Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 22

Chapter 22

Rabo Ajali Book 1 Complete Hausa Novel 1,207 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Afee dakyar suzo gurin Affan, in Affan ya ganta to fa aranar murnarshi ta karu kenan saboda ya dinga mata shirme kenan yana kwaso kayayyaki yana bata wai ta tafi dasu gida, a cikin yan kwanakin suka dan fara sabawa kadan2, dakyar jabeer ya fahimtar dashi cewa an kusa daura mishi aure da Afeeya, dariya kawai yayi yace to in kukayi aure zaka barmin ita anan gidan, jabeer yace sosai ma ai anan zata zauna, Affan yayi dariya ya kalli afeeyah yace wai haka, ta gyaďa mishi kai tace eh, wani irin ihu yasa ya mike wai zaije ya fadama mummy, da sauri Afeeyah ta riko hannunshi ya tsaya chakk yana jin wani irin abu a rikon da tayi mishi, juyowa yayi kamar me hankali ya kalleta itama shi take kallo haka jabeer kallonsu kawai yakeyi, jikinta ne ya bata jabeer na kallonta tayi saurin sakin hannun Affan tace karka faďa ma mummy zatace kar abaka ni ko yaya jabeer, jabeer ya gyada kanshi yana kallon Affan, zama Affan yayi yana murza hannun da Afeeyah ta rike yace to babu abinda zatamin in ta sani, Afeeya ta gyada mishi kai tace baza ma tasani ba, jabeer yayi mamakin yadda affan yaji maganar afeeya, mutumin da magana in dai akan mummy ne to babu wanda ya isa ya tsayar dashi, kallonsu ya cigaba dayi yadda yake mata hira tana biye mishi suna kyakyata dariya sai yaji daďi a ranshi dan ko ba komai zai yi amfani da Afeeyah ta dinga dawo dashi hanya, sam baiji kishin komai a ranshi ba dan yasan Affan baida hankali kuma ko yanada hankali ma bazaiyi kishi ba saboda yasan irin son da afeeyah take mishi.. Safiyyar monday jabeer ya shirya da wuri saboda zai kai Afeeyah makaranta ranar zasu fara jarabawa, a kofar gidansu ya sameta tsaye tayi kyau sosai tana jiranshi, kusa da ita ya kai motar ta bude ta shiga suka gaisa, yace da fatan kinyi karatu ko, tace sosai ma banyi bacci sosai ba, yace kedai fadi gaskiya kodai kin boyo xpo, ta turo baki tace kaima kasan wuce nan duk da bana zuwa 1st kasan dai ban taba wuce 10th ba, yayi dariya yace 3rd term ss2 dakyar na roka fa aka barki a 10th din shine zaki wani cika min baki a faďa da dambe ne dai ake baki A1, ta harareshi tace eh naji ďin, yayi dariya ya tada motar suka wuce yana cigaba da tsokarta, kan titin "hausawa" ya hango motar gidansu Affan, bai bi takanta ba bare yasan su waye a ciki, ya wuce ya sauke Afeeyah a skool haďe da yi mata adduoin samun nasara.. Yana fitowa daga layin skull dinsu ya kuma hango motar, wannan karan Affan ya hango a gaba da baloon a hannunshi yana dariya mummy ta hakimce a baya, bin motar yayi dan yanason yaga Affan kafin ya tafi aiki, asibitin da ake mishi check up suka tsaya, saida suka shiga ciki Jabeer yayi parking, saida ya gaisa da wani abokinshi da suka dade basu haďu ba sannan ya shiga, sam oyizah bata ganeshi ba saboda hankalinta a tashe yake da result din check up din, jabeer yaji doctor na cewa gaskiya an gode Allah dan zai iya dawowa normal cikin kwanakin nan saboda mun samu improvement sosai, ya mika mata magani yace wannan maganin shine maganinshi na karshe in shaa Allah in ya kare komai zai zama normal, jabeer saboda murna zaiyi magana ya bugi wata nurse kayanta suka zube ya durkusa ya kwashe mata yana bata hakuri, yana ďagowa yaga har sun fita sun shiga mota, binsu yayi a baya har gida, a waje yayi parking motarshi saida ya tsaya a waje ya kirah office ya dau excuse sannan ya shiga ciki da sauri, babu kowa a parlon gidan hakan yasashi hawa sama saboda tsananin murna, tsayawa yayi jikin wata kofar da yakejin magana da karfi haďe da huci kamar zakanya, lekawa ya fara yi ta gurin mukulli, ya hango Affan zaune kan wani jan kyalle, da sauri ya dago kanshi jikinshi na rawa ya ďeka ta window, oyizah ya hango da wata halitta suna magana suna zagaye Affan, suna gamawa yaga an bawa oyiza wani ruwa ance ta bawa affan muddin yasha to bashi ba samun sauki kuma haukarshi zata fi ta da, oyizah tayi dariyar jindadi tayi sujjada ga wannan halittar nan da nan yaga ta bace,, jabeer sai mutsike idonshi yakeyi a tsorace kamar a mafarki, muryar oyizah ce ta dawo dashi hayyacinshi waya takeyi da esther tana faďa mata duk yadda tayi ta mayar da Affan haka har abin da tayi ma zeenatu, a kidime jabeer ya fara fadin innalillahi wa inna ilaihir rajiun, jin tayi shuru ne yasa ya leka da sauri ya hangota ta mike zata bawa Affan wannan ruwan, cikin zafin nama ya murda kofar ya kabe ruwan ya zube a kasa, oyizah ta kalleshi a firgice tace j-a-b-e-e-r, ya dago Affan ya rikeshi yana mata wani mugun kallo yace asirinki ya tonu, muguwa azzaluma, matsafiya mai shan jinin alumma, naga duk abinda kikeyi yau in shaa Allahu karshenki yazo, yaja hannun Affan zasu fita oyiza tace jabeer ka dawo, ka rufa ma kanka asiri dan wallhy babu wanda ya isa yaga karshena, ka dawo ka fadi nawa zan biyaka ka rufa min asiri, jabeer bai saurareta ba ya fita dan a tsorace sosai yake, suna zuwa gate Affan ya fisge hannunshi yasa ihu yana faďin mummy kizo ga su lion nan zasu kamani, ihu yakeyi yana ja baya ya ruga ciki da gudu, jabeer ya kalli gate din cikin mamaki dan shi baiga komai ba, har zai koma ciki sai kuma ya fasa ya fita a fusace, Police station ya nufa yana zuwa kofar gurin ya fara tunanin to ina evidence yake, Affan shi kadai ne evidence kuma bashi da hankalin da za"a saurareshi, shuru ya zauna a motar yana tunanin mafita, can ya fara tunanin yadda zaiyi affan ya samu sauki, a zuciyarshi yace malamai zan tara suyi ta mishi addu'a ita kuma oyizah zan mata lamfa in nuna mata kamar bazan fadama kowa ba har sai nasan yadda nayi har Allah ya bawa Affan lafiya,... Mrs tijjani shattima... [15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 2⃣7⃣ By Aysha Ya'u Kurah Juya kan motarshi yayi ya nufi gurin wani babban malami dake zaune a Tarauni, saida ya jira malamin ya gama da almajirai sannan ya shiga suka fara zantawa, Bayan malamin ya gama jin bayanin jabeer sai ya jinjina kai yace tabbas imani yayi karanci a wannan zamanin, na dade banji rashin imanin da har yakai wannan ba, ya kalli jabeer yace in shaa Allahu zamu hadu mu fadawa Allah nan da kwana uku zuwa hudu komai zai dai2ta kai dai ka dauke kafarka daga gidan ka barta cikin tunanin baka fadama kowa dinba sannan kayi taka tsan tsan da ita, jabeer yace to malam nagode sosai ya ajiye musu kudin sadaka sannan ya mike ya fita, Gurin malamai uku yaje a ranar duk yayi musu bayani suma sun dauki alkawarin yi mishi addua ba dare ba rana,, ranar jabeer ya yini cikin bakin ciki babu yadda ummi da Afeeya da hajja basuyi ya faďa musu abinda ke

Table of Contents

Chapters

61 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});