Chapter 44
Chapter 44
ranta zai fice,sameerah mai karfin gwiwar tambayar ta menene,amma sauran mutanen dakin koh kallo bata ishe su ba, "Ba........ba shine ba wai an zanye yin auren sai ya dawo daga service din aikin dan sanda ,yace wai sai bashida kudi toh sunansa ya fito a cikin masu tafiyah service,kuma dama wai bai gama giniba yana so dama a daga auren" "Koh so yake yah gudu dama ba" Salma ta fada tana dariyar mugunta,wani ashar zainab ta nana mata kafin suka rukume da fada kaman karnuka. Itah kuwa sameerah da dakin mahaifiyar su ta nufah da sauri domin jin tushen bayanin. Da wuri ta tashi yau babu baccin safe,wanka tayi ta ruwan sanyi amma ba ta sanyin take na burinta kawai taje inda yake ranta. Kayan uniform ta dauko na vigilant ta saka,dan karamin hijab din kayan ta saka tareda dora hular a kansa,hoda ta shafa kawai sai mai kafin ta feshe jikinta da turare,glass ta saka baki wanda yayi match da wandon jikin ta ga kuma kalar fatarta ta fito a cikin coffee rigar tasu,jakar ta dauka da kuma key din motarta kafin tah fita daga dakin. Duk abinda takeyi su salma suna kallonta,dukkansu mamaki suka dungayi da ganinta cikin kayan,dan babu wanda tah fadawa zata fara aikin. A tsakar gida kuwa bata hadu da kowa ba har ta isa wajen motarta ta shiga. Su surayyah kuwa an fi kowa d'oki dan rana ma acan ta fito ta ganta,dukkan su kame wa sukayi tareda sarawa lokacin da sameemah tah iso wajen,dan labarin sauyin shugaba dama yazo musu,kuma sunyi farincikin da hakan dan dama babu wanda yake somsa,shiyasa da tace wanda yake bukata zai iyah tafiya babu wanda yah tafi,suna fatan dai kar ayi gudun gara a tadda zago. Fitowa tayi a motar tana gyara zaman glass dinta fuskarta babu alamar fara'a bakinnan a d'ane. Hanyar office dinta ta nufa koh kallonsu batayi ba,wata bazawara ce wanda anan suka zo suka samesu tah kalli surayyah tareda sauke murya kasa kasa tace, "Hmm kika ce shugabarku tanada mutunci?,amma yanzu ji yanda tazo ta wucemu koj kallonmu bata yiba bayan wannan shine zuwanta na farko" "Ke me kike ci na baka na zuba yanzu fah aka fara wasan,ki tsaya ki gani mana" Itah kuwa sameemah batayiwa kanta a ko ina waijiba sai kan kujerar ta office din,saida ta zuyah ta sake juyahwa kafin ta saki wani dan iskan Murmushi. Wasu takardu aka kawomata da alama sauran aikine da tsohon shugaban bai gamaba. Zare glass din idonta tayi ta ajiye a gefe kafin ta daga takarda tah farko,case ne akan yanda karuwai da yan daudu sukayi yawa a gidan kara,yan hisba sun kawo case din akan za'a hadu dasu ayi amma babu wanda yayi magana. Sai kuma na gaba yanda sane yayi yawa a kasuwa sannan idan an kama su yan sanda basayin komai akai,da kuma wani saurayi dayah kama wani tsoho a unguwarsu yayi masa duka,dan kawai yakaishi kara yah sace masa akuyah. Dariyah sameemah tah fashe da itah saida mai kawo takardun yah ja da baya,daga ganin dariyahr kasan ta mugunta ce zallah, "Irin wannan kujerar dama nake nema,inda zan baje tawa baiwar,kai inaso ka kiramin duk wani maikaci yasameni a waje yanzunnan" "Angama Ranki yah dade" Da gudu yah fitah kaman zai kifah. Bayan mintu kadan yadawo tareda shida mata kowa ya hallara. Fitowa tayi ta tsayah a gabansu,kowa yah kame kaman an daskarar shi,yaranta ta kallah acikin tsofin maikatan dukkan su sun sha kaya kaman ba suba,koba komai taji dadi da ta sama musu sana'a. "Inaso kijini da kyau,wanda suke wajennan dayawa dama yarana ne nasan halinsu,su kuma sauran na duba bayanansu wanda ina fata muyi aikin daya kawomu banason shashanci. Abinda yasa na kiraku shine,akwai casr kuda uku wanda sune suka fi girma kuma ina so yau dinnan basai gobe ba a gama dasu" File din ta Bude tareda kiran suna,saida ta tabbatar ta raba wani rukuni gida uku tukunnan tace sauran su koma aiki. Su burgu tah nuna da wssu suma biyar tace su je kasuwa,duk wanda yayi sata su kamo mata shi kafin ma yan sanda du sani,sannan wsu ma guda uku tareda surayyah da kuka shamsiyyah(bazawar nan),su kamo mata yaton da yayi duka ga tsohon anguwarsu. Sai kuma wanda tasaka akan aje gidan kara kamen karuwai,amma kar a tabasu har sai taje tukunnan,kawai suyi kaman ba wajen suka jeba su yi shiru har zuwa yamma. Nuna lubna tayi da kubra kafin tace su biyota zuwa wani waje. Direct office din hisba ta nufah,tana isa ta nemi iso zuwa office din shugaban,shiga sukayi ta zauna su kuma su kubra suna tsaye a bayanta sun kame,dan dama matan sun ji karfi da kuka kira,bare suka samu training daga wajen sameemah na salon fada daban daban,shiyasa itama take ji dasu ta wannan fannin. Dagowa yayi daga rubutun dayakeyi yana kallonsu,ganin sun shigo amma babu wanda tayi magana, "Eh ina jinku mai ke tafe daku" "Da baka tambayi mai ke tafe damu ba shiyasa nayi shiru domin baka daMa ka gama,amma yunda yanzu ka taambaya sunana sameemah sabuwar shugabar kungiyar vigilantee. Gameda abinda yakawomu kuma ba kkmai ba ne illah akan zancen case daka rubutah na gidan karuwai ne yakawoni saboda na ganshi a office" "Eh anyi haka amma wannan case din yace bazasu damar yiba,ku kuma muma muna wani aikin har yanzu gashi bamuda wasu ma'aikata masu yawa,idan muka ce zamuje irin wannan aikin mu kadai,mukan samun barazana,toh shi kuma yace mana wai ogansa ya hanashi irin wannan aikin" Numfasawa sameemah tayi dan tasan wa yake nufi da ogan, "Shikenan karma damu dama akan case din nazo,Inaso kasaka hannu akan takardar Ta yajejeniyar ni zan ajiyesu a wajena ba ma kune zakuyi ba, nikuma a yau basai gobeba zan kamasu" Hankalinsa ne kaman bai dan kwanta da zancneta ba dan da alama bai wani yarda ba,ganin hakanne yasa tace, "Idan wata matsala ta faru ka dora laifin a kaina sannnan karka sake bani wani hadin kai anan gaba" Karbar takardar yayi yai mata sign din kaman yanda ta bukata kafin yabata. Tana fitowa direct gidan karuwan suka shige,acan nesa da wajen suka hadu da sauran yarannata inda itama ta fito daga motar ta suka shige. Gidane mai fili sai dakuna dayawa,kaman dai gidan haya,da wasu yam daudu suka fara cin karo a tsakar gidan suna wasan karta,aikuwa suna ganinsu suka rufah da gudu kowanne yana zefar da zanin daya rufe kirjinsa dashi. Dakuna dakuna suke bi suna fito da mutanen ciki,mutane kala wasu da attach wasu saikace fatalwa dan fari. Duk tarasu akayi a tsakar gidan masu ihu suna yi masu roko sunayi. Wata kujera sameemah taja ta zauna tanan kare musu kallo,wai yau itah ake roko kartayi rashin mutunci,gashi kuma gangar rashin mutuncin nata ta riga ta kada sauti. Wani dan daudu ne yakalle ta tareda cewa, "Haba ke kuwa sister ai andaina zamanin kame tun wancan karnin,ki fadi kawai nawa kike so a baki a wuce wajen" "Ahah mai kake ci na baka na zuba dama ai za'ayi ciniki,har saikayi cinnki ka kaji,yanzudai bari muje a gyaraka ka koma ainihin siffarka tukunna koh?" Shiru yayi jikinsa yafara tsima jin abinda tace,wata ce a cikinsu tace, "In gaskiya ne naga ba'a je chamber su yar sheelah ba idan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55