Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 18

Chapter 18

Rabo Ajali Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

alhj, Affan ya samu "brain disorder" abin da yabamu mamakin anan shine duk girman ciwo da karfin buguwar nan bashi ya taba kwakwalwar shi ba har yasamu "mental illness" sai wani abun daban,,,, ya mika mishi wata takarda yace wadannan sune ciwukan da kwakwalwar shi ta samu "Psychological trauma": wannan cutar may be triggered by P.T suffered as a child, kamar "severe emotional", physical, or sexual abuse;" abinda ke kawoshi kuma shine, "a significant early loss", kamar the loss of a parent; and neglect... sai kuma "Environmental stressors": "itama ana samunta ne a shock din mutuwa ko macen da aka saka, ko kuma dysfunctional family life, sacking 4rm jobs or schools, and substance abuse -- it can trigger a disorder in a person who may be at risk for developing a mental illness." Kaga kenan akwai abinda ya gani ko kuma ya sameshi cikin waďannan abubuwan amma sam ciwon kanshi bai da alaka da cutar, Alhj basheer cikin tashin hankali yace yanzu doctor kana ganin Affan zai samu lafiya nan kusa,? doctr musah cikin tausayawa yace sauki na gurin Allah alhj, in yazo yanzu baiyi gaggawa ba sannan in baizo yanzu ba baiyi jinkiri ba saboda Allah ne kadai yake iya bada sauki a lokacin da yaso, sannan ina tsoron sanar dakai mostly mental illnesses irin wannan are caused by a combination of factors and cannot be prevented so easily, saidai a dage da addu'a saboda babu abin da ya gagari Allah kuma babu wanda yasan gaibu sai Shi.., da sauri oyizah da tun shigewar su office din doctor ta iso ta juya cikin jin dadin ciwon da taji ya sami Affan da kuma firgicin jin affan nada rai kuma zai iya samun sauki a koda yaushe, kuma tasan yanzu alhj na dawowa zai fara tambayarta ina zeenatu? Kuma me ya samu Affan me ya gani har ya haddasa mishi wannan cutar, fita tayi daga asibitin da sauri cikin tsananin tsoron abinda zai je yazo, bata zame ko ina ba sai gurin tsafinsu..... Mrs tijjani shattima..... [15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 2⃣2⃣ By Aysha Ya'u kurah Alhj basheer ya fito daga office din doctor Musah idonshi jajur saboda kukan da yaci, dakin da aka kwantar da Affan ya shiga ya zauna gefenshi yana zubar da hawaye yana ta tunanin yadda akayi har Affan ya faďo daga wannan saman nisan gaske, to wai ma me Affan ya gani da har ya firgita shi haka, da sauri ya mike da ya tuno da tun asuba baisa zeenatu a idonshi ba, kuma ace har Affan baida lafiya batazo inda yake ba, girgiza kanshi yayi a fili ko dai wani abu ne ya samu zeenatu, gabanshi ya faďi sosai da ya tuno da kalaman doctor, jikinshi ya fara rawa ya murda kofar dakin da affan yake ya fita da sauri yana fadin innalillahi a zuciyarshi, da taimakon Allah ya isa gida, a waje yayi parking motar saboda tashin hankali, yana shiga ya wuce dakinta, babu inda bai duba ba a ďakin bai ganta ba, cikin kiďima ya fito yana haďa sunayen mutanen gidan yana kirah da karfi, da gudu suka firfito, oyizah da bata fi minti 5 da dawowa daga gurin tsafinsu ba ta matso kusa dashi tace lafiya alhj, ya nuna dakin zeenatu yace ina zeenatu take, fareeda da salma suka ce daddy tun jiya bamu ganta ba, oyizah tace ni rabona da zeenatu ma ay tun ranar da zaka tafi mukayi maka rakiya, cikin karaji yace to ina ta shiga, oyizah ta dafashi tace calm down my dear muje ka huta ka kira can gida kaji ko tana can, cikin damuwa ya kalli fuskar oyizah, nan ya tsinci kanshi da kasa yi mata musu ya bi bayanta suka wuce gurin dinning, saida ta bashi abincin da ta haďasu da sinadaran asiri sannan ta zauna gefenshi tana matsa mishi kafa, kallonta yayi har lokacin fuskarshi dauke da damuwa yace safiya ya akayi Affan ya faďo daga wannan saman mai nisa, sannan me ya faru a gidannan da har ya haddasa tabuwar kwakwalwarshi, oyizah ta fara share hawayen karya tace alhj nima ban sani ba, kowa na bangarenshi ya za'ayi insan abinda ya faru, Allah sarki Affan yanzu brain dinshi ya samu matsala, murya a dashe alhj basheer yace eh safiya, kuma bawai fadowar da yayi bane ya taba brain dinshi, hankali tashe kamar gaske tace to me ya sameshi, nan ya kwashe abinda doctor ya faďa mishi ya fada mata, wani irin kuka ta fashe dashi harda zama a dirshan a kasa tana faďin mun shiga uku, yanzu shikenan Affan ya haukace, alhj basheer ya shiga rarrashinta yana faďin addu'a zamuyi mishi safiya, dakyar oyizah tayi shuru tace ni alhj babban tashin hankalina shine rashin ganin zeenatu, Allah yasa ba wasu mugayen bane suka saceta suka wurgo Affan daga sama, hankalin alhj basheer ya tashi da jin furucin oyiza, ya kalleta yace da zeenatu tayi musu me zasu saceta, oyizah tace Alhj ka manta muna cikin zamanin da ba sai kayi ma wani komai ba zai maka mugun illah, nidai gobe kabi jirgin safe kabar kulawar Affan a gurina kaje can cameroon ka dubata dan wannan abun yafi karfin waya, alhj basheer ya share zufar goshinshi yace kin kawo shawara mai kyau safiya, amma--- ta katseshi da sauri tace na fada maka zan kula da Affan fiye da yadda zaka kula dashi, kai dai ka tafi nemanta dan hakkinta na wuyanka, cikin jindadin tsararrun kalaman oyizah alhj basheer yace nagode sosai safiya, Allah ya kaimu goben, tace ameen yanzu kaje ka kwanta ni zan tafi gurin Affan din in ta kama ma sai in kwana, alhj basheer yaji dadi sosai a ranshi ya dinga shi mata albarka.. Ďaki oyiza ta wuce zuciyarta wasai yanzu gida zai dawo karkashin ikonta, wani kulli mai kyalli ta kwance ta fito da babyn "Mutum mutumi" an soke kanshi da mashi, Kallon babyn tayi hade da kwashewa da dariya tace Affan kai da warkewa har abada, haka zaka dawwama cikin hauka har ka mutu kamar yadda babyn nan take haka zaka kasance sai yadda nayi dakai, ta mike ta daga karkashin gadonta inda ta dade da haka wani ramin sihiri ta kara tona gefen ramin ta kira sunan Affan sau uku sannan ta tura babyn ciki tana dariyar mugunta, ta kalli wata laya ta kara saka wata dariyar tace wannan naki ne zeenatu, ba yanzu zanyi aikin ba sai an gaji da nemanki, ta mayar da layar cikin daurinta sannan ta loda magunguna hade da turarukan tsafi a jakarta ta shirya wucewa asibitin.. Tun asuba jabeer ke neman wayar Affan ba'a dauka ba, daga karshe ma jin wayar yayi akashe, gurin karfe 8 yaso shiga ya dubashi sai wani muhimmin aiki ya taso mishi a office ya wuce, bai dawo gida ba sai bayan magriba, saida ya fara shiga gurin Afeeyah suka dan taba hirah sama2 sukaci abinci tare kamar yadda suka saba sannan ya mike jikinshi a sanyaye saboda rashin jin muryar amininshi yau tru out, abinda bai taba faruwa ba tun tasowarsu dan ko tafiya daya yayi to suna manne a waya, sallama yayi ma hajja da afeeyah ya fita ya isa kofar gidan su Affan, tun a gate mai gadi

Table of Contents

Chapters

61 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});