Chapter 3
Chapter 3
"Banjin sunan zazzakar kazar ba?" "In min hadu zakaji abinda yafi suna ma" "Shikenan idan kinshirya zamuyi waya " Bata sake cemasa komai ba tafice daga cikin parlorn. Bayan sun gaisane shida alhaji Sama'ila,sai yayi shiru kaman mai tunani yana ta murmushi shikadai,alhaji Sama'ila ne yakatseshi ta hanyar cewa, "Amma alhaji BALA naji dadai kuwa harkar da kuka kulla kaida seemah jar wuyah" "Au Ashe kajimu,gaskiya na samu dami a akala dan dagani zatayi dadin harka sosai" "Hmm alhaji bala kenan,anya kuwa kadauki dami mai kyau kuwa,karfah ka dauki dan maciji ina........,.." "Kai kai alhaji Sama'ila menene kuma na wannan maganar,babu abinda yafaru kabar ma wannan zancen muyi abinda yakawo mu kawai". A wajen fita waje kuwa bayan sun zo hawa mashin,burgune yakalli sameemah da Mamaki abinda yafaru, "Amma shugaba maganar da kukayi keda wannan alhajin anya ba matsala kuwa" "Me nake Tunani,ka fara mantani ne,gaskiya yakamata ma na fara sabon aiki dan ina ganin nayi laushi dayawa tunda har kuke min wannan kallon kaman kuna gaban kannenku mata na gida" Basu sake cewa komai ba sai burka mashinansu dasukayi kowa ya dale,dan da alamar sun jiyo gargadi da kuma fushi a cikin muryar tata. Acikin gidan gandu kuwa tun safe ake abu daya har rana ta fara zafi lokacin daura abinci amma babu alamar zasu daina hayaniyar dasukeyi. Inna larai kuwa tun ana jiyo muryarta da karfi harta fara dushewa saboda masifah,kawu shehu ne yayi sallama ya dawo daga gona,tun daga wajen kofar gida yakejin masifar da akeyi wanda inda sabo yariga ya saba,saidai daya shigo gidanne yakula da kofar tasa cike take da mutane kaman ana rabon kudi,karo sukayi da baba umaru (baban su sameemah)wanda shikuma gadin makarantar primary anguwar yake wanda antashi kenan ya dawo gidan, "Ahah shehu yadai kana kallon gaban ka kuwa?".a kokuma maganin abinda yafaru?,ai kin fi kowa dabbanci da irin wannan kwakwalwar taki,baku da aiki sai shege kishi da fada,shi kadai kuka iya kawai" Baba umarune ya rike kawu shehu wanda yake ta zazzagawa larai masifa saboda tsabar ransa yabaci,daki ya wuce yadauko yarinyar wanda jikinta yayi zafi rau saboda Zazzabin daya hau Jikinta. A hanyar fita suka hadu da mazan gidan guda biyu,da Sule dakuma Bashari wanda dukkansu yayan baba umaru ne, "Yawwa kai sule bi bayan kawunka shehu ku tafi asibiti ,kai kuma bashari zo mu tafi wajen yan sanda" Hakan kuwa akayi kawu shehu suka tafi asibiti,wanda ganin zasu tafi yasa inna larai dauko gyalenta tabiyo su har waje,saida baba umaru yasaka baki kafin kawu shehu yabar ta bisu asibitin,saida tayi ta rusa musu ihu tukunna aka barta ta tari mashin tabi bayansu. A wajen su baba umaru kuwa,saida suka bi layi tukunna suka samu layin yazo kansu,dan sandanne yakalli su baba umaru amma idon sa yafi tsayawa akan bashari da alama yaganeshi, "Malam muna tsaye amma bakace mana komai ba" "Eh ina jinka menene yake tafe daku" Saida suka tsara masa, abinda yake faruwa tas kafin ya yamutsa guska yace, "Hakikanin gaskiya babu inda zamuje kamo wani dan ya taba wani mutum a gidan gandu,saboda kuma da wani a cikin gidanne ya aikata mukaje kamoshi da kyar zaku bari dan sandan yafito da ransa in ya fito ma to saikun sanja masa kamanni kuwa. Toh fah yadai gidan gandu?? ❤❤SADY-SAKHNACEH❤❤ Kar ku manta da #comment #share #like #follow. ____** *GIDAN GANDU* **____ ❤❤By sadi-sakhana❤❤ Wattpad username:SAKHNA03 *wannan shafin sadaukarwane kwacokam ga,@sumayya yarima,@Aisha dakuma @hajiya,allah yabar kauna ga duk masoyana,hakika ina godiyah sosai* Bari muga nagaba kuma😀😀😀😀 ❤03❤ "Baba kayi hakuri fah dan yayan gidankune suka jawo,lokacin da mukaje kamo manjo dan gidan malam IDI a gidan ya saci mashin din wani saurayi kuma yayi masa duka,naga wannan shegiyar yar takace ta aiko mana arnan yaranta sukayi mana faca faca da ofishinmu,waima dan bata gari ba da kanta tazo ba,dan haka babu inda zamuje,in labiru kuke zance ma,dazu wasu samari suka kawomana kara wai sun nemeshi sun rasa a baking rafi lolacin da suke shan rake dazu,dan haka ku tattara naku ya naku kubar nan wajen tun wuri" Cikin sanyin jiki na rashin sa'a suka bar wajen,wanda dama shi bashari baiyi magana ba,inda wajen tsara yan matane da bleaching toh ya rufe kofah,amma harkar yan sanda kam,matsoraci ne shi sosai na bugawa a taro. Fitowa sukayi daga police station suka tari acaba wanda zai kaisu asibitin da aka kwantar da hanifan,nan ma saida akayi ja inja da mai adaidaita sahu kafin ya daukesu,suna cikin tafiyane bashari yagyara zama yafara magana wacce baiyi ba tun sanda aka shiga police station din, "AI baba umaru in fada maka,mutanennen basuda imani,cewa muka cemusu anyiwa fah yarinya fyade amma ji yanda suke wani nuna halin ko inkula,hmmm abin duka babu sanda" "Dallah can yimin shiru da fuska kaman ta sabuwar fatalwa,waiku adole yan gayu,duk kun shafa mai kun mele fuska kaman wanda aka bi da dutsin guga,zaka ce wani abin duka babu sanda in anbaka sandan uban me zaka iya idan an baka sandan,akwai abinda ka iya ne banda shegen zuwa wajen yan mata,duk wani dan kudinku anan yake karewa da kuma sayen tsukakkun wanduna" "Kai baba umaru ku bakwa gane zamani,idan ta ganka baki babu wanka ai babu rabin zance,ai idan ta ga fuskarka fara tas ga kuma wandonka irin sabin gwanjonnan yanzu zakaga ana love wallhi in ba kaiba sai rijiya" "Kai bashari zaman mu lafiya kayimin shiru anan wajen tammmm" Shiru kuwa yayi da bakinsa bai sake cewa komaiba har suka iso asibitin da aka basu gadon. A wajen cashier suka hadu dasu inna larai a tsaye suna jiran layinsu ya iso saboda ganin likata(kasar tamu kenan allah yah ya fiddamu cikin wannan hali). Kudin wajennasu bai isa ba ,saida baba umaru yaciro guntun sanjinsa kafin aka bawa mai karbar kudin. Bayan sun samu an basu gadone,baba umaru yah kalli kawu shehu yana mayar masa yanda sukayi da yan sanda a police station dazu,tun bai karisa jin mai ya faruba ya fara masifa saboda tsabar ransa ya baci, "Hmm dama nasan za'a rina,wai an saci zanin mahaukaciya,duk sun bata yayannan basuda aiki sai jawo magana acikin gari,kowa acikin su bayason laifin dansa toh yanzu wa gari ya waya ,gatanan ina tatura yarinya kwadayi anyi mata aika aika tabar mutane da wahala" Inna larai ce ta goge idanunta da yacika da hawaye ta dubi kawu shehu cike da masifa tafara magana, "Kai shehu ya isheka haka,kawai zaka samu mutane da shegiyar masifa,zaka ce wani mun b'ata y'ay'a ,aikai suka iyo kaidin na allah ko kanace bamusan mai kake aikatawa,dama wanda yayi ai sai anyi masa,kuma dama kyan d'a yagaji ubansa,kai suka iyo,dan haka kadaina wani jingina laifin akaina eheee" Kunyace takama kawu shehu ganin yanda inna larai tafere baki ta masa wankin babban bargo da masifa kaman d'anta gashi dakin Da'aka kwantar dasu da mutane. Sallama baba umaru yayi musu ganin yanda abin yafara zama na tone tone maimakon zaman jinya,fatan samun lafiya yayi musu yai hanyar gida na fatan allah ya kyauta aransa. Yana shiga gida inna RAMATU(matar baban SAMEEMAH ,uwar su sameerah )ta tari baba umaru da barka kaman ba itaba,da Mamakin sa yah kalleta saidai ya boye baice komaiba,ruwan sanyi ta kawo masa da shinkafa fara da mai da yaji da akayi da ranar. Saida yah wanke hannun sa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55