Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 40

Chapter 40

Rabo Ajali Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Afeeyah ta kauce tace toh fah!!, ashe dai rashin aure ba masifa kadai yasa ku harda harkar dabanci, fisabillihi ku ko kunya bakwa ji, ni bansan meyasa kuke bakin ciki dani ba dan nayi aure at dis age of mine, dan Allah ku barmu muci soyayyarmu ni da mijina zan muku addua' kuma Allah ya kawo mashinshini nan bada dadewa ba dan rik'ar da kukayi a gida ta isa haka, abun ma ni har tausayi yake bani, babu wanda ya iya cewa komai sai kallon mamaki da suka bita dashi, cikin karfin hali salma tace ina mijin yake anan da zamuyi bakin ciki, ke nan har wani miji ne, wannan tababben da baisan kanshi ba ma bare mace, Afeeyah tayi saurin cewa tabdijam,, ke kike ganin tababbe, ta rungumoshi tace ni nan namiji nake gani wanda a cikin maza ma sai an tona kafin asamu irinshi, dan Allah ku fitar mana a ďaki dan naga alamar baku san wannan lokacin na hutawar ma'aurata bane, fareedah ta harzuka matuka ta ajiye maganin hannunta tayi kan Afeeyah zata duketa oyizah tayi saurin dakatar da ita da hannu, tace barta fareedah wallhy sai tasan ta faďa muku wadannan maganganun, kuzo mu tafi, Afeeya tace to sai da safenku Allah ya aurar daku ku huta da kunci, amma fa mummy baki nuna min yadda zan bashi maganin ba, oyizah kamar ta rusa ihu tasa kai ta fita ba tare da ta bata amsa ba, Afeeyah ta bisu da li'ilah fi quraish ta datso kofar ta dawo ta kalli Affan da ya gama tsurewa tace matsoraci to sai ka zauna tunda dodonka ta tafi, Affan ya zauna murya a sarke yace mummy tayi fushi dani ko, Afeeyah tace batayi fushi ba bari in kawo maka abinci kaci sai kasha magungunanka kayi bacci kaji, Affan ya gyaďa kanshi, Da kanta ta bashi abinci yana gama ci yasha ruwa da drink ta dauko magungunan da oyizah ta kawo, saida ta karance su tsaf ta kalli wani ruwan jarka shi ba ja ba shi ba maroon ba, daga kafadarta tayi tace may be na gargajiya ne, na asibitin ta fara bashi duk wanda ta kai bakinshi sai tace yayi bismillah sannan zata zuba mishi, tana bude na jarkar taji wani karni karni, da kyar ta tsiyayya a cup tace wa'iyazubillah wannan irin karni haka, ta mika mishi tace kayi bismillah, yana yin bismillah ya kai bakinshi yaji hannunshi na rawa sosai, da kyar da taimakon Afeeyah ya shanye maganin, boye magungunan tayi ta gyara gurin ta dawo ta zauna tana mishi hirah yana kyakyata dariyah harda buga kai a pillow, sun shagala sosai cikin farin ciki Afeeyah taji ana buga musu kofa, mikewa tayi tana mita a zuciyarta, tana budewa taga oyizah tsaye kamar gunki, Afeeyah taja baya tace kin dawo ne mummy, Oyizah ta kalleta tace tambayar da ya kamata kiyi min kenan ni da gidan mijina, Afeeyah tayi dariya tace to ai wannan tambayr tafi da inyi miki shuru in kyaleki, kuma nima nan turakar mijina ce, oyiza tace wallhy zan babbalaki a gidan nan in bawa karnuka kasusuwanki su cinye, Afeeyah tace waii ay ko da sunci kashi da wahala dan wallhy kashi na taurin tsiya gareshi, oyizah tayi shuru dan taga abinda ke neman fin karfinta tace kin bashi magungunan, Afeeyah tace wannan dole ne tunda inason mijina ya samu sauki, oyizah tace akwai wani a jarka ki tabbatar yasha dama dan in jaddada miki ne yasa na dawo, Afeeya tace karki damu in ma akwai wani ki karo bazan gajiya ba, oyizah tayi tsaki ta wuce ranta a bace, ta riga ta gama kudirawa a ranta a daren nan zata lalata rayuwar yarinyar nan, wallhy yau sai tasan ta tabo ni, dan bazan barta ba abinda ta dinga fadi kenan,,,,, To oyizah sarkin sa'a muna miki fatan nasara akan Afeeyah... ... Mrs tijjani shattima.... [PM, 05/04/2016] Ummu Nan: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 4⃣6⃣ By Aysha Ya'u Kurah Tun sha biyun dare Afeeyah ke jin wasu irin sautittika masu ban tsoro ta windon ta, kallon Affan tayi yana baccinshi hankali kwance, cikin dabara ta cire hannunshi a jikinta ta gyara mishi kwanciya ta mike a tsorace saboda sautin karuwa yakeyi, cikin karfin hali da dakewar zuciya ta ďaga labulen windon dakin, sakin labulen tayi da sauri taja baya tana maimaita "HASBUNALLAHU WA 'NI'IMAL WAKIL" saboda ganin wasu halittu masu ban tsoro kewaye da windon,,, wani kara taji an saki nan take taji ďakin da suke ciki yana girgiza ta ko'ina, runtse idonta tayi tana karanto adduo'in neman tsari, da dai taga kamar kara girgiza ďakin akeyi sai tayi karfin halin buďe kofarsu cikin sauri tayi hanyar da zata sadata da ďakin oyizah, Tana zuwa kofar dakin ta kama murfin xata bude taji sautin magana da karfi wanda ya sata sakin kofar bata shirya ba, sunanta taji sosai ana kira a ďakin ta kuma ji wannan sautin na windon su ya dawo nan inda take tsaye, a gigice ta leka ta windo don jin mai ambaton sunanta cikin wannan sigar a kuma wannan talatainin daren, tana lekawa ta hango oyizah cikin jajayen kaya tsugune gaban "chummy," sai wani bakin basamude a tsaye a gafensu rike da wani bakin kare, Afeeyah bata kara firgita ba sai da taga oyizah ta dauki kwaryar jini ta shanye tass sannan ta kara daukan wani ungulu tana kiran sunanta dashi, fitsari ta saki nan take saboda ganin duhu ta ko'ina bata iya hangen gabanta, lalube ta fara yi tana addu'a da karfi tana kiran sunan hajja dan ta tsorata matuka da abin da idonta ya gane mata, ga wannan girgizar har lokacin bata bar jinta ba, a cikin laluben taji hannunta ya taba mutum, nan take ta tsandara ihu haďe da faduwa kasa sumammiya, A gigice alhj basheer da ya fito dan ganin abinda ya samu wutar gidan ya haskata da torch light, cikin kidima ya fara kiran sunanta yana fadin innalillahi wa inna ilaihir rajiun, safiya, safiya, oyizah ta tsorata matuka da jin muryar alhj basheer dan tasan yayi bacci, cikin azama ta tattara kayan tsafinta ta cire na jikinta ta mayar da night gown din jikinta ta fito tana mutsika ido, alhj basheer yace safiya zo ki kama min yarinyar nan mu kaita asibiti ko numfashi bata iya yi na rasa me ya fito da ita cikin daren nan, oyizah ta matso da sauri tace wace yarinya, alhj basheer yace Afeeyah ce, kamata da sauri dan Allah, oyizah cikin murna ta kama Afeeyah dan a tunaninta tsafinta ne ya kamata, suna fitowa wutar gidan ta kawo alhj basheer ya bude motar suka tura Afeeyah ciki, oyizah ta koma ta dauko hijab dinta suka wuce asibiti, Tunda aka kaita asibiti a wannan daren likitoci ke iya kokarinsu suga ta farfaďo amma abin yaci tura, oyizah cike da murna ta nemi guri ta zauna a zuciyarta tace yarinya ai tunda kika shiga gona ta sai kinyi noma wallhy, alhj basheer kuwa hankalinshi ba karamin tashi yayi ba dan baisan meye ya sami yar mutane ba, safa da marwa kadai yakeyi a cikin asibitin, dakyar doctor musah ya lallabashi akan in shaa Allahu zuwa gobe zata farfado in kuma bata farfado ba sai musan abin yi, alhj basheer akanta ya kwana

Table of Contents

Chapters

61 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});