Chapter 10
Chapter 10
kar ka bawa kowa kaji, bakin suwaiba ya kasa rufuwa tanata godiya kamar wacce akayi ma kyautar aljanna, oyiza tace haba ba komai ay zaman tare ya wuce komai nima kin min abinda ya fi wannan, har gate ta raka suwaiba tana kallon Abulbait saida ya shanye tass sannan ta juya gida, Suwaiba da rawa ta shiga gida tanata ďaga kuďin sama tana nunawa ma'u dake ma Asiya yar Abida kitso, rawa takeyi tana habaici wai wata saidai bauta amma bata samun kudi, kullum aikinta renon yayan da ba nata ba daga a bata ragowar abinci sai a bata na batarwa, Ma'u ko kallonta batayi ba ta karasa ma asiya kitso tayi mata wanka ta bata abinci ta goyata kafin mamanta ta dawo daga gurin aiki,,, Tun bayan isha'i Abulbait ke kakarin amai kamar zai amayar da yayan hanjinshi, jike jike suwaiba ke tayi mishi tana bashi amma ina amai yaki tsayawa, kudin da oyiza ta bata ta kalla a zuciyarta tace nasan yanzu in nace zan kaishi asibiti zan kashe fin dubu biyu, ta maxa ta mayar dasu tace inaa a gida zaka zauna bari in jiķa maka tazargade dan da gani aman hakori ne, tashi tayi tana bincika tazargade bata gani ba, ta duba ko ina na dakin amma bata ganshi ba kuma tasan tana dashi ko dazu ta ganshi, mikewa tayi ta fita da gudu ta shiga gurin hajja dan bata rabo dashi, hajja ta dubo ta mika mata tace Allah ya bashi lafiya, tace ameen ta fita da gudu, tana shiga ďaki ta tarar da gawarshi bakinshi duk ya baci da jini, wani irin ihu ta saki tana jijjigashi tana kiran sunanshi, da gudu hajja da ma'u suka shigo cikin dakin, ganin Abulbait ya daga musu hankali hajja ta daukeshi tana dubashi ko da sauran numfashi, girgiza kanta tayi tace saidai kiyi hakuri suwaiba Allah ya karbi abinshi, ta kara sa ihu tana kuka tana birgima kamar tababbiya, dakyar aka lallasheta tayi shuru akayi mishi wanka aka suturceshi malam atiku ya daukeshi ya kaishi dakinshi yayi kwanan keso acan... Aiki sosai chummy takeyi ma oyiza akan ta samu cikin ďa namiji, tace mata ta nesanci alhj basheer har tsawon kwana uku, a ranar na hudun ne zata bata magani sai tasa ya kusance ta, haka kuwa akayi oyiza ta kauracewa shimfidar alhj basheer gashi mabukaci gashi kuma ta hanashi kusantar zeenatu, abin na damunshi amma haka ya daure dan kar ya bata mata rai.. Suna zaune a kofar gidanshi shi da alhj bara'u suna hirar rayuwa, alhj bara'u ya tuno da wani tsumi a motarshi ya shiga ya dakko ya mikawa alhj basheer daya, alhj basheer yace na menene wannan, alhj bara'u yayi dariya yace goggo ta aikomin shi daga daura maganin basir ne, alhj basheer ya fara sha yace lallai wannan irin bauri haka da basu sa zuma ba dakyar zai shawu, sai gurin sha ďaya suka rabu kowa ya shiga gidanshi, a parlor ya tarar da oyiza cikin wata matsiyaciyar shiga mai tada sha'awa, karasowa yayi kusa da ita ya zauna, matsawa tayi sosai tace meye haka kuma, idonshi yayi ja yace ki taimakeni safiyya, , tayi tsaki ta mike tace in taimakeka akan me, nifa banason jaraba na fada maka kayi min hakuri na tsawon 3dys jibi ne fa , ni banason gajen hakuri walhy, ta wuce ciki ya bita da sauri tayi maza tasa keyy ta datse dakin,, ya koma ya zauna cikin tashin hankali, mararshi yaji tana murďa mishi sosai ya rasa yadda zaiyi sai juyi yakeyi, kamar an mintsileshi ya mike rike da mararshi ya wuce dakin zeenatu, tana zaune tana addua tana kai kukanta gurin Allah ya murda kofar ya shigo, waigowa tayi ta kalleshi ta mike da sauri saboda yadda taga idonshi yayi ja, karasawa tayi kusa dashi cikin damuwa ta rikeshi tace lafy me ya sameka, kankameta yayi yana fitar da wani wahalallen numfashi yace ki taimakeni zeenatu, dan Allah ki taimakeni in sauke nauyin da rataya a wuyana akanki saboda ina cikin mawuyacin hali, ta rikeshi sosai itama tace babu taimako tsakanin mata da miji, duk lokacin da kake bukatata a shirye nake in amsa kiranka, ya sauke ajiyar zuciya yace Allah ya miki albarka zeenatu, nan suka shiga faranta ran junansu, tabbas zuciyarshi tayi missing zeenatu ta ko wane bangare amma ya rasa meye ya tokare wani shashi nata har baya iya kyautata mata, Alhj basheer ya ji dadin wannan daren saboda yayi gamsuwar da ya dade baiyi ba, ga zeenatu ma haka abin yake domin ganin daren tayi kamar duk yafi sauran darurruka amma ta dangantashi da missing din mijinta da tayi, sai da yayi wanka a dakinta yana sa mata albarka sannan ya fita cikin tsananin ciwon kan da yarasa dalilinshi, a daren ranar Alhj basheer da zazzabi mai zafi ya kwana saukinta ma ya sauke wani nauyin, sai kawai yaji da na zazzabin..... Mrs tijjani shattima.... [15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 1⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah Satin Alhj basheer daya yana zazzabi har saida yasha allurai, zeenatu ke kula dashi dan oyiza na fushi dashi tun da ta ganshi ya fito daga dakin zeenatu a ranar, Ga kuma maganin da chummy ta bata ya wuce ka'idar amfaninshi saboda ciwon da yakeyi, a ranar da taga alamun yaji sauki ne ta fara neman hanyar da zatayi amfani da maganin har ya kusanceta, haka kuwa akayi sai da tasan duk yadda tayi da kissa da yaudara har ya kusanceta,, oyiza ta kasance cikin farin ciki a wannan dare dan gani take ma har ta haifi ďan komai ya dawo under her... 4mnts ltr Zeenatu ce zaune suna hirah da Abida dake da tsohon ciki, Abida ta kalli zeenatu tace matar nan fa ni ban gane miki ba, tun wata biyu da suka wuce kika wani canza kikayi fresh, yanzu kuma gaba daya kin cika famm sai kace me ciki, zeenatu ta shafa cikinta tace sai kace yin cikin wasan yara ne, ko sign fa ban taba ji ba, Abida tace ji ki da wata magana, akwai cikin da haka yake ba'a taba ganeshi sai in ya fito da kanshi kuma wallhy alamu sun nuna cikin nan ya dan dade a jikinki, zeenatu tayi dariya sosai tace to doctr Abida naji bayaninki, dama ana jini in ana da ciki, Abida tace nawa akayi kedai ina zuwa, gida ta shiga ta dauko ragowar "pt strip" din da tayi amfani dashi farkon cikinta sannan ta dawo ta bata kwalba tace taje tayi fitsari, zeenatu ta mike tana dariya tace Abida kenan wahala kawai zaki bawa kanki, Abida tace tunda ba ke zaki wahala ba meye na compln, ta yi dariya hade da shiga bayi tayi fitsari ta fito ta mika mata kwalbar, Wani irin ihun murna Abida tayi da taga postive, ta kalli zeenatu tace wallhy nayi tunanin hakan, wayyo dadi kasheni, zeenatu a ruďe ta shafa cikinta tace kina nufin ciki gareni, u mean akwai halitta mai rai a cikina, Abida tace sosai ma kuwa in baki yarda ki shirya gobe kafin na tafi karbar hutun haihuwa muje asibiti, zeenatu idonta ya ciko da kwallar farin ciki tace Abida bansan irin farin cikin da zanyi ba in har wannan maganar taki
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61