Chapter 45
Chapter 45
da sauri ta diro daga gado tana mamakin baccin da ya dauketa har ya hanata zuwa shan jinin matsiyaciyar yarinyar nan, karar shigowar kira wayarta ne yasata saurin dagawa tace morning esther, jiya bacci ya hanani zuwa meeting, esther tace haba ay ni tunda naga ban ganki nasan kina can kina shegen baccinki, amma oyeee meyasa kikayi haka, meyasa kika bada jinin yari---- oyizah tayi saurin katseta tana dariya tace badai an gama komai kuma kun riga kun koshi da jinin ba, to ay shikenan, esther cikin damuwa tace oyizah me tayi miki haka da zafi har kikayi sacrificn dinta 4 no reason, oyizah tace meye ma bata min ba yarinyar nan, kedai zamuyi magana bari inje mu fara shirye shiryen jana'izah, esther tace to sai munyi waya, oyizah ta kashe wayar ta shiga bayi ta wanke fuskarta cikin farin cikin ta yar da kwallon mangwaro ta huta da kuda, a zuciyarta tace yanzu ne zan kara daure alhj da Affan ta yadda su da dukiyarsu zata dawo karkashin iko na gaba ďaya, bazan kara yarda a auro ma affan mace ba bare ma har ta zame min damuwa, Tana fitowa ta wuce parlor inda alhj basheer ke kallon news, saida ta gaisheshi sannan tace bari inje in dubo lafiyar Su Affan sai in kawo maka break ko, yayi murmushin jin dadi yace ya kamata kam saboda mai larurar ciki, ta shafi fuskarshi tana dariya tace su alhj ana ji da wannan jikan, yace sosai ma, Allah dai ya fito min da ita ko shi lafiya, oyizah ta kaurara dariyarta tace ya Hajjjj kenan sannan ta wuce side din su Affan.. Da izzarta ta buďe kofar tana murmushi, bata samu kowa a parlon ba dan haka ta tura kanta bedroom ďin, zaro ido tayi cikin firgici saboda ganin Affan kishingiďe da towel a jikinshi Afeeyah na zaune da night gown a gefenshi tana mishi gyaran fuska suna kallon juna suna murmushi, A-f-e-e-yah oyizah ta faďi bakinta na rawa, Afeeyah ta mike tana gyara gashin kanta tace naaaam ina kwana mummy, oyizah bata iya amsawa ba sai ma fita da tayi dasauri kamar zararriya, tana gab da shiga dakin alhj basheer dan daukar wayarta ta kira esther taji ihun farida a ďakinta, da sauri ta juyo ta karaso ďakin dan ganin abin da take ma ihuu..... Mrs tijjani shattima..... [15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5⃣1⃣ By Aysha Ya'u Kurah Cikin ruďewa ta isa gaban gadon tana fadin ke lafiya, ihun me kikeyi, Fareedah ta kasa magana sai nuna salma takeyi da hannu tana kuka sosai, a firgice oyizah ta fara girgiza salma tana kiran sunanta, wani irin ihu ta saki haďe da zama a kasa tana faďin wayyyo salma, da gudu alhj basheer ya shigo ďakin yana faďin me ya faru, oyixah cikin ihu tace salma, salma--- yace salma me, tace salma ta mutu alhj, karasawa gaban gadon yayi kirjinshi na bugawa da karfi ya ďagota yana dubata, sakinta yayi da ya tabbatar bata rai ya shiga fadin innalillahi wa inna ilaihir rajiun, oyizah ta mike kamar zararriya tace alhj ka tasheta wallhy karka bari ta mutu, wayyyo na shiga uku na lalace, alhj basheer ya daka mata tsawa yace wani irin hauka ne wannan, waye ya isa da dawo da matacce, oyizah ta kara rusa ihu tana faďin wallhy sai ta dawo salma bazata mutu yanxu ba, tsaki alhj basheer yaja ya tashi ya fita daga ďakin hankali tashe, ihun suka cigaba dayi ita da farida suna kuka suna jijjiga salma suna faďin ta tashi, Ihun da sukeyi ne ya janyo hankalin Afeeyah dake zaune suna karyawa ita da Affan, da sauri ta mike tace ya karasa bari ta duba taga ihun me akeyi, tana fita tayi hanyar dakin mummy dan nan takejin ihun, sankarewa tayi da ta shigo dakin ta hango salma kwance inda ta shimfida wannan farin kyallen, innalillahi kawai take maimaitawa a zuciyarta, sam ta kasa karasawa gurin saboda tsoro, a zuciyarta tace yanzu da ni ce zan mutu, meyasa matar nan takeso ta kashe ni, wani irin kuka ta fashe dashi ta ruga dakinta da gudu a zuciyarta tana dana sanin sa farin kyallen a gurin, da tasan na mutuwa ne da ta daukeshi ta konashi bata shimfiďa wani ya hau ya mutu ba, kuka sosai takeyi tana fadin shikenan nayi kisan kai, da sauri Affan ya matso kusa da ita yana tambayarta abinda ya faru, bata bashi amsa ba ta shige can cikin daki ta dauki wayarta ta kira kaka liman, ringing biyu wayar tayi ya dauka, cikin muryar kuka ta gaisheshi ya amsa yace lafiya me ya faru, ta kara fashewa da kuka tace kaka nayi kisan kai, wallhy bansan abun mutuwa bane, na dauka wani tsafin tayi dan ta nakasa mu ashe na mutuwa ne, kaka liman yace nutsu ki fada min komai yadda yake dan bana fahimtar abin da kike fadi, nan ta tsagaita kukanta ta faďa mishi duk abinda ya faru, kaka liman yayi ajiyar zuciya yace kwantar da hankalinki Allah baya kama mutum da laifin da bai sani ba, lallai Allah na tare dake Afeeyah shiyasa har ya nuna miki wannan mummnan alamarin ya kuma baki basirar ki mayar mata da kaidinta, wannan aya ce Allah ya saukar gareta in har tana da hankali, har gurin Allah baki da laifi dan ba ke kika kasheta ba uwarta ce ta kasheta, ki dage ki cigaba da addu'a saboda yanzu ne zata kara karfin tsafinta in har tasan kaikayi ne ya koma kan mashekiya, Afeeyah ta share hawayenta tace to nagode kaka dan Allah ka cigaba da yi min addu'a dan wallhy abubuwan tsoro suke bani, kaka liman yace babu komai jikata addu'a kullum munayi saidai akara bude wuta, Allah ya dauraki bisa kanta, Afeeyah tace ameen sannan ta kashe wayar ta fita ta wuce gurin gawar salma.... Kafin karfe 10 angama shirya salma cikin suturarta za'a kaita gidanta na gaskiya, har lokacin oyizah bata bar ihu ba sai sambatu takeyi tana fadin wallhy babu inda za'a kai mata ya, babu wanda ya isa yaje ya binne mata 'ya a rami, sosai ta fita hayyacinta tun kukan na fitowa har ya daina fitowa, dakyar aka fita da gawar salma daga gidan, sai da oyizah ta suma sai uku saboda tashin hankali, tana farfadowa ta shiga tsine ma mutanen gurin tana fadin ita fa yarta bata mutu ba dan ko ciwon kai batayi ba, Da mutane suka ga abin nata jahilci ne sai suka watse suka barta da kukan takaici, Bayan azahar esther ta kara kiran oyizah, cikin kuka oyizah ta ďauka tana faďin esther salma ta mutu, batayi ciwon komai ba, ko mura ba tayi ba lafiya lau muka rabu jiya da daddare,, esther tayi dariya tace kin iya acting oyizah halan kina cikin taron mutane ne, oyizah cikin ihu tace wane irin acting ina fada miki yau da safe mun tashi ba salma shine har kike dariya, esther tace to ay abin naki ne, ki bada yarinya da hannunki sannan kizo kina kuka, oyizah ta zaro ido tace wace yarinya, esther tace salma mana, salma kika kawo jiya, kinsan kuwa saboda hakan da kikayi har mukami aka kara miki saboda kin kawo yarki wacce kika fi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61