Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 57

Chapter 57

Rabo Ajali Book 1 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

murmushi a kullum ba,, nasan bazamu sake haďuwa mu rungume juna mu faďa ma juna damuwarmu ba, bansan me yasa mutuwa ta zabi jabeer ta barni, bansani ba Afeeyah, ya karasa fadi yana kuka kamar karamin yaro,, kuka suka dinga yi babu mai rarrashin wani a cikinsu, saida sukayi mai isarsu sannan Affan ya ďago ya kalleta murya a dashe yace nagode, nagode da abin da kikayi min, kau da kanta tayi tace ka gode ma Allah da kaka liman, ya juyo da fuskarta yana kallon rinannun idanuwanta yace kullum cikin gode musu nake, godiyarki ta daban ce Afeeyah, babu wanda zai dauki kasadar da kika ďauka a duniyar mu ta yanzu, kinyi mana abin da ko dan uwa na jini bazai iya yi mana shi ba, bamu da wata kalmar da zamuyi amfani da ita gurin gode miki, Afeeyah tace karka gode min na cika kudirin jabeer ne, wannan shine burinshi na karshe, saboda wannan kudirin aka kashe min shi,,, Affan yace nasan komai Afeeyah kuma in shaa Allahu wacce ta kasheshi ba anan duniya ba ma har a lahirah bazata taba samun kwanciyar hankali ba, Afeeyah tace tun a duniya nakeson Allah ya wulakanta min ita, wallhi da nasan ita ce silar mutuwarshi na rantse da bazan kyaleta ba da nayi mata abun da zata gwammaci mutuwa da rayuwa, Affan ya share mata hawaye yace ki kwantar da hankalinki nasan yanzu duk inda take a cikin bala'i take, Afeeyah ta girgiza kanta tace da hannuna nakeson in kasheta kuma yau dinnan, Affan yace hmm nima naso hakan tun ranar da na dawo cikin hayyacina, nan ya bata labarin komai harda dawowar umma da bacewar oyizah,,,,, cikin mamaki Afeeyah tace zatayi abinda yafi haka muguwa azzaluma, Allah ya isa tsakanina da ita, in shaa Allahu sai tayi mutuwar kask---Affan ya katseta da sauri yace wannan adduar bata kamace ki ba, Allah yasan yadda zai tafiyar da irinsu ki zuba ido ki jira lokaci, Afeeyah tayi shuru tana kallonshi kamar ba shi bane tababben bawan da baya taba maganar da zaka iya fahimta a da, Allah mai iko...... Mrs tijjani shattima.... [15/12 09:38] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 6⃣4⃣ By Aysha Ya'u Kurah Daren ranar suna zaune gurin meeting bayan sun dawo daga gurin dodon tsafinsu, gaba dayansu suna sanye da jajayen kayansu da suke amfani dashi, bayan sun gama tsaface tsafacensu sai chummy ta mike taje ta shigo da ďan tsoho, a tsakiya suka sashi kamar yadda suka saba, kewayeshi ta farayi tana yan sirkullenta a kanshi sannan ta zauna, ďaya bayan ďaya tsohon yake bin mutanen gurin da kallo, yana zuwa kan oyizah ya tsayar da idonshi kyarr a kanta baya ko kiftawa, kureshi itama tayi da ido cikin rashin tsoro ta daka mishi tsawa tace daina kallona, idon wannan tsohon ko rawa baya yi ya fara motsa bakinshi da babu hakori ko ďaya a ciki, oyizah ta kalli chummy tace my lord plss mu gama da tsohon nan mu cigaba da abinda ke gaban mu, chummy bata kalli oyizah ba ta cigaba da haďe haďenta na tsafi cikin wani katon koko, mikewa tayi ta iso gaban tsohon ta ja hannunshi da karfi har yana bigewa ta jona mishi wani abu mai tsini kamar kibiya a jijiyar hannunshi tana kallon cikin kokon, a firgice ta juyo tana kallonshi ta kuma maida idonta cikin kokon dan gasgata abin da ta gani a ciki, da sauri ta saki karfen taja baya saboda yadda ya dauki zafi kamar tana rike da garwashi, wata irin dariya tsohon nan ya saki yace jinin nawa ya isheki haka, in kina bukatar kari kizo ki diba san ranki dan ko zaki dibi cikin tanki bazai kare ba, su oyizah duk suka marmatso suka leka cikin kokon, a gigice suka ja baya saboda ganin wani bakin ruwa mai kaurin gaske a ciki, oyizah murya na rawa tace my lord kiyi wani abu plss wannan kamar ba mutum bane, cikin su esther da alhj sambo ya ďuri ruwa suka ce kwarai wannan ba mutum bane, cikin dakewa chummy tace ko ma waye shi tunda yazo nan bazai taba fita ba, ta dauko wata sanda mai mugun kyalli ta nufi wannan tsohon dashi, tana karasowa gaban shi ta ďaga wannan sandar ta saita cikin idonshi ta turata ciki, ga mamakinta sai ganin sandar tayi ta rabe gida biyu, daya a cikin idonshi ďaya a hannunta, sa hannunshi yayi ya zaro sandar yana dariya ya mika mata yace haďata guri ďaya, a harzuke ta yar da sandar hannunta ta koma ta shirya kanta sosai tace yau ko waye tsohon nan sai na gama dashi, ta bayanshi ta bullo ta sa farcen hannunta ta shako wuyanshi ta baya, da azama ya juyo ya sanya nashi faratan a makogoranta, wani irin kakari ta farayi tasa kafarta ta haureshi yayi baya, nan suka fara b'ace b'ace suna faďa sosai, ba karamin wahala chummy take sha ba amma saboda tsabar ta dahu da tsafi kuma bata so mabiyanta suga gazawarta haka ta jajirce suka cigaba, wani lungu ta shiga a cikin ďakin ta fito rike da wani magani ta bace tana kokarin watsa ma wannan tsohon, sam bata san yana kallonta ba ta ďaga wannan maganin zata zirara mishi yayi saurin juyar da hannunta ya zuba wannan ruwan a tsakiyar kanta, wani irin ihu ta saki ta faďi kasa tana ta shure shure nan take kanta ya fara zagwanyewa, tun tana ihu mai karfi har ta koma yi a hankali gaba ďaya mummunar halittarta ta canza kama,, a gigice su oyizah suka fara ja baya hankalinsu a tashe babu wanda a cikinsu yayi kokarin zuwa gurin wacce suke kira mai taimakonsu, itama yau gashi ta kasa taimakon kanta, mikewa wannan tsohon yayi yana kallon su oyizah, mai da hankalinshi yayi gurin alhj sambo yace alhj sambo Bana, minister mai fuska biyu, a fili fuskar kamala a zuci ta zalunci, ina son kayi ma kanka hisabi ka zabi hukunci cikin jerin abinda zan lissafo, na farko ko in kasheka anan in kaika gida da kayan jikinka, ko kuma in barka ka koma gida ka fito media ka faďi ko me kakeyi sannan ka fadi adadin mutanen da ka bayar akasha jininsu, alhj sambo cikin rudewa yace kayi min rai dan Allah, dan tsoho yace Allah shi ke da rai bani ba, alhj sambo yace ka rufamin asiri wallhy na tuba, har abada bazan kara aikata irin wannan aikin ba, dan tsoho yayi dariya yace zunubin da kayi baya kuma fa, kayi kisan kai, shirka, da sauransu duk dan ka samu mulki, haka nake so kaje gidan talabijin ka sanar musu da halinka, alhj sambo ya girgiza kanshi yace mutunci na zai zube, dan tsoho yace ai gara ya zube a duniya, alhj sambo yace dan Allah ka kasheni anan kawai gara suga gawata, dan tsoho ya girgiza kanshi yace a'a bazan yi kisa ba gara a hukunta ka kafin kaje ka tarar da na ubangiji, kuka sosai alhj sambo yakeyi yana mishi magiya akan ya kasheshi ya huta amma tsoho yayi kememe yaki, alhj sambo da yaga babu sarki sai Allah sai ya amince da abinda tsoho yace mishi ya kimtsa ya bace yayi gida hankalinshi a tashe, kallon sauran yan

Table of Contents

Chapters

61 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});