Chapter 65
Chapter 65
ake bukata tunda shima ya zama business man, sosai suke samun nasibi baya ga business dinsu da Maryam Kuma, sun Kara da saro designers perfumes, shoes and bags latest designs. Rahima ta biyawa Umma da Baffa kujerar Hajj, ranar Umma Saida ta zuba ruwa a kasa tasha domin murna tare da godiyar Allah da ya rayasu ya shirya musu zuriyyar ya daukaka su har an fara dawainiyya dasu da wasu ma duk ana cin gajiyarsu. Ka'idane duk shekara Haseeb na fitar da zakka ya rabawa marasu galihu, ya kuma biyawa wadanda Allah ya tsaga rabonsu zuwa sauke farali ko Umrah, wannan karon kuri'ar kan Lauratu goggon Rahima, Malaminsa Mal. Nuhu da amintaccen maigadinsa Mal Hassan ta fada.. Rahima tace itama zata biyawa Uwale da fatar Allah ya kai ladar kabarin mahaifiyarta da Rabi'u Duk karshen wata suke haduwa family ana sauke qur'ani a gidan Daktan, in an kare ayi adduoi ga dukkan mamata da masu rayuwar, iyaye, 'ya'ya, 'yanuwa da abokan arziki, jiharsu da kasarsu baki daya. Duk ranar jumma'a za a dafa abinci a rinka rabawa mabukata sadaka duk don neman yardar Ubangiji da neman karin yalwarsa cikin dukkan al'amurran ratuwarsu. Aikin Dr Haseeb sai dada bunkasa yake, sunansa na dada yaduwa yayinda yaci gaba da bude rassuna jiha-jiha Yana samo kwararrun likitoci Yana zubawa Gwamnatin tarayya ta yaba da kwazonea kwarai suka bashi mukamin *Minister for health* Yace bai so hidimomi sunyi masa yawa... Mata da 'yanuwa suka yi masa ca! Bai amince ba saida Hajiyarsa tasa baki tace "Ya Allah zai maka daukaka ka butulce? Hidimomi ba Allah ke taimakonka tafiyar da komi ba ko da karfinka kake?" Ya amsa da zuciya guda ya fara aiki. Kamar ba za a sake haihuwa gidan ministan ba domin Saida Ummi ta shekara uku aka samar mata kani, wannan karon sai ga kyakkyawar yaro, ga tsawo ga kiba, babansa zahiri.. Ranar suna Saida kowa yai kwalla da yaji sunansa *Rabiu* Nauyi kam ya karu kan Daktan, ga na iyalinsa, ga na Mahaifiyarsa, 'yanuwa dana yanuwan Zuwaira ga na jama'an Annabi da suke cin arzikinsa banda na aikinsa, ya zama bai da lokacin kansa. A ka zo batun komawa Abuja Zuwaira tace sai dai Rahima ta tafi domin ta sakankance ita dince ce *star* din Haseeb, ta kuma hakura da haka duk da cewa ba nuna banbanci yake tsakaninsu a zahiri ba, Rahimar taki yarda da shawarar Aunyn ta domin tsakaninta da ita girmamawa ce. Da kansa takobin dagan ya raba gardama cewan kowacce zata rinka zuwa wata uku ta dawo dayan ta tafi Kuma, wace lokacin hutu ya shigo cikin turn dinta ta tafi da yara. Zuwaira ta sake samun 'yar bebinta 'yar caraf kyakkyawa, da ganinta tace wannan ai Rahima ce,kamar yana jiran ta furta, ministan ya rada mata suna *Rahima* suna kiranta Amira. Zuwaira na murna ita kuwa wace akayi dominta ta korafin me yasa ba a fara sanya sunan Zuwaira ba? Ya kalleta yace "Banyi gwaninta ba kenan?" Ta amsa "Wallahi kayi sosai na kuma ji dadi nagode amma kayi min alkawarin idan muddin na haifi mace Zuwaira ce." Yace "Allah ya kawo cikin, shin ko har an samu?" To Allah yayi an haihun amma namiji aka samu sai yaya kenan? Ya rada masa suna Habibullah. Shekaru sun mika kwarai, tuni Dr Abdul Haseeb Junaid ya ajiye aikin gwamnati bayan shekaru takkwas yana bautawa kasarsa a matsayin ministan lafiya. 'Ya'yansu maza sun kare univertsity. Junaid (Khalifa) Engineer ne, Mohammad(Abba) Architect, Abdul Haseeb karami ya bi sahun babansa ya zama likitan kwakwalwa, yana kasar Bulgeria karo ilmi. 'Yan matan Kuma Muhibba ta dage saita zama irin Dr Kausar ta cikin littafin Anti Saliha Zumuncin Zamani, ita din Gynaecologist ce, Ummul Salama Lawyer ce don ita Bartister Tahir ne gwaninta(Son Zuciya) Ummi Habiba sha'awar Boutique din Sufab ya tunzuro ta da yadda ita kanta Surayuar ke tafiyar da business dinta da son taimakon iyayenta yasa ta karanta Business Administration yayinda Amira Rahima ke son zama cikakkiyar malamar makatanta mai zaman kanta irin na Sa'adatun Sagir haka dan autan gidan Daktan yace shi malamin lissafi zai zama, so Habibullah mathematician ne. Wata rana Daktan ta tara manyan 'ya'yansa lokacin Abdul karami ya kare karatunsa yace lokaci yayi da kowannansu zai fitar da abokiyar rayuwarsa. Ba bata lokaci Junaid ya nuna Walida diyar Maryam yake so wace ke zuwa hutu wajen Innarta Rahima, Muhammad yace Nabila diyar Uncle Hayatu. Wadannan 'yan Mata duk karatu suke a B.U.K. ne, Walida na karanta Mass Communications tunda a rayuwarta Laila Tahir Mutallib ce role model dinta, Nabils na karanta Economics. Idan ta bi daga-daga na kurya kan Sha Kashi, Abdul Haseeb junior yayi shiru bai ce komi ba, to shima miskilin ne irin uwarsa da wan uban, to Barewa tayi gudu ne danta yai rarrafe? Baban nasa yaxe ya rubuto sunan wace yake so tunda ba zai furta ba, ya rubuta ya ajiye, yana fita ya dauki takardar ya warware, abinda ya gani yai matukar faranta ransa, ba domin namiji yake ba da yai guda Amma yayi abinda yafi dacewa yayi a irin yanayin, ya daga hannuwansa sama yace "Tsarki ya tabbata gareka ya Allah Ubangijin Al'Arshi mai girma!!! Ya sake duban takardar da Abdul ya rubuta *Daddy Rahima Amira ce mata ta Insha Allahu* Ya juya takardar yana mamakin ko ya aka yi yaran suka yi tunanin hada auren zumunci gaba dayansu oho? 23/09/2020, 12:31 - Anty saliha: ...RAHIMA...doc by jami 54 Iyaye, 'yanuwa da kakanni kama da abokan arziki da sauran jama'ar da suka ji labarin hada wadannan igiyoyin aure sai sha'awa da murna suke. Kasa-kasa ba inda Daktan bai aika da katin gayyata ba, duk wasu masu hulda da asibitocinsa, abokai da tawagar shugaban kasa da kusoshin gwamnatocin jihohin Arewa sun halarci wannan gayarumin dauren aurarraki. Da yake al'amarun tuwona Mai na ne shi kansa Daktan ya rasa inda zai fi maida hankali a sha'anin, to kusan shine uban angwaye da amaren baki daya, haka ya wakilta kanninsa da abokan arziki aka taru aka yi komi cikin tsari gwanin sha'awa. A wajen bukin ne su Ummul Salama suka hadu da masoyansu ita ta hadu da abokin Khalifa, Muhibba dan abokin babanta balarabe nan na Riyadh ke sonta, har sun amincewa juna, sai adduar Allah ya nunawa iyaye lokacin nasu bukin. Bayan an gama shagalin da wata guda, kura ta lafa, Zuwaira ce da Rahima ke zaune a main parlour suna hira, sai kallon Rahimar take cike da sha'awa tana yaba yadda take tafiyar da al'amurran rayuwarta ta yau da kullum, me zata ce da wannan baiwar Allah? Gaskiya sai godiya da adduar Allah ya saka mata da khairan domin a dalilinta ita kanta da 'ya'yanta sun samu nagartacciyar rayuwa, ta sami kan maigidanta yanzun girmamata yake sabanin da can inda aka fito..... Karar waya ta dawo da ita daga duniyar tunani, tayi firgigit daidai Rahima ta dauka ta sallama, can taji ta rafka salati ta kalli Zuwaira, ita Kuma a firgice tace "Me ya faru wa Kuma muka rasa?" Rahima tace "Allah yaiwa Husaina rasuwa sanadiyyar accident.....Zuwaira tayi kasake tsoron Allah ya Kara kamata, duniyar kenan mai halin dan mangwaro, sai ta bari ka saki jiki kana tsotso kana jin zakinta ta subuce maka. Ita yaushe rabonta da ita tun ranar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66