Chapter 47
Chapter 47
ganin abubuwan da suka taba faruwa a gurin kuma yake ganinsu kamar zanen cartoon, fuskar zeenatu ce take mishi gizo yanata so ya gano ko wacece saboda dishi2 yake ganinta, rike kanshi yayi dasauri bakinshi na rawa a hankali ya furta U-M-M-A,..... .. Mrs tijjani shattima... [15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah Maimaita sunan ya dinga yi yana ja da baya kanshi na juyawa saboda yadda abubuwan ke zuwan mishi cikin kwakwalwarshi, a firgice Afeeyah ta kamashi tana faďin me ya faru, girgiza kanshi yayi da karfi ya runtse idonshi yace dan Allah ki sakko dani ki kaini ďaki, Afeeyah cikin tsoro ta rike hannunshi taja shi tana waigen gurin ko itama zata ga abin da yake gani, daki ta wuce dashi ta zaunar dashi ta tsuguna a gabanshi har lokacin bai buďe idonshi, a hankali tace ka buďe idonka, kara runtse idon yayi yana girgiza kanshi, Afeeyah tace a daki fa muke ka bude idonka ka gani babu komai anan, a hankali ya fara bude idonshi har ya bude su gaba ďaya ya saukesu a kan Afeeyah, Afeeyah tace kaga ni ba komai ko, ya gyaďa mata kai, tace to me ka gani a can saman, ya ďaga kanshi sama yace babu komai sai fan, Afeeyah ta dawo kusa dashi tace ina nufin a sama inda muka je, rufe idonshi yayi shi kanshi yana son tuno abinda ya gani duk da bai gansu clear ba amma yasan ya gane fuskar ďaya a cikinsu,, bude idonshi yayi dan ya kasa tuno fuskar da ya ambaci sunanta a sama, kallon Afeeyah yayi yace ni ban ga komai ba, Afeeyah tace kagani mana, baza dai ka faďa min ba ko, ya tabe baki yace ni na manta kome na gani, Afeeyah tace to shikenan, tashi muje muyi sallah magriba tayi, ba musu ya mike ya bita fuskar da ya gani a sama tana ta mishi gizo amma sam ya kasa tuna ta.... Zaune take a gefen gadonta rike da turaren da kaka liman ya bata a hannunta tana shafa shi tana addu'a kamar yadda ta saba, tofe jikin Affan tayi da addu'a sannan ta kwanta tana istigfari har bacci yayi gaba da ita,,,, Mafarki***** Tafe take a cikin gidan tana bin inda bata taba bi ba tun zuwanta gidan a zuciyarta tana yabawa da kyau da tsarin gidan,, Kamar giftawar walkiya ta hango wani katon DAMO yana bin wata mata tana gudu tana salati haďe da ihun neman ďauki, da sauri ta bisu tana addu'a zuciyarta cike da tsoron wannan damon dan bata taba ganin suffa irin tashi ba, ja da baya tayi saboda yadda ta hango wannan damon ya hankaďa matar cikin wani kewayayyen flower bed ya haye kanta, tun tana jiyo ihun matar har ta daina jiyowa saboda matar ta nitse ciki sai tashin kura mai karfi kawai take gani,,, a firgice ta juya jikinta na rawa ta hango wannan damon ya fito daga cikin flower bed din yayi gurin fishpond, yana zuwa gurin ya rikiďa ya koma kifi ya shiga ciki,, a hankali ta tako ta leka cikin ramin ta hango kifayen sun cure kansu sun zama kifi ďaya, a gigice ta koma baya tana sauke numfashi tana fadin "innalillahi wa inna ilaihir rajiu'n," dan ganin yadda kifayen nan suka cure ba karamin daga hankalinta yayi ba, cikin sassarfa tayi hanyar daki, anan ne ta haďu da wani tashin hankalin dan ganin wata guntuwar halitta tayi a kofar ďakin oyizah tayi wuf ta shige ta kofa ba tare da ta buďe ba, nan jikinta ya fara rawa ta leka ta window ta hango wannan halittar ta haye gado ta nutse cikin katifar, wata dariya taji an saki mai karfi haďe da guguwar da ta fito da wani mugun bakin hayaki daga karkashin gadon, da sauri ta juya zata koma ďaki taji haushin karnuka a bayanta, tana waigawa taga bakaken karnika sun fi ďari sun doso inda take suna haushi kamar zasu tsaga gidan, a razane ta fara gudu tana fadin "hasbunallahu wa ni'mal wakil," bin ta karnunkan suka fara yi da gudu suna kara yin haushi, tana zuwa kofar dakinta taji an taďiyeta ta fadi kasa sosai, ja baya ta farayi tana kara karanto adduoi da karfi tana kuka, wani irin tsalle wani katon kare yayi zai hau kanta, a razane ta runtse idonta ta saki ihu mai karfi haďe da tashi daga baccin da takeyi, Affan ta gani a zaune yayi tagumi yana kallonta, kauda kanta tayi ta janyo wani zani a gefenta tana share zufar da ta jikata tana fadin "'A'oothu bikalimaatil-laahit-taammaati min ghadhabihi wa 'iqaabihi, wa sharri 'ibaadihi, wa min hamazaatish-shayaateeni wa 'an yahdhuroon."" Singlet ďinshi yasa a gefen kunnenta yana share mata zufar da take gangaro mata daga kanta, juyowa tayi ta kalleshi tace har ka tashi, karfe hudu fa yanzu, ya karkatar da kanshi gefe idonshi ya ciko da kwalla saboda mafarkin mahaifiyarshi yayi amma sam ya kasa tina mafarkin, da sauri tasa hannu tana share mishi kwallar idonshi tace menene,? A hankali ya kwanta lamo a jikinta yana kara zana fuskar zeenatu a cikin kwakwalwarshi,, shafa kanshi ta fara yi tana karanto addu'a tana tofa mishi a kanshi har bacci ya ďaukeshi, haka suka kasance a wannan daren Afeeyah bata koma bacci ba dan tana matukar tsoron ta runtse idonta ta kara yin wani mafarkin.... Mrs tijjani shattima.... [15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5⃣4⃣ By Aysha Ya'u Kurah Washe gari sukuku ta gama aikinta, sai da suka karya sannan ta kirah kaka liman tayi mishi bayanin abubuwan da ta gani a cikin mafarkinta, cikin mamaki yace na faďa miki mugun tsafine dankare cikin gidan nan, yanzu gurare uku zakiyi aikin kisa a ranki Allah na tare dake, ki tabbatar yau kinsa an hake wannan flower duk abinda kika gani a ciki ki cire shi, sannan ki tabbatar wadannan kifayen yau basu kwana a gidan nan ba, kisan duk irin dabarar da zakiyi kisa a fitar dasu daga cikin gidan a wanke gurin ya zamana ba komai a ciki, sannan guri na uku shine mai wuyar, yadda zakiyi ki shiga wannan dakin nata har ki iya bankade karkashin gadonta, Afeeyah dai ta gama tsorata matuka idonta ya ciko da kwalla tace kaka duka suna da wahala, wallhy har yanzu jikina rawa yakeyi, yace nasani jikata nasan suna da matukar wahala amma Allah zai mayar maki dasu masu sauki daga kin fara, dan Allah karki ji tsoro zan tayaki addu'a ina daga nan, Allah zai taimakeki saboda niyyarki mai kyau ce, kisan duk yadda zakiyi ki bankade na karkashin gadon nan dan duk wasu alkadaranta anan suke, in mun gama da wannan zan fassara miki na karnunakan nan, jiki a sanyaye Afeeyah tace to kaka nagode sai anjima, yace to sai anjima Allah yayi miki albarka tace ameen kaka... Karfe 11am ta fito daga ďakinta ta fara bin hanyar da tabi cikin mafarkinta, sannu a hankali take tafiya har saida kafarta ta sada ta da wannan kewayayyen flower bed ďin da farida ke raya shi da ruwa babu dare babu rana,, karasawa tayi gurin flower ta leka ciki dan tasan duk dabarar da zatayi a hake mata gurin, ta kai minti
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61