Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 1

Chapter 1

Rabo Ajali Book 1 Complete Hausa Novel 1,197 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

[◆ RABO AJALI ◆◆ 1⃣ By Aysha Ya'u Kurah بسم الله الرحمن الرحيم الحمد لله رب العالمين والصلاة والسلام على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه وسلم. ..... Affan... Affan... Affan.. sau uku saurayin dake tsaye a kanshi ya kira sunanshi amma ko waiwayowa baiyi ba bare ya amsa,, hankalinshi na kan ruwan dake malale cikin wani katon ramin kiwon kifin dake cikin gidansu yana kallon yadda suke wuntsil wuntsil ciki yana girgiza kanshi da jikinshi hakoranshi waje yana dariya da karfi, duk wanda ya ganshi yasan hankali sam bai isheshi ba, dafashi saurayin yayi hade da zama gefenshi ya watsa ma kifin abincinsu nan take suka kara hautsinewa suna yawo cikin ruwan gwanin ban sha'awa, ihuu Affan yasa yana kaďa kanshi yana kokarin kai hannunshi cikin ramin kuma yana nokesu alamar tsoro, saurayin yayi murmushi ya kara watsa abincin,,, affan ya cikwikwiyeshi cikin murna yana fadin yeeehhh Jabeer kara zuba musu yunwa suke ji dama, jabeer ya shafa fuskarshi cikin tausayin halin da amininshi yake ciki yace affan lokacin sallah yayi muje muyi sallah mu dawo sai in cigaba da basu abincin, affan ya no'ke wuyanshi kamar karamin yaro yace um um ba yanzu zanyi sallah ba mummy tace ko da yaushe nayi sallah dai2 ne saboda ni ba a rubuta min zunubi, Jabeer da idonshi ya fara canza kala dan ya riga ya saba da jin hakan a bakin affan kullum in yayi mishi maganar sallah, cikin dabara yace waya fada maka ba a rubuta maka zunubi Affan, to bari kaji kasan wutar nan da ake kunnawa mai zafin nan? Affan cikin firgici yace eh na santa wanda ake dafa min indomie mai zafi ko, jabeer yace of course ita ay kasan tafi indomie zafi ma ko, affan ya gyada kanshi, jabeer yace to wutar da Allah ke kona waďanda basa sallah tafi wannan zafi sau "dubu malala gashin tinkiya" affan ya mike a firgice idonshi zuru2 yace tafi wutar dake dafa ruwan toilet heater ma wanda yake kona ni in zanyi wanka, jabeer yace sosai ma ay wannan ruwan kamar ruwan sanyi ne akan wutar Allah, affan ya fara ja baya yace karya kakeyi sai naje na tambayi mummy, jabeer ya mike da sauri dan yasan yana zuwa ya tambayi mummy to fa bazata taba bari yayi sallah ba, da sauri ya rike hannunshi yace affan ni ke karya, ya fizge hannunshi yace eh mana kaine kake karya ya juya ya ruga cikin gida da gudu jabeer na kiranshi yayi banza dashi, dafe kai jabeer yayi cikin damuwa sai da yafi minti 5 tsaye sannan ya wuce ya tafi masallaci,,,, Jabeer ďinne ya fada maka haka, affan ya gyada kanshi yana daďa kwanciya jikinta alamun tsoro yakeji kar wuta ta kona shi, mummy tace rabu dashi makaryaci ne na fada maka ka daina kulashi kullum burinshi ya tirsasa maka yin abinda da bakayi niyya ba kuma ko a musulunce babu takura a addini, rabu dashi kaji affan din daddy tashi kaje kaci abinci kayi wasanka kaji, ya daga kanshi ya mike yana tsalle har ya karasa gurin cin abinci yana kiran sunan Hansa'u mai aikinsu tazo ta zuba mishi abinci, murmushi mummy tayi hade da ajiyar zuciya, Salma babar diyarta ta ajiye laptop dinta tace mummy wannan tsinannan jabir din so kawai yake ya ruguza miki plan dinki, kullum shi kenan maganar sallah sai kace wani sallau, mummy tayi dariyar mugunta ta kalli gurin da affan ke cin abinci duk yayi kaca2 da gurin amma ko digo bai diga a rigarshi ba saboda tsananin tsaftarshi, tace barni dashi ummu, jabeer yana wuce gona da iri tabbas zan san duk yadda zanyi in rabasu da affan in ba haka ba wata rana zai sa kwaba ta tayi ruwa, Fareedah tace wallhy I so much hate him sai ya dinga wani ďadďaga kai kamar kadangare shi a dole ga kyakykyawa mtsww taja tsaki, mummy tace ku barni dashi dani yake magana in yasan wata ay bai san wata ba..... Mrs tijjani shattima...... [15/12 09:32] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 2⃣ By Aysha Ya'u Kurah Da gudu ta shigo gida ta tarar da jarababbiyar kishiyar uwarta a tsakar gida tana fiffita, sannu da gida kawai tace bata jira amsa ba ta wuce ďakin kakarta Hajja Giďe, fadawa dakin tayi babu ko sallama ta cire skul Bag ďinta tayi wurgi da ita a kan gado sam bata kula da mutum a kan gadon ba ta fita da sauri ta shiga toilet, Hajja ta idar da sallah tayi tsaki tace wannan yarinya saidai Allah ya shirya yi hakuri jabeer, ya mike zaune yana murmushi yace zata sani ay bari ta dawo, hajja tace ay kai baka iya yi mata faďa sai dai kullum kace zata sani kullum kai ke kara sangarta ta, kafin yayi magana ta shigo ta ďane kan cinyar hajja tace hajjanah" sannu da gida, hajja ta tureta tace dalla ni sauka karki karya ni, sai a sannan idonta yakai kan jabeer dake kallonta baya ko kiftawa, da sauri ta mike tana murmushin jindadi ta zauna kusa dashi kamar zata shige jikinshi tace dama kana cikin dakin nan, ta shagwabe fuska tace shine kana kallon hajja tana tureni ko kayi mata magana kalli fa hannu na saura kaďan taji min ciwo, Hajja tace Allah ya kiyaye dai banji miki ciwon ba ko, ta turo baki tace kinso kiji min mana inaga ma dan kinsan yaya jabeer na nan ne shiyasa baki ji min ciwon ba, hajja ta kwashe da dariya tace to yau dai sharrin kaďan ne ko Allah nagode maka ma yana cikin dakin da yana zuwa nasan ce mishi zakiyi yau da kyar na barki da rai, jabeer ya kwashe da dariya, ta kwabe baki ta fashe da kukan shagwabe harda buga kai a gado, jabeer yace subhallahi me kuma akayi miki, hajja ta mike tace tabarar fa, ni bari kaga in fita dan in ina dakin nan zane yarinya zanyi, cikin kuka tace kaji ko wallhy bulala takemin kullum yauma dan ta ganka ne, jabeer ya haďe rai yace gaskiya hajja zamu kai kararki can kotun karshe a yanke miki hukunci, hajja tayi dariya tace mu fara shariar daga yau ma in dai akan AFEEYAH ne, afiyah ta dago kai ta harareta, jabeer yayi murmushi ya ciro hndky dinshi yana share mata hawaye, yace so sorry babynah, ya dago fuskarta ya kalli cikin idonta yace baki san kin girma da kuka ba, ta kara marairaicewa kamar karamar yarinya tace to baka ganin abinda takemin, yace to nace kiyi hakuri kinji, ki daina yarda suna saki kuka kinaso a dinga ce miki ruwa2, ta noke wuyanta tace ah'ah, yace to sai kin zama mai hakuri kin daina yawan kuka kinji, tace tam zan daina, yace yauwa wifey nah,, ya dakko ledar gefenshi ya fito dasu biscuits da chocolates, rungumeshi tayi cikin murna ta mishi peck a kumatu tace I love u so much hubbynah, wani abu yaji yana mishi yawo cikin kwanyarshi, a hankali cikin rashin kuzari yace more than u do babynah,, ta sakeshi tana dariya, nan suka cigaba da hirah cikin jindadi tana shan chocolates, sai da aka kira la'asar sannan ya fito zai tafi, rakoshi ta fito yi bayan yayi sallama da hajja,

Table of Contents

Chapters

61 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});