Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 49

Chapter 49

Rabo Ajali Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

nata da alhj yasa a fitar dasu daga cikin gidan, duuffffffff taji saukar mutane akanta suna maida numfashi, da sauri ta hankade farida da Afeeyah ta kalli su tanimu tace lafiya kuka shigo min parlour, a ruďe farida tace mummy kifayen nan sun bace a cikin kwanon da aka sasu....... Mrs tijjani shattima..... [15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5⃣5⃣ By Aysha Ya'u Kurah Zaro ido oyizah tayi tace kamar yaya sun bace, Afeeyah ta kalli alhj basheer da ya fito yana gyara hula tayi saurin cewa wallahi bacewa sukayi mummy, haba shiyasa suke tsorata ni cikin dare ashe ba kifaye bane, alhj basheer ya karaso da sauri yace kifayen ne suka bace, oyizah ta galla ma su Tanimu harara sum sum suka fice ta juyo ta kalli alhj basheer tace iskancin su ne ni nace ma wanda ya kwashe kifin ya dauka na bashi shine dan basu gansu ba suke tunanin sun bace, to ina zasu, Fareeeda tace wallhy tall--- oyizah tayi saurin katseta tace dalla rufe mana baki, shekarun su nawa a gidannan kin taba ganin sun bace, dallah ku wuce ku ba mutane guri, Afeeyah ta ja hannun Affan da jikinshi ke kyarma suka wuce daki a zuciyarta tace 99days 4 the thief muje zuwa, Allah dai ya kara bani sa'a... Tun karfe hudu na yamma oyizah ke gurin chummy cikin matsananciyar damuwa tana faďa mata anyi destroying fishpond dinta na tsafi, dariya chummy tayi sannan ta buga kasa nan take ya tsage ruwa haďe da kifaye suka fara fitowa daga ciki, saida suka gama fitowa tsaff sannan suka haďe kansu guri ďaya, oyizah tayi murmushin jin dadi tace ashe suna nan, har hankali na ya kwanta, bacewarsu ba karamin daga hankali na yayi ba dan ba karamin taimako na sukeyi ba, chummy tayi dariya mai karfi tace fitarsu a gidanki tonan asirinki ne saboda haka kisan duk yadda zakiyi ki mayar dasu gidan nan Affan ya dinga ganinsu kullum, oyizah tayi tagumi tace ta yaya zan mayar dasu bayan alhj da kanshi yace a fitar dasu, yanzu ina komawa dasu zai fara zargin wani abu, chummy tace karki damu, akwai abun da zan baki kisa mishi a abinci daga yaci shikenan ko yagansu hankalinshi bazai kawo su bane, oyizah tayi dariyar jin daďi tana faďin thank u my lord,, mikewa oyizah tayi ta shigo da wani yaron da zasu sha jininshi a gurin meeting, da ganin yaron kasan mugun takadiri ne dan ko gezau baiyi ba idonshi a soye babu alamar hawaye, dakyar ya tsuguna a gabansu, chummy ta harareshi sannan ta umurceshi da ya miko mata kafafuwanshi, tirjewa yayi yaki mikowa, babu yadda batayi ba akan ya miko kafafuwanshi tayi wani aikin dasu yaron nan yaki, kwala kiran BULADUNA tayi nan suka shigo shida abokin aikinshi, cikin isa ta umurcesu da su kamo yaron su kawoshi gabanta, da karfinsu suka fara kokarin kama shi yana tirje musu yana tokarinsu da hannu, sai sun daukeshi sunyi sama dashi sai yasa iya karfinshi ya zille ya fado kasa, daukar da sukayi mishi na karshe ne yasashi wani irin kukan kura ya hankaďe buladuna yayi baya, tartsasssssss sukaji dukansu suka duba gurin da sauri, glass din da fanne da fanna ke ciki ne yayi tarwatse ya bullo tun daga bayan buladuna har cikinshi, nan take ya fadi kasa matacce, da sauri su chummy suka yo kanshi suna kiran sunanshi, su kuwa su fanne cikin azama suka fito cikin glass suka nufi gurin yaron da aka kamo da niyyar taimaka mishi ya gudu, cikin tausayawa yace ku meyasa bazaku zo mu tafi tare ba, fanne cikin sauri tace mu matattune gawar mu ta dade a rami kai kuwa ba'a riga an birne gangar jikinka ba kayi saurin komawa gida, da sauri yace waye ya kawo ku nan, fanna tace mahaifin mu ne Alhj sambo ministern Abuja na yanzu, kafin yaron yayi magana ya hango su chummy sun doso su suna kokarin kama su fanne, da sauri kurwar yaron tabi ta inda su fanne suka nuna mai ya bace daga gurin, cikin kunan rai chummy ta ciro sandar tsafinta ta fara nuna su fanne dashi, zagayen dakin suka farayi har suka kai inda kwalbar gunkin zeenatu take, da sauri fanne tasa hannu ta dauki kwalbar, wani irin ihu oyizah tasa tace karki fasa, karki fasa, zan taimakeku in maida ku gidan ku, fanna tace fanne fasa da sauri saboda mu dama a mace muke gurin wa zata maida mu, kafin chummy ta cimma fanne har ta fasa wannan kwalbar ta karya gunkin ciki, zama oyizah tayi a gurin tana girgiza kanta tana fadin shikenan, shikenan my lord, sai da nace miki mu gama da yaran nan saboda nasan zasu iya zame mana matsala, yanzu nasan duk inda zeenatu take ta farfado, chummy bata ba oyizah amsa ba saida ta tabbatar ta kwantar da fanne da fanna sannan tace yau dinnan zan gama dasu, ki kwantar da hankakinki dan sun fasa kwalbar a banza dan babu wanda yake tunata bare har yayi mata adduar da zaisa ta gama dawowa hayyacinta,, yanzun nan zan kara yin aikin da yafi wancan akanta, oyizah ta saki ajiyar zuciya tace nagode my lord.. Afeeyah na zaune tana lazumi, tunda ta idar da sallar la'asar bata tashi daga kan daddumar ba sai gurin biyar, shafa addu'ar tayi ta mike ta nade daddumar sannan ta zauna a kasa a gefen gadonta ta tura hannunta karkashin gadon ta zaro zanin da ta kunshe damon nan a ciki, a hankali ta warwareshi ta nade hannunta da leda cikin dakewar zuciya ta fara kakkabe kasar tana kokarin bude bakin damon, cikin sa'a ta budeshi sai wari yakeyi ta karkatar da bakin ta girgizah shi, nan wata katuwar laya ta faďo kasa, da sauri ta ajiye wannan damon ta naďeshi cikin zanin ta dauki layar ta warwareta, babu abinda ta gane a cikin rubutun sai sunan zeenatu, nade layar tayi ta mike ta fita da wannan damon ta kulleshi a leda takai main bolar gidan sannan ta dawo ta kona layar ta tattara tokar ta zubata a magudanar ruwa... ★ Magaryah Nijar★ Indo!!! tankaďen ne har yanzu baki gama ba, baki gudun malam ya dawo ya tarar ba'a gama abinci ba, wane irin shashanci ne wannan, nda tashi ki ban guri sai shegen Nawar tsiya, indo ta turo baki ta mike tayi hanyar waje, Sallamar da akayi ne ya tsayar da ita, da sauri ta rungumeta tana faďin "Tanti Gaje" sannu da zuwa, Gaje tayi dariya tace sakan ni yar Magaryah ya na same ku, indo tace kalau muke sai dai har lau Tanti Ayyu na nan da masifarta, Gaje tayi dariya ta karasa cikin gidan tanti ayyu ta mike tace maraba da gaje mutan jigawa, gaje tace ina wuni Ayyu, ayyu ta amsa tana shimfiďa mata tabarma tace ya jigawar, ay tun shekaran jiya muke zuba ido shuru, Gaje tayi murmushi tace mun yi sabga ne a kazaure dan haka baki ganni ba, ya kokari ya kuma mai jikin an samu cigaba kuwa--- kafin Ayyu tayi magana wani razananen ihu ya fito daga ďakin majinyaciyar ya ziyarci kunnuwansu, kallon kallo suka fara yi sannan suka mike da gudu suka shiga dakin har suna bige juna, zama

Table of Contents

Chapters

61 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});