Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 9

Chapter 9

Gidan Gandu Book 1 Complete Hausa Novel 1,271 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

sukayi suna kallonta, "Hello,burgu mai kake cewa waim" "Had'uwa da BUBA JINI kuma ?" "Shikenan zamuji da Wacce yazo saidai ka kaishi zuwa gobe dan yanzu akwai abinda nake shirin yi ne" Saida ta ajiye wayar ta kallesu kafin suka kula da yanda ta basu umarni cikin kankanin lokaci kuma suka bi batare da sun sani ba(sameemah kenan). ❤❤SADY-SAKHNACEH❤❤ Kar ku manta da #comment #share #like #follow. ____***GIDAN GANDU***____ ❤❤By sadi-sakhana❤❤ Wattpad username:SAKHNA03 ❤07❤ Tashi sameemah tayi kaman mai kiwuyar tashi a wajen kafin ta nufi kofar da alhaji babban yake. Yana kwance anyi masa shimfidi a tsakar dakin saidai idonsa yana kallon mai wucewa,kallon sameemah yake da son gano wacece, "Wannan din wacece?" "Sameemah ceh " "Ohj sameematuh ceh,toh yah labarin mahaifiyar taki kuwa an ji labarin itah y'ar inace ?" "Mahaifiyata kuma ,ita kam ai tah rasu" "Yaushe amma banida labari. Koh?" "Ina nasan maka ni zaka tambaya,ya jikinnaka?" "Lah jiki da sauki yar nan kinsan tsufah ne " "Eh AI naga alama kam" Tafada tana kare masa kallo daga inda take zaune, "Toh nizan tafi allah yasa kurigamu gidan gaskiya,ina haka ake cewa?" "Ni zaki tambaya,toh kigaida ummartaki idan an ganta" "Kai ni karka dameni da wani zancen na gaisheta,inaga ma kaine kake kallonta saboda ka kusa jona sahunsu,haka kawai zaka wani dameni da cewa in gaida wanda yah mutu,kai idan kaje kace ina gaisheta " "Lallai yar nan allah yayi ja'irah" "Ashe da sauran hankalinka kasan mai kake,to sai anjima allah yah sawwake" Daga haka ta kade skirt dinta tabar wajen tana buga feduwa,tai hanyar waje,bayan tah gyara gyalen wuyannata(dan itah yanda maza suke ficewa daga gida sanda suka so fita haka take ficewarta sai sanda ta dawo). Washagari da safe da wuri tabar gida saboda shirye shiryen haduwa da buba jini,dan kaff garin ba kungiyar dabar da ta kai tasa wajen kwarewa da kuma bud'adden ido. Lokacin da suka isah ainihin inda sansanin yan dabarsa take saida burgu yayi Mamakin irin tsarin da akayiwa wajen kaman na yan boko haram. A harabar cikin wajen suka samu anyi shimfid'a da kayan marmari duk na tarar seemah jar wuyah da yaranta. Tun daga nesa kuwa buuba jini yah hangosu itahce a gaba suna biye da itah ,har Mamakin irin biyayyar da yaranta suke mata yake,saboda ko shi daya tara manyan yan daba,basa masa biyyayah yanda yaran seemah suke mata biyyayah. Tana zuwa saida ta zauna a tsakiyar daddumar suna kallon juna ita da buba jini kafin sauran yaran ta,wato su burgu suka zauna a bayanta. Murmushi yayi tareda dage girar hagun irinna yan iskannan kafin yace, "Barkanki da zuwa" Itama irin yanda yayi mata tayi kafin tace, "Na amsa gayyatarka ,saika fadamin meyake dauke a bakinka da har ka nemi yin magana dani,kuma har cikin gidanka?" "Ba komai bane ,inaso ne kawai ki had'e da kungiyata muzama d'ayah" "Meyasa ka bukaci hakan" "Saboda keh macece,nasan ba iyah dan kungiyah yan siyasa suke nemanki ba,harda wani kudurinsu na daban,kinga idan muka hade ,karfin izzarki da kuma tsaro zai karu,nikuma kinga saiki kawo mana hankalin yan siyasah su bamu aiki,nasan bazaki ki amincewa ba" "Idan kuma naki amincewar fah mezakayi?" Kallon idonta yayi yanda take maida martani kaman ba a gabansa take ba ,babu alamar tsoro a idonta, "Tunda kika shigo gidannan dole ki amince da bukata ta " "Idan naki fah mai zai faru" "Toh bazaki bar gidannan da kafarki b............" Tin kafin yah karisa maganar,seemah ta yanka jijiyar hannunsa daya rike wukar dayake mata barazana da itah cikin kiftawar ido. Kururuwa yah fara yana danne wajen da jini yake tah fitah, "Kai din dama ba babban shege bane ,ya za'ayi wanda yake kiran kansa da suna jini kuma yayi ihu dan jini yah fito daga jikinsa?" Yan dabar sa ne suka iyo kanta da sauri,sai kuma yah dakatar dasu ,cikin dauriyah da cije baki yace "Karku yi mata komai,kuyi hanzarin shiryah motah yanzu mu tafi asibiti,banason kowa yayi mata hukunci,ni nan da kaina zan hukuntata,sai tayi dana sanin abinda tah aikata" "Kai dakata da surutun haka,duk naji su,bana bukatar neman ayimin maimaici,saidai kai din kayi hanzari,domin in bakayi sauriba jininka zai kare a nan wajen,kaga sai muga wa zai baka ransa kazo daukar fansar dashi" Mikewa yayi idonsa yayi jawur dan azaba,fadawa mota yayi tareda watsawa sameemah wani mugun kallo,na alamar zamu had'u. Ita kuwa gogar ko a jikinta saima murmushi da tayi masa tareda daga masa hannu tana yimasa bye bye. Duk abinnan da ake,su burgu mutuwar zaune sukayi lokacin da suka ga abinda sameemah ta aikata,dan sun saddakar yau kam kwanansu yah kare a wajen buba jini,dan duk fadin garin babu wanda bai sanshi wajen yanka ba da kuma aika aika,kowa tsoronsa yake babba da yaro. Saida ta shuri burgu kafin yayi ajiyar zuciya yace , "Ma'am shugaba,sun yanka mu ne" Zefah masa makullin mashin tayi kawai batare da tace komai bah. Bayan sun hau mashi dinne suna tafiyah burgu yace, "Amma shugaba bakya ganin yanzu muna cikin matsala" "Dallah ni yi shiru ka rufemin baki ,bakuda aiki sai tsoron tsiyah,ni narasa meyasa ma nake tare daku har yanzu" "Yi hakuri bazan kuma bah" "Kudin hannuna yayi low,kaini gidan badariyyah,zan karbi bashina da tazo har gida ta karbawa mijinta a wajena,yau zanga mai hanani fitowa da kudina a cikin gidannan,in tareda uwar wani ake samosu" "Gaskiya kam shugaba kiyimasu rashin mutunci ba shin fah ya kusa wata guda a wajensu,babu ma yah wannan mijinnata kullum yana wajen caca" "Toh ina ruwanka,kai waye zaka zagi mijin yar uwata,ko cewa nayi ka tayani,kudinka ne koh nawa?" "Kiyi hakuri shugaba an iso gidan " Sauka tayi daga kan mashin din kafin tacewa burgu, "Jirani na Shiga na fito,dan ko bayanan saita fadamin inda yake" Langa langan kofar gidan tah buga da karfi,saida awakin gidan suka dungura suna d'aure,badariyyah ce ta fito da sauri,suna had'a ido da sameemah ta buda wani uban salati da a'uziyyah tana dafeh kirji. "Eh zaki kori shedan mana tunda kinga nice,na rantse ko dujal zaki kora saikin fitomin da kudina,koh kuma ki fadamim inda lalataccen mijinnaki yake naje na karba" "Haba sameemah babu koh Sallama,kuma ai saiki shigo mu gaisa koh?" "Ba gaisuwa ceh ta kawoni ba,kudina nazo karba,saiki bari sanda nazo zumuncin saiki ce ga wajen zama,ki fitomin da kudina yanzu ,dan babu d'aga kafa yau,koh inna karime zaki sayar bai dameniba,ni kudina nasani,tunda ba da wani shege aka hadu aka tarasu ba" "Kiyi hakuri sameemah,wlh ko kudin cefane nima bai baniba,kuma ai ni yar uwarkice" "Hmmm ke kikasan wannan yaren,fad'amim inda yake yanzunnan,ko kuma na tattare y'an awakincan nayi kasuwar dabbobi dasu yanzunnan" Tafad'a tana nuna awakin Badariyyahn, "Ahah kiyi hakuri,indai baban iliyah neh,wallahi yana rumfar kofar gidan Ashiru mai shayi" "Dama nasan ai duk munafurcine,ba sonsa kike na,indai akan kudinkine" Juyawa tayi ta fice daga gidan bayan tayi boll da langar data gani a tsakar gidan miyar kuka ta bushe a ciki, "K'azamai kawai,ai dole kuyi ta gudawa" Bayan ta fitane Badariyyah ta sauke ajiyar zuciyah tareda cewa, "Na rabu da masifar yau kam,saikuma wata ta gaba" Ashiru mai shayine ya k'ara gyara zamansa zance yayi dad'i yace, "Hmm AI baka saniba BALA,shi sha'anin kudi a bishi a hankali kawai" Audu ne (baban iliyah mijin Badariyyah),wanda shine mai raba cacar yana

Table of Contents

Chapters

55 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});