Chapter 10
Chapter 10
tah juyata acikin hannunsa kafin yah raba, "Shiyasa ni da kaganni nan,banason na ci bashi na mayar,dan ji nake kaman ana zarar hanjina" Bayan angama rabawa ne,aka hau wasa,round din farko baban iliyah yah cinye wasa,tattare kudin yah farayi,yana washe baki tareda zuga kansa, "Saini baban iliyah mijin Badariyyah,caca tah sanmu mun santa,nasars a jininmu take" "Eh in ka gama kirarin saika kirgo kudina ka bani koh?" Yana d'aga kansa sukayi ido hud'u da sameemah wanda take tsaye a kansa,kokarin maida kudin cikin aljihu yake burgu yayi Sauri ya warce kudin a hannunsa, Haba sameemah ya zakiyimin haka,Wannan kudin............" "Yimin Shiru Dallah,kai burgu kirgamin kudin kaga nawane" "Dubu bakwaine shugaba" Mika masa hannu tayi tareda cewa, "Miko sauran cikaton kudin?" "Iyee na'am ni banida wasu kudin,haba ke kuwa,yah ina auren yayar ki dan kawai na ari bashinki ki dungamin irin wannan tijarar" "An taba yimaka kaciyah tah biyu?" "Kaciyah kuma?" "Toh in baka daina nunani da yatsa ba saina yimaka kaciyah ta biyu yanzunnan,maza ka dauko kudia sauran dubu uku ka bani yanzunnan" "Ni bani dasu kiyi hakuri,dan allah karki sakemin kaciyah,wallahi ta wanzamai akayimin mai kyau ,bana bukatar ta biyu" "Toh shikenan,kai burgu ku bud'e gadon bayansa kuyi masa balli balli guda talatin,kowace nairah dubu balli balli goma" Kowa a wajen dayaji mai za'ayiwa audu sai yacika wandonsa da iska yabar wajen,shikuwa haka suka danne shi yana ihu yana komai suka babballe bayansa da aska, "Wayyyyyo wayyyyyo,dan Allah kiyi hakuri,wallahi zan baki kudinki wayyyoo" "Mtswww aikiniki banza lokacin biyan kudin ai yah wuce,bari a gama maka kawai saika tafi gida,na yafe sauran dubu ukun ma,kaga yanzu ba zuwa caca sai an warke kuma😄😄😄😄😄". Nan suka tafi suka barshi yana ihu,saida yaji bayan yafara hucewa kafin yah lallaba yah tafi gida,Yana ihu yara suna binsa suna dariyah har yah shiga gida. Tun daga bakin kofah da burgu ya sauketa a mashin takejin hayaniyah,amma da alamun ba na fad'a bane kaman yanda aka saba. ❤❤SADY-SAKHNACEH❤❤ Kar ku manta da #comment #share #like #follow. ____** *GIDAN GANDU* **____ ❤❤By sadi-sakhana❤❤ Wattpad username:SAKHNA03 ❤08❤ Tundaga daga tsakar gidan tayi arba dana miji mai kayan mata,yana ta wani rausaya kaman bishiyah. Saida ya juyo kafin takula a she DAN LITI ne yayan bashari,wanda yanzu yah koma LITTY,da suna wanda rabonsa da gidan tun lokacin su sameemah suna shekara goma. "Hay sister ya kike yah hidima" "Wata harara ta watsa masa,tareda matsawa zata shige" "Habadai y'ar uwa yah antynki tana miki magana kina wani shigewa kamar baki ganni ba,ni ba seemah bace bane" Kare masa kallo tayi,yan da yah sha jan baki,ga hoda kaman zatayi magana,sai rausaya yake yana gyara attachment din dayake kansa wanda ya sakko har kafadarsa. "Hmm kaine antyn nawa?" "Eh mana kinyi mamaki ne ?" "Ahah banyi mamaki ba,taya zanyi mamaki,amma kasani koma kai wayeh banason shishshigi ka fita a sabgata ,in kuma ba haka ba,ko kuma kana tantama ka tambayi y'an gidan suyi maka karatun zama dani in kuma ba hakaba,bazaka iyah jure hukuncina ba,in kunne yaji jiki yah tsira" Tana gama fad'a masa tayi hanyar dakinnasu,dan liti ne (littty)yah juya yana kallon y'an gidan wanda kowa kallonsa yake da mamaki. Sameemah tana shiga dakin su,taga kayan mata,akwatina da kuma kayan shafe shafe,batayi mamaki ba ,sai ma abinda yakawota da tayi ta fice a dakin. A hanyar kofah zata tafi tasake haduwa da shi har sannan yana tsaye a wajen,suna ta tad'i shida su matan gidan,dan yanzu kowa yasake dashi saboda kayan daya kawo ya raba musu,masu shaddodi da masu atampopi,kowa sai washe baki yake yana murna(hmmm mutane da san banza). Dan litine yah kulada fitar sameemah,cikin sauri yah sha gabanta yana tattaro zanin shaddar dayasa,shi a dole ga mace, "Haba y'ar uwa,yah daga shigowa kuma zaki fice,tun safe fah ban ganiki a gidannan ba,kuma yanzu kice fita zakiyi?,gaskiya hakan bai daceba,ace kina mace kina fitah" Yah karisa maganar yana shafa fuska da hannunsa sannan kuma yana kifta ido,takaicine yah isheta ta kasa cemasa ma komai, "Kasan Allah Idan nasake ganin ka shiga lamarina saina b'atamaka rai,sannan kuma kaje dakinmu ka debe kayanka dan dakin matane ba na gardawa ba" "Tabbb kijimin karamar yarinya,me kike nufi ai naje dakin maza gardawa?,bazan iyah ba,dakin mata zan zauna yan uwana,dole mu zauna daku karkuji komai,ni banason harkar kauyanci da rashin wayewa ehhe" "Toh shikenan Allah yabaka sa'a,zakuwa ka bawa wani labari" Fita tayi da sauri dan ta tuna da zasuje ita da burgu wasu yan kato da gorah sun kama yaronta guda d'ayah yasaci akuyarsu a wani k'auyeh. *Wanene dan liti?* Ainihin sunansa shine Shu'aibu ana kiransa dan liti. Tun yana saurayi yabi yan tafiyah neman kudi can kasar kudu onitcha,tun daga can yabi masu tuwo tuwo. Shima kwanci tashi yanzu yazama mai zaman kansa dan yanzu yana da gidan tuwo tuwo har guda uku,gashi yazamana rikekken dan daudu,mai gidan kansa na karuwai da kawalai. Sai wannan lokacin yaga damar zuwa gida bayan barinsa gida na tsawon shekaru,sanda yazo sunyi Mamakin yanda yazama,amma daga lokacin daya fara rabon kaya,sai kowa yah sake yana godiyah,inna karime kuwa sai washe baki ake yi,dan ita kadai saida ta tashi da turmin atamfa har guda goma,ka kuma mayuka da sabulai,ba abinda kkeji sai guda da yada habaici. Da daddare a zaune suke ana ta hira kaman ba su ba,dan liti yabayar an siyo nama an dafa kowa yana ta ci,ana zazzare ido. Mazan gidanne suka shigo kowa saida yayi turus ganin bakon al'amari a gidan, "Ku wace macen ce tazo da mangariba haka?" "Lah baba umaru nice fah litty ,baka ganeni bane" "Lah ha I'll ah,kai dan liti,dama kana nan,menene wannan din zan gani haka" Shi ma kawu shehun uban gayyar kama baki yayi,haka sauran mazan gidan ma, "Meka gani,sabon salone mun tuna gidane shine muka zo,kasan ance duk wanda yabar gida toh gida yan barshi,gwara mudinga tuna gida saboda wataran" "Eh zaka tuna gida mana,saboda in an tashi kawoka sanda kafara kashin ajali koh?" "Haba shehu wannan wane irin fata kake wa danka daka haifah,in bazakayi faran alkhairi ba kayi shiru" Inna karima ta fada tana tafa cinyah ta cuno baki,itah a dole an zagi d'anta mai k'ashin arzik'i, "Lallai karima idonki yah rufe yanzu wannan ne d'an? Yanzu zai tattara yabar gidannan basai anjima na karya jawo mana abin magana,muji da wadda ta baibayemu ma yanzu" "Oh Toh bishiyah ka gani?,kana ganin kayan arzikin dayah kawomin ,idan aka tara abinda kamin tun aurenmu bazai kai hakanba,zancen yabar gidannan kuma babu shi,in abun magana ne ai akwai wanda suka fishi abun magana ma,menene bamuda shi a gidannan,tundaga kan yan fashi,da yan daba,harda yan shaye shaye,toh babu inda zaije,kaima ai bana allah bane,ai kawai ayi sha'anine wai na birni ya cuci na kauye" Kowa shiru yayi jin abinda uwar dan liti tace,wanda yaga dama yayi addu'a allah yah shirya wanda yaga dama kuma yah yi shiru ya bisu da hmmmm. Baba kamulune yah shiga kofarsa inda yasamu amaryarsa wanda bai dade da aurota ba dan itah d'anta d'aya ,kuma jinjirine,uwar gidance hauwa mai y'ay'a guda goma, "Baban su mustapha sannu da shigowa" "Yawwa Sannu,Ina yayartaki ne,kiramin itah" "Ohh ta zagaya bandaki bari tah fito" Suna cikin magana kuwa saiga ta ta fito da buta a hannunta, "Menene yafaru baban mustapha?" "Hmm Ku bakujiba kenan,wai dan litine
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55