Chapter 13
Chapter 13
har zuwa gobe" "Shikenan promise karka dade" "Yeah I am sure" "Okay bye " Toh nima bye😍😍😍 ❤❤SADY-SAKHNACEH❤❤ Kar ku manta da #comment #share #like #follow. ____** *GIDAN GANDU* **____ ❤❤By sadi-sakhana❤❤ Wattpad username:SAKHNA03 ❤10❤ Sai can wajen karfe 9:00pm,kafin sameer yadawo daga inda yacewa saleemah zaije,batare da tambayeshi mai ya faru ba kawai tah fara zazzaga masifa dama tah cika tayi famm ,dan tun dazu take jiransa a falo bayan tayi sallah. Takaicin halinnata ne yasashi wucewa daki kawai batare da yabata karin bayani ba,itama bata huceba binsa dakin,sanda tah shigo yajuyah bayansa yana fitarda wani huci mai cike da bacin rai,saleemah bata kulada yanayin dayake cikiba tah cigaba da ta cigaba da mitar da take, "Amma abban farouq dakai fah nake magana shine ka shareni ka shigo daki bayan kasan..........." Katseta yayi daga karisa maganar sanadiyyar had'e bakinsu dayayi waje d'ayah,yah dad'e kafin yabata damar jan numfashi. Fatar bakinta har saida tayi ja saboda farmakin daya kai mata cikin zafin nama,kallon idonta yake kafin ya fara magana kasa kasa, "Dama ina abinda yasa kika damu na zauna a gidan kenan,sannan dana shigo ma kika fara fad'an na dad'e?,ba damuwarki rashin dawowa tah ba ko halin danake ciki,burin ki shine wannan,toh zo na baki" Cikin halin ko inkula da maganar da yayi mata cikin salon maganar halinka mai sanda kuwa tah cafke bakinsa tareda maida martanin kiss din. Sun dad'e a tsaye kafin suka isa ga kan gadon,saidai gogan cikin zafin nama daya kuma had'u da halin dayake ciki na baci rai yake kaiwa duk wani sassan jikinta farmaki. Tun tana jurewa har tah matsa daga inda yake tah koma gefe tana sheshshsekar kuka,(dama su saleemah sakalai). Shikuwa kansa yasaka acikin filo yana cije lebe tareda sauke ajiyar zuciyah,yah dad'e a haka shikadai yasan halin dayake ciki. Itah kuwa saleemah tun yana jin ajiyar zuciyarta har yah fara jin numfashinta yayi nauyi da alamun tayi bacci. Tausayinta ne yakamashi,danshi kansa a sanin dayayi mata yasan bazata jure yanayin daya zo mata dashibagashi kuma tana dauke da yaran ciki,saidai shikansa yana tausayin kansa domin yasan koh kusa zaman su da saleemah bazai dore da haka ba,dole yah nema wa kansa mafita ,duk da yasan fitina yake shirin kunnowa,dan saleemah da d'anta ma kishi take ina kuma ga wata matar idan yah auro?(tabb hmmm). Yah dad'e yana tah Tunani kafin yah tashi ya shiga bandaki. Saida yah yi sallahr dare da addu'o'i kafin shima yah koma ya kwanta. Da safe har sameer yah tashi yah gama shiryawa amma saleemah bata tashiba,kare mata kallo yayi da takaici kafin yace bayan ya bubbuka gefen filonta ta tashi, "Wai kinyi sallahr dana tasheki kiyi da asuba kuwa" "Eh nay I" "Toh shikenan ni na tafi,sannan na manta ban fad'amiki ba,ki shiryah a cikin satinnan zamuyi tafiyah,zanje na gaida iyayena sannan kuma kakanmu alhaji babba bashida lafiyah" Mitstsikewa idonta tayi tareda tashi zaune kaman ba itah ce take muryar bacci ba, "Gidanku kuma?" "Eh gidanmu menene a ciki?" "Amma bazaka tafi kai kadai ba,kasan fah ni ba lafiyah ce dani ba" "Tareda Ku zamu tafi dan nagama yanke hukunci,saboda tunda na aureki baki taba zuwa garinmu ba ka kuma farouq basu sanshiba yakamata na kaishi gidan kakanninsa yagansu" Bai jira amsar dazata bashiba ya yi ficewarsa yabarta a kan gado baki a sake, Tabdijan garinsu kuma,toh wata sabuwa(😂 yarinya zakije gidan gandu ki more). GIDAN GANDU PALACE(na su princess sameemah😂) Koh kwana biyu ba'ayi da tafiyar dan liti ba saiga shugaba MANJO yah diro garin. Koh sallama babu said ganinsa sukayi a tsakar gidan yana zazzare ido kamar anyi masa kwalli da barkwano,kowa idan yah kalleshi sai yah karewa dress din jikinsa kallo. Saboda wata biri da wando yasamu yah mamuk'a hantsar da matseshi ,kafafun rigar kuma a iyah gwiwarsa suke,ga kuma hular sanyi daya tabka,sannan ya goyi wata uwar jaka a baya. A takaice dai kana kallonsa kaga mahaukaci sabon kamu,yaranne suka tafi da gudu suka kirah kulu a kofarta,da sauri ta fito jin ance manjo ya dawo har tana tuntube da gyara zaninta,turus tayi ganin irin shigar dayayi ga kowa sai dariyah yake kasa kasa,haushine yakamata ita da inna ramatu saboda daga gani babu wani abin arziki daya kawo,saida yah juyo ne kafin yah kulada kulun, "Lah kulunkulun din manjo bakya ganin na dawo ne,babu wani dan tarba ta irin miji da matar nanne?" Duk maganar cikin shakyakykyiyar muryah yake yin ta,ga bakinnan jawur dashi kaman bakin tsoho mai cin goro,tab'e baki tayi kafin tace' 'Wannan shigar fah daga iyo ta me cece?" "Lah wannan suwaga ce,suwaga ba ,ai irinta ake yayi" "Mtswww Toh naji,saika shigo ai muji dame kuma ka dawo" Binta yayi kaman rakumi da akala suka yi kofar tata,dan idan suna dad'i itah dashi tana juyashi yanda taga dama,saidai idan kwayar tagaya masa ba daidai ba kokuma tayi masa laifi ,toh ba iyah ita ba ko yan gidan sai sunsan an tab'oshi ,dan manjo shima number one ne wajen rashin mutunci,gashi bayan manta tsiyar da akayi masa a sauki. Suna isa kofarsu manjo yah akiye jakarsa yah shiga bandaki ,kulu ta dau jakar tareda zazzageta a tsakar dakin,zare ido tayi gsnin abinda yake dauke a cikin jakar,ba komai bane sai wasu shafta shaftan silifas da kuma wani tsohon bargo sai kuma kayansa guda uku,har sun sanja kama dan daud'a. Manjo yana shigowa dakin kulu tace, "Wai uban me toh ka kawo duk tsawon dad'ewa dakayi da tafiya ranin iyee?" "Uban me nakawo kaman yah?,tsaya wai kema uban me yasa kika zazzagemin jakata,har zaki wani sakani a gaba mai na kawo,uwarki na kawo,kulu billahillazi ki kiyayeni ,tunda na dawo kikemin masifa kaman wani d'anki,dan kinga ina muss(missing) dinki,toh wallahi zan ajiye muss din nayi miki duka,kinga saiki tunoni mu zauna lafiya" "Eh zakace zaka dakeni mana saboda ga jaka,karyah nayi uban me ka kawo,naga jiya dan liti daya zo rabon shaddodi ya dungayi da atamfofi nima har turmi biyu aka bani " "Ke dan yah rasulu,sheege toh ina tawa shaddar nasan yah bayar a ajiyemin kinga saina dunka in za'ayi daurin aure a gidan mudunga sakawa muna fitowa a manyan yayu,kuma baki isa kicemin an baki ki ajiyemin kice kin sayar ba,dan saikin fito da itah yanzunnan" "Kutt lallai ma manjo wai wannan wane irin zance kake ne haka,toh ko yah baka ma bazan ajiyeba sayarwa zanyi barema babu wanda yah tuna da wata halitta wai itah manjo,dan koni saida akacemin ka shigo kafin na tuno da kai,saidai bansaniba koh inna ramatu ta tuna dakai" "Kulu kulu tam" "Menene? Dukana zakayi yanda ka saba?" "Ahah bazan dakeki yau ba saidai inaga gobe kam saina yimiki lilis yanzudai debomim abinci tukunna,idan naci kuma saina zaga gari domin asan na dawo garin" "Ni ban dafa komai ba,saika jira in an gama na dare na karbo maka" "Ke Wai ina wancan shedaniyar yar wiwi dinne,tunda na dawo ban ganta ba" "Me kake ci nabaka na zuba zaka ganta ai,tsab zaku zone,nida kwanaki sauran kadan tah cire min wuyah" "Kehh wuyah dai batason kece matar manjo,lallai zata gamu dani" Tunani kulu tayi da ta tuna cewa sameemah tah san sirrinta,aikuwa cikin sauri tace, "Kai manjo da gangan nake fah irin wasan nanne" "Aiko wasane sai nayi mata masu warning (last warning) saboda gaba" Daga haka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55