Chapter 43
Chapter 43
kara zama shuru kafin ta tashi tayi musu sallama haďe da jaddada ma hajja akan ta kula da Afeeyah ta dinga cin abinci akai2, cikin mamaki hajja ta kalli Afeeyah tace kin ga matar nan yadda ta canza kamar ba ita ba, gaskiya naji dadin yadda ta nuna kulawarta gareki ga dukkan alamu ta saduda ta fara sonki, Afeeyah ta juyar da kanta gefe a zuciyarta tace kwarai kuwa tana matukar son kasheni hajja ai dole ta kula dani kafin hakanta ya cimma ruwa, buďe kulolin abincin hajja tayi tana fadin masha Allah irin wadannan namomi haka, Afeeyah tayi saurin mikewa tace hajja dan Allah a ina zan samu agwaluma ko cashew anan gurin, hajja tace aiko akwai wani mai agwaluma da na gani anan waje bari in duba Allah yasa bai tafi ba, Afeeyah tace ameen dan Allah hajja ya baki mai tsami sosai, hajja tace to ta fita da sauri, tana fita Afeeyah ta mike ta kwashi kulolin abincin tayi waje dasu ta zuba a bola tayi saurin komawa daki, ko minti biyar hajja batayi ba ta dawo da agwaluma cikin leda ta mika mata, kwanciya Afeeyah tayi ta dauki agwaluma daya ta fasa ta fara sha, salatin hajja ne yasata juyowa da sauri tace lafiya hajja, hajja tace kulolin ne naga babu komai, Afeeyah tace eh na cinye baki ga dama na mutum daya ta yi ba, hajja tace daga fita ta har kin cinye, Afeeyah tace eh mana to nawa abincin yake, hajja tace shine dan bakar mugunta ko naman baki ragemin ba, Afeeyah tayi dariya tace ke kuma nama ne aranki sai kace wata kurah, hajja tace waya sani ko kurar ce gaskiya kin shiga hakkina, Afeeyah tace karki damu hajja nah anjima nasan zamu samu wasu naman, hajja tayi tsaki ta tashi ta fita wanko coolers din... Bayan isha'i kaka liman ya dawo asibitin, sun dade suna hirah da hajja kafin ta basu guri shi da Afeeyah, kaka liman ya kalli Afeeyah yace dazu muna magana bamu gama ba na tafi, yanzu sai muyi sauri dan naji gobe za'a sallameku ko, Afeeyah tace eh, kaka liman yace nima goben zan koma, da fatan duk abubuwan da na fada miki dazu kin fahimcesu ko, Afeeyah ta gyada kanta, yace yauwa to yanzu sai ki faďa min abinda kika gani, nan Afeeyah ta faďa mishi duk abinda ta gani jiya da daddare, kaka liman ya jinjina kanshi yace wannan shine abinda nakeso Allah ya nuna miki dan nasan da na faďa miki hakan tun farko to tsoro bazai barki ki shiga gidan ba ma bare har tausayin affan ya shigeki ki yarda da taimakon da zakiyi, wannan abun da kika gani shi jabeer ya gani amma nashi ya banbanta da naki saboda shi yaji suna tsafin ne akan Affan da mahaifiyarshi, shin tunda kika shiga gidan kinji ko sau ďaya alhj yayi maganar zeenatu, Afeeyah ta gyada kanta, kaka liman yace to bashi ba ma har yan uwanta da makusantanta basa iya maganarta ko ke kin taba tuna ta tun bacewarta, cikin mamaki Afeeyah tace a'a kaka, kaka liman yace mugun asiri akayi mata, karyewar asirin na farko shine jin da jabeer yayi mata har ya sanar da ni, a aikin da nayi na gano laya ce aka turata cikin bakin DAMO aka binne ta anan cikin gidan da kuke, Afeeyah ta zaro idonta tace a cikin gidan? yace kwarai kuwa, sannan duk wasu asiran da tayi a cikin gidan ta binnesu da yawansu bansan takamaimai inda ta binne ba amma suna cikin gidan, in har Allah ya taimakemu muka san inda suke har muka ciresu to saukin abun yazo dan mun riga mun gama wasu ni da jabeer karashen ne wannan kuma sune masu wahalar, Afeeyah ta jinjina kanta tace to kaka ya za'ayi musan inda tayi binne binnen, kaka liman yace shine yanzu abinda nake tunani, hannu yasa a aljihu ya ciro wata bakar leda, bude ledar yayi ya fito da wasu layu guda biyu da wani ruwan turare sai garin magani, layun ya fara mika mata yace rike wadannan layun, dafatan zaki jajirce akan duk abinda zaki gani, Afeeyah tayi kulu kulu da ido tace kaka banyi yarinya da daukar wannan kasadar ba kuwa, kaka liman yayi dariya yace Afeeyah kenan sai kiga abinda zakiyi ni bazan iya yinshi ba saboda wani lokacin kwakwalwar yaro tafi ta babba kaifin rike abu, Afeeyah ta gyada kanta tace to Allah ya bani juriyar iyawa yace ameen abinda ya kamata ki fadi kenan, wadannan layun a karkashin pillown ki zaki sasu, in zaki kwanta kiyi alwala kiyi sallah kiyi addu'a sosai akan Allah ya bayyana miki guraren da akayi wadannan binne binne, sannan ki shafa wannan turaren a jikinki ki kwanta kina mai kyautata niyya, in shaa Allah cikin kwana bakwai Allah zai nuna gurin da suke, duk wani abun tsoron da zaki gani na rokeki ki daure kar wannan tsoron ya sare gwiwarki, ke kadaice garkuwar bayin Allahn nan, in har kika sare to ki sani babu wani wanda zai iya daurewa yayi wannan aikin, Afeeyah ta gyaďa kanta tace in shaa Allahu kaka zan daure, nasan ina tare da Allah da kuma kai, yace masha Allah, sannan wannan maganin ki dinga ba Affan yana sha, kafin kwana bakwan nan zai dinga yin wasu abubuwa wadanda zasu dinga dawo dashi cikin hayyacinshi ya dinga tunanin abubuwan mamakin da suka faru dashi a shuďaďdun lokuta, kin gane bayanin ko, Afeeyah ta gyada kanta tace eh na gane, to amma kaka yaya zanyi in na gansu, kaka liman ya mike yace wannan kuma shawararki ce, in kiga zaki iya ciresu ki taimaki uba da kakar abin dake cikinki to in kuma zaki barsu su dawwama a haka nidai na gama nawa yanzu naki kadai ya rage sai mu barma Allah sauran, Afeeyah tace to kaka nagode sosai, ya miko mata wayarshi yace samin numberki kiyi flashing in wani abu ya shige miki duhu kya nemeni, Afeeyah ta amsa tasa mishi numbrta sukayi sallama ta bishi da kallo har ya bace ma ganinta , ganinshi kadai yana kwantar da hankalinta, badan tsufan shi ba da babu abinda zai hana a kirashi da jabeer dinta.... Mrs tijjani shattima..... [15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 4⃣9⃣ By Aysha Ya'u Kurah Karfe 9 na safe aka sallameta suka ďunguma zuwa gida a motar alhj basheer, oyizah na zaune a parlonta tana gyara farce hankalinta sam ba'a kwance yake ba dan tun jiya take jiran jin mummunan labari game da Afeeyah amma shuru gashi har gari waye, Shigowar motar alhj basheer ne yasa ta mike ta kwashe kayan gyaran kumban dan taje ta tarboshi ko zataji wani labari a gurinshi, tana buďe kofar parlon tayi tozali da mai taurin kashi wato Afeeyah, kallon mamaki ta tsaya yi mata a zuciyarta tace to ko karya hajja take mata yarinyar nan bata ci abincin ba, Afeeyah ta katse mata zancen zucin da takeyi tace ina kwana, oyizah ta sauke ajiyar zuciya tace lafiya lau ta juya ciki bata ko bi takan hajja dake rike da kaya ba, Side dinsu ta wuce tana kallon hanya ko zata ga Affan, da bismillah ta murďa kofar dakin suka shiga ita da hajja, bayi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61