai naci ubanki a gidannan, duka duka yaushe aka haifeki da zaki tsaya kina gaya ma mutane magana, Afeeyah ta haďe rai sosai tace sakeni kar muyi creating sin a gurin nan, farida tace baza'a sakeki ba, Afeeyah ta buge hannunta da karfi tace dallah sakeni, farida ta daga hannunta cikin fushi zata mareta Afeeyah tayi saurin rike hannunta tace karki fara wannan gangancin dan wallhy bazamu kare faďan nan yau ba, ki bar ganinki katuwa wallhy babu abinda zaki dauka ajikina dan abun a zuciya yake, kuma sannan da kike cewa yaushe aka haifeni to bari kiji ko jiya aka diga maniyyi na na fito yau na fiki daraja a idon duniya saboda nayi aure kuma nasamu Apple of marriage, ke fa? har yanzu kina gida babu mashinshini bare har yayi yunkurin dauka, tayi wurgi da hannunta taja tsaki ta wuce ta barta tsaye idonta jajur.... Gurin Affan ta wuce yana zaune yana kallon kifayen dake cikin fishpond, runtse idonta tayi saboda tuno mafarkin da tayi, da sauri ta mike tayi hanyar ďaki tsigar jikinta sai tashi takeyi, da sauri ya biyota dakin yana tambayarta me ya faru, a hankali take maida numfashi tace wallhy na tsani ganin kifayen nan, dan Allah muje gurin daddy yasa a fitar dasu daga gidan nan, Affan ya bata rai yace kifin mummy ne fa, bazata bari a fitar dasu ba, Afeeyah ta fara kakarin amai ta mike ta shiga bayi tana kakarin karya tana kuka kamar zata mutu, da gudu ya tafi dakin daddy yana fadin daddy kazo Afeeyah zata mutu, da sauri ya tashi ya fita yace tana ina, Affan yace tana bayi daddy, da gudu ya shiga dakin ya tarar da ita kofar bayin tana haki kamar da gaske, karasowa yayi da sauri yace me ya sameki, Affan yace daddy wai kifayen nan ne ke bata tsoro, Alhj basheer yace wani irin tsoro kuma, Afeeyah tace wallhy daddy kullum sai nayi mafarkinsu bana iya bacci da daddare, alhj basheer yace subhanallahi to gaskiya gara a fitar dasu daga gidannan dan kar su shafi lafiyar dan cikin ki, oyizah da ta shigo dakin dan taci uban Afeeyah akan abinda tayi ma farida tace baka isa ba wallhy, babu wanda zai fitar min da kifi, ance dole sai kinje gurin ne bare ki gansu, Afeeyah ta kara narkewa tace amma mummy ay a gidan suke, dan Allah kiyi hakuri a fitar dasu wallahy suna firgitani cikin dare, oyizah tace to zanga uban da ya isa ya fitar min da kifaye daga cikin gidan nan, alhj basheer yace haba safiya, ni bansan amfanin kifayen nan ba, ace shekara uku ana kiwon kifaye basa girma saidai su dinga cin abinci kullum, gaskiya yanzu za'a fitar dasu daga gidan nan kije can fili na na Na'ibawa ki cigaba da kiwata su, oyizah tace haba alhj yanzu saboda yarinyar nan tace bata son abu shin--- yayi saurin katseta yace saboda kar mu shiga hakkinta ita da abin da ke cikinta karki fassara maganar dan Allah yasa kai ya fita.., oyizah ta kalli Afeeyah ranta a bace ji takeyi kamar ta shaketa ta huta, mikewa Afeeyah tayi tana gyara jikinta tana murmushi tace mummy bakiji daddy na kiranki bane, oyizah ta harareta sama da kasa tayi kwafa tace billahil lazi sai kin gane ba'a shiga gonata, tasa kai ta fita, Afeeyah tace gonarki na nawa kuma, ta karshen ta rage in shiga in saki nometa da hannunki.. Karashe 54 Ba karamin tataburza akasha da oyizah ba gurin fitar da kifayen nan, saida alhj basheer ya nuna mata matukar bacin ranshi sannan ta yarda aka kwashesu ruwan ciki na yauki da kyar aka gama kwashewa, ana sakin ruwan wani irin wari ya gauraye gurin kowa a gurin saida ya toshe hancinshi, da gudu mati ya ruga ciki ya samu oyizah zaune tayi tagumi yace hajiya an gama kwashewa, wani irin harara ta sakar mishi cikin tsawa tace dazu saboda ka rik'a shine ka hake flowers din dana hanaku tabawa ko, mati ya marairaice fuska yace alqur'an hajiya sani akayi, tace ka fada min abinda ka hako a gurin, yace na rantse da---- babu abinda ya hako mummy, Afeeyah ta katseta, tace a gabana ya gama gyarawa akwai abin da kika binne a gurin ne, oyizah ta dafe kanta ta dago tace kan ubanki na binne, Afeeyah tayi gaba tana dariya tace kan ubana tauri gareshi, oyizah ta kalli mati tace bace min da gani banza shashasha, da sauri ya mike ya fita yana bata hakuri, wani irin juyawa taji kanta nayi saboda abin da ke shirin faruwa da ita yau, farin cikinta daya da mati yace bai hako komai ba, to ya zatayi da wadanan kifayen tsafin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61