Chapter 4
Chapter 4
kafin yafara garwaya shinkafar dan dama da yunwa yadawo gidan ,kuma yayi arba da tsautsayin daya faru,dawowa tayi ta samu waje ta zauna tana gyara zaman dan kwalinta, "Ah dama nace baban su ATIKA,(haka take cemasa),kaman dakai aka tafi da hanifa asibiti koh?" "Eh dani ne ya akayi?" "Meyafaru ne acandin?" "Shiyasa kika tareni da fara'a harda ruwan sanyi da kawo abinci a kwano mai murfi dan kiji labarin abinda yafaru koh?" "Haba baban atika ya zaka ce haka kuma naga dan ka fadamin ba laifi bane koh" "A gunki kenan ba,toh bazan fada ba,waiku mai yake damunku ne bakuda aiki sai kowa buri yake yaga wani abu yasamu dan uwansa yadora agaba koh,haka kuke daga ku har y'ay'anku kamar an garwaya an raba" "Kaga baban atika nifah ba cewa nayi kafara min wani zance na banza da wofi ba,kawai tunda bazaka fada ba shikenan,dadinta ma da su sule kaje,zan tambayesu su fadamin,kuma dama dazu na kara kudi an dad'o maggi na ashirin saika bani kudina na fasa yafewa" Kade zaninta tayi tana cika kaamar kububuwa ta bar wajen,dan tsabar takaici daya shak'i baba umaru jijjiga kai kawai yayi yana rufe kwanon abincin,dan ji yayi duk abincin ma ya fita a ransa. (Allah ya shirya matan mu a yanzu,musamman ma kauye koh babban gida wannan matsalar tafi yawa a irin wannan muhallen). A kofar su larai kuwa kowa yah watse yakama harkar sa sai matan dasuke karkashin inna karima su kadaine a kofar ana maida abinda yafaru ana yada shewa,Hansai ceh matar dan baba umaru na farko manjo wanda yatafi cirani bayan ya saci kudin sarkin noman anguwar tasu ana nemansa,wanda yanzu y'ay'anta biyar kenan,duk suna gidan suma ana fama dasu. "Hmm ke kiji sai mukaji abu yafaru kuma?" Itama wata a gefensu ce ta cafe tareda cewa, "Naga dama ita ke likawa labirun,yanzu gashinan ai yayi mata aika aika,maganinta" Wata a can gefece tana bawa danta nono ta kalli MAIRO wanda ita ta gama magsna yanzu, "Ke mairo yanzu kece mai cewa wani wai allah yakara dan anyiwa Y'arsa fyade?,ai gwara ita dole akayimata naga ke yar ki HAFSA,amai muka ga tanayi akaje aka dawo kuwa ashe cikine da ita,kuka shirya ke da ita da asuba kikaje aka zubar mata ,harda cewa wai shawara ce take damunta" Kunya ce ta ishi wanda aka kira da mairon wanda tafara masifa cikin borin kunya itama ta fara maidawa wanda tayi maganar da nata laifin, "Naji dai ina Y'a tace kawai tayi,kuma hakan bazata sake faruwa ba,amma ba'a kama uwata da makocinsu ba a daki ina" "Ke dan kutumar ubanki mairo mutsaya iyah kan gidannan banda sako gidan kowa,dan wallhi inta hakane kowa bazai ji dadi ba in toza'afara'za'afara" "Hehe dama in baki yasan mai zaice bai san mai za'a mayar masaba,kan me uwa da wabi duk uban abinda za'a fada a fada ba tsoro nakeba,abin kunyane kowa gaba yabashi anan wajen ba baya ba,dan babu wanda abin kunya bai lullubeshi ba anan wajen,dan haka kawai ayi sha'ani wai na birni ya cuci na kauye". Ganin abin zai bacine yasa inna karima korar kowa daga dakinnata ,kowa yayi hanyar kofarsa yana maida nasa zancen. A wajen su sameemah kuwa lokacin da suka dawo daga gidan alhaji Sama'ila har sunyi hanyar gidan kungiyar tasu,ta bada umarnin a nufi hanyar gidan karagiya inda aka kai labiru dazu da safe,mashin din suka k'uza suna sakin hayaki a duk layin dasuka wuce kafin suka yanka cikin gari inda zai kaisu inda yake. A zaune suka sameshi yana rarraba ido fuskarsa ta kumbura suntum saboda dukan dayasha,mamakine kwance akan fuskarsa daya ga sameemah a wajen, "Yayah labiru kayi Mamakin ganina ne,nice dai y'ar kanwar taka" "Amma mai kike a wajennan,ko dagskene da ake cewa kece shugabar yan dabar garinnan?" "Kwarai kuwa gashi ka tabbatar da kanka,kafin mukai ga nan,ajiye wannan wasan a gefe muyi abinda yatara mu,miyasa ka aikata abinda nake zarginka dashi" "Makike zargina dashi iyee,kaika jimin yarinyar nan" Murtuke fuska sameemah tayi kaman ba itace take dariya yanzu ba,wani irin wawan mari ta sauke masa akan fuskar sa saida dungura jini yana fita ta hancinsa,komawa yayi ya gyara zamansa da Mamakin irin naushin daya fito daga hannun nata kamar wani babban majiyin karfine ya dakeshi, "Yanzu zaka bani amsa koh kuwa,mai ka aikatawa karamar yarinya dazu da safe?" Karkarwa jikinsa yafara yana rarraba ido ganin abun dagaske ne ba wasaba, "Iyyeee na'am wai nnnni .........din" "Oh tambaya kake,kai burgu ku dan taba lafiyarsa na dan minti talatin da alama bayason lafiyar tasa" "Ahah su tsaya,kiyi hakuri wayyo,dama kullum tana wajena,ina yin hakuri shine har jiya nakasa toh yau dana ganta shine,na saya mata shayi da biredi bayan ta shanye najata shagon ilu dama bai bude ba,na biya bukata ta,shine kawai" "Mesunan abinda ka aikata kenan?" Saida yayi dan shiru ganin zata sake zabga masa wani marin yasashi saurin cewa, "Fyade,fyade sunansa" "Kowa yaji laifinsa ko baijiba?" "Eh munji shugaba" Suka amsa dukkansu a tare, "Kai arnen dawa dakkomun abinda nasaka kamin dazu nasan yanzu yayi yanda nakeso,cikin sauri kuwa yabar wajen ,bai dade ba sai gashi da wani kwano abinda yake cikinsa yana turiri, "Kai burgu kucire masa wando yanzunnan" Aikuwa kaman jira suke cikin kankanin lokaci suka sutale masa wando,tun baisan mai zai faru ba yafara ihu yana rokonta, "Shshshsshdh,katsaya da ihun tukunna bari nayi maka wani gargadi,idan ka kuskura nayi maka hukunci kaje gida aka tambayeka mai ya faru ka kira sunana.......,hmmm,saina rabaka gabadaya da abinda kayi amfani ka aikata laifin" Tun bata gama masa gargadin ba,ta juye soyayyan mangyadan da aka dauko daga wuta akan gaban labirun,cikin kankanin lokaci kuwa fatar wajen tafara sutalewa tun daga kasan cibiyarsa har zuwa rabin cinyoyinsa. Su kansu yarannata saida suka girgiza da hukuncin da sameemah tah aikata, "Kuje kujefashi a bayan layin unguwarsu inda yan gidan zasu ganshi,uwarsa saitayi jinyarsa tunda ita ke daure masa kan macijin yake wasa da wutsiyar" Tabbbnnnnnnn,lallai sameemah!! Mucigaba dai mutane Nah🤣🤣😂🤣 ❤❤SADY-SAKHNACEH❤❤ Kar ku manta da #comment #share #like #follow. ____** *GIDAN GANDU* **____ ❤❤By sadi-sakhana❤❤ Wattpad username:SAKHNA03 ❤04❤ Ihu yake yana jijjiga kai tun yanayi da karfi har yazamo baya iyacewa komai sai nishi dayake saukewa kaman mai nakuda tazo gargara dan wahala. Burgune yakalli sameemah wanda har yanzu fuskar sa bata dawo dadai ba da laifin daya ga shugabar tasu ta aikata, "Amma shugaba wannan hukuncin dakika masa baiyyi tsauri ba kuwa?" "Toh ka rama masa mana,saina san kaji babu dadi da abinda na yanke,kai wai yaushe kuka fara ma wannan challenge dinnna wa,ne,banason wani iyayi da nuna tausayi na karyar banza a fuskarku,dan tsabar munafurci har kune masu cemin kuna tausayi,da Y'ar gidanku ya farde,ai bansan sanda zakuyi masa aika aika ba saidai naji anakirana a police station naje na fitar da ku,aikin banza kawai inzaku kaishi inda na sakaku ku kaishi in kuma bazaku jeba ku fadamin saina kaishi da kaina" Sunkuyar dakai sukayi dukkansu suna bata hakuri a tare. Dalewa tayi kan mashindin burgu saida ta burka yafara kara kafin tace, "Zanje gida na dawo,ku tabbatar kun shirya shagalin kafin na taho,bayan kun gama cika aikin" "Bakomai Shugaba bakida matsala" Fisgar mashin din tayi ta bule kura kafin tayi cikin gari da mungun gudu. Bayan ta bacewa ganinsune burgu yajuyo yah kalli su arnan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55