Chapter 38
Chapter 38
dai inaso insan ko kayi wankan tsarki, yace eh nayi wanka sosai jikina yanata kumfa, yanata kumfa, yanata kumfa na koma fari sosai, tayi dariya tace to sallah fa, nan ya kirne fuska yace ai ni bana sallah, Afeeyah ta kwalalo ido waje tace la haulu, baka sallah, saboda me,? Kafin yayi magana sukaji muryar oyizah a bayansu tana cewa saboda ubanki bai koya mishi ba..... Mrs tijjani shattima... [15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 4⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah Afeeyah ta sunkuyar da kanta da sauri kirjinta na dukan uku2, Affan ya kalli oyizah yace mummy dama saboda babanta bai koyamin ba shiyasa bana yi, oyizah ta mika mishi cup din hannunta tace amshi maganinka kasha rabu da wannan kinibabbiyar, Affan ya karbi ruwan asirin da ya saba sha kullum ya fara sha ya miko ma Afeeyah yace kema zaki sha, Afeeyah ta girgiza kanta ta mike zata wuce oyizah ta janyo hijabinta tace dawo nan ban gama dake ba, ta kalli Affan tace tashi ka kai cup din kitchen sai kaje kayi wasanka, Affan ya mike yana yafito Afeeyah da hannu yana cewa zo muje ki tayani buga game, oyizah tace a'a jeka kayi wasanka zata zo ta sameka, ya wuce da gudu yana dago ma Afeeyah hannu, Wani irin kallo oyizah tayi ma Afeeyah sannan tace jiya me nace miki game da Affan,, Afeeyah ta sunkuyar da kanta kasa tace dan Allah kiyi hakuri, oyizah taja kunnenta da karfi tace hakurin uban me kike bani, bance miki kar ki shishshige ma Affan ba? bance miki karki shiga rayuwarshi ba, ohhh wato kema zaki fara tursasashi akan sallah kamar yadda ďan iskan saurayinki yayi ko? Afeeyah ta runtse idonta zuciyarta na zafi saboda kiran jabeer dan iska da oyizah tayi, Rankwashi mai karfi ta sakar mata akai tace zan miki kashedin karshe, kashedin da idan kika ďauka kin tseratar da kanki daga fushi na, anyi na farko anyi na karshe tsakaninki da Affan, kin fahimci abinda nake nufi ko sai na warware miki? , Afeeyah tayi shuru kirjinta na tsananta bugawa, oyizah tace to ina nufin kwana ďaki daya ke da shi, anyi ta yanke ta gille tsakaninku, wallhy kinji na rantse duk ranar da kika kara yarda Affan ya shigo dakinki har kika barshi ya kwana, hmmm faďin hukuncin da zan miki ma bata baki ne kina jina ko? Afeeyah ta gyaďa kanta tace eh inaji, oyizah ta saki hijab dinta ta kara kai mata duka a kai tace bace min a gaba ko in illata ki, da sauri Afeeyah ta wuce daki tana kuka****** Bayan hajja ta gama rarrashinta ta zuba mata abinci ta karba ta fara turawa da sauri saboda azabar yunwar da takeji, cikin tausayawa hajja ta fara bata baki cikin hikima da kalamai masu taushi, sai da ta tabbatar da hankalinta ya kwanta sannan ta tashi tafi gida cike da tausayin yar jikarta da ta fara dandana rayuwar duniya, dan da sam Afeeyah bata san bacin rai ba kullum cikin farin ciki take in ka ganta tana kuka to na shagwaba ne, babu wanda zai taka ta ta barshi bare har ya daura mata bacin rai duk wanda yayi mata take zata mayar mishi ta wuce hankalinta kwance.. Haka rayuwar Afeeyah ta kasance cikin kunci da bauta, wulakanci kala2 babu wanda bata gani, sam bata bari Affan ya ganta ko yazo yana bubbuga kofarta bata budewa, ba karamin tausayi yake bata ba in ya fara buga kofar dan baya bugun hankali yana bugata yana ihu wani lokacin ma harda kukanshi, abinci kuwa saidai hajja ta kawo mata dan bata nasu, duk wannan wainar da ake toyawa alhj basheer bai sani ba saboda baya gari, A ranar da ta cika sati uku a gidan tana tsaye tana mopping dining room, oyizah da suwaiba suna zaune cikin parlon suna gulmarta, suwaiba tace lallai yarinyar nan ashe duk iskancin da take mana guri ta samu, ji yadda take muku bauta kuma duk zagin da kuke mata ta kasa tabuka komai, oyizah tayi dariya tace ay wargi ma guri ya samu, ni yaushe kamar wannan yarinyar zata tsaya min a gaba, ai wallhi kema suwaiba harda laifinki, suwaiba tace ai da dinma daurin gindi ta samu to yanzu mai shagwabatan ya mutu shiyasa shegen bakinta ya mutu, oyizah tace ai ko shugaban kasa ne ya tsaya mata bata isa ta min ba bare wannan tsinannan yaron mai shegen girman kan tsiya.. Afeeyah ta yar da mop din hannunta ta runtse idonta zuciyarta na tafarfasa, muryar salma taji a bayanta cikin isa da gadara tace kee.. je kiyi min pepper soup mai yaji sosai yanzu nan ki kawo min, Afeeyah bata juyo ta kalleta ba ta tsalleke ruwan da take mopping dashi ta kama hanyar side dinta, da sauri salma ta bita tana huci taja rigarta ta baya har saida wuyan ya yage tace ke dan uban--- Afeeyah ta juyo cikin azama ta dauketa da gigitaccen marin da ya hanata karasawa yasata sakin Afeeyah bata shirya ba.... Mrs tijjani shattima..... [15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 4⃣4⃣ By Aysha Ya'u Kurah A firgice oyizah da suwaiba suka yo kan salma dake rike da kunci idonta yayi jajur, fuskarta oyizah ta ďago tana shafawa ta kalli Afeeyah murya a sarke tace m-ari, suwaibah ta jinjina kai a munafurce tace tabdijam, lallai yarinyar da tsaurin ido kike, ki kalli girman salma ki dauketa da irin wannan marin, Afeeyah taja tsaki ta juya zata wuce oyizah ta saki salma ta janyota da karfi tana huci, ihun da Afeeyah ta saki yayi daidai da shigowar alhj basheer parlon, da sauri ya karaso yace subhanallahi lafiya safiya, me tayi miki, oyizah ta saki Afeeyah da sauri ta juyo ta fara hawaye tace alhj ace kamar yarinyar nan ta dubi salma ta tsinka mata mari, Afeeyah ta durkushe ta fashe da kuka tace dan Allah daddy ka kaini gurin hajja, wallhy kasheni zasuyi, dukana sukeyi kullum, yanzu ma dukana suka gama yi har suka yaga min riga, dan Allah ka kaini gurin hajja, kafin alhj basheer yayi magana mahmud dan suwaiba ya shigo rike da kular abinci a hannunshi, ta gefen ido Afeeyah ta hangoshi cikin muryar kuka tace mamu kai min daki ka dauko kular jiya, alhj basheer cikin mamaki yace meye a cikin kular nan, Afeeyah tace abincin rana na ne, alhj basheer cikin tashin hankali yace duk abincin dake gidan nan sai an kawo miki abinci daga gida, oyizah da ta gama tsurewa tace umm al--- Afeeyah ta katseta da sauri tace sunce abincin gidan nan ba na talakawa bane wai ban saba cin irin shi ba saboda haka kar in taba musu, oyizah ta sankare cikin mamakin sharrin da Afeeyah ta lafto musu, alhj basheer ya juya ya kalleta cikin tuhuma tayi saurin cewa wallhy karya take min alhj, ya za'ayi in hanata abinci, alhj basheer ya kalli mahmud yace kai tun yaushe kake kawo ma Afeeyah abinci, mahmud yace kullum nake kawo mata da safe da rana da daddare, alhj basheer ya saki salati yace kin kasheni safiya, kin tozarta ni a unguwar nan, yanzu kowa ya gama sanin sirikata daga gidansu ake kawo mata abinci, oyizah tace wallhy alhj kar---rufe
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61