Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 48

Chapter 48

Rahima Book 1 Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

zai amsa, idan aka nemi jin kansa dasu zai yi jin Kan, idan aka nemi yayewar tsanani zai yaye.. Ki tabbatar da kafin ki fara kowcce adduar kin fara gabatar da shimfida, watau istigfari da salatin Manzon Tsira, idan kin kare kuma ki sake rufewa da salatin. Idan zaki yi addua ki rinka girmama rokon, ki daukesa da muhimmanci, ki rinka na ci, sannan ki dunkule bukatarki ki roki Allah Kai tsaye, ki yawaita tuba da yin adduat tare da sauran jama'ar musulmi Kar kiyi ta rokon ke kadai. Babban muhimmin abu game da addua shine tawali'u da rage aikata sabo da tarar lokuttan da aka yi nuni ana amsar addu'ar. Misali idan cikin dare ne tsakiya da karshensa don ance a wannan lokacin ne Ubangiji ke tashi da kansa yana Kiran Ina me neman biyan bukata in biya masa.. Kinga Wanda duk ya dace da wannan lokaci yayi kyakkyawar sa'a.. Akwai farkon asubah da karshenta, sai lokacin da mutum ya fuskanci abokin gaba wajen yaki, lokacin saukar ruwan sama, bayan kiran sallah da tsakanin kiran sallar da tada ikama, ko ki fuskanci alkibla ki rokesa, amma inda Ubangiji yafi amsar addua shine yayin da bawa ya kaskantar da kai cikin sujada ya roki Mai dukan zai amsa. Saboda haka yanzun ma ki tashi mu gabatar da sallar nafilar da ma'aurata keyi mu nuna godiyarmu ga Ubangijinmu da ya kaddaremu yin wannan aure, mu rokesa ya tabbatar mana da dukkan alkhairinsa ya kade mana kiwanne irin sharri. Ta mike tsaye ta saka hijab dinta suka natsu, ya shiga gaba ta bi bayansa suka gabatar da nafilar, bayan sun idar ya juya gareta ya dafa kanta ya sake rokan Ubangijinsa alkhairinta da neman tsari daga sharrinta, daga nan ya umurceta da suka karanta suratul Ikhlas kafa 3 ko11 suyi taswili zuwa kabarin Rabiu, iyayensu da dukkan musulmi da suka rigamu gidan gaskiya. Duk hakurinta ta kasa danne zuciyarta tunanin Rabi'u da mahaifiyarta da bata taba sani ba a rayuwarta. Kuka take Mai tsuma zuciyar Mai saurare, hankalinsa yai dubu ya baci, ya fara rarrashinta "Rahima kiyi hakuri Allah ya gafarta musu, meye na zubda hawaye bayan munyi musu addua shi suke matukar bukata daga garemu" Hawaye ya rinka kwaranya daga idanunta, ya mike tsaye cikin damuwa ya kamata suka shiga toilet "Ki Yi hakuri ki daina kukan nan haka, wanke fuskarki." Ya umurceta. Tayi abinda yace, suka dawo dakin, ya zaunar da ita a bakin gadon ta zuba tagumi, ya fita dakin, zuwa can ya dawo dauke da babban tray dauke da warmer da plates da kwalin mango juice dana fresh milk da cups ya dire a gabanta yace "Kinga ni yunwa nike ji tun rabuwarmu ban ci komi ba, sauko mu ci abincin." Bata musa ba saboda itama yunwar take ji, cikinta kamar an washe mata tas! Ta bude warmer din, gasashshen nama ne irin Wanda ba'a bari ruwan jikinsa ya kafe dinnan, sai kamshin kayan yaji, ga tumatur da albasa an yanka kanana, miyaunta ya tsinke tun kafin ta saka yanka daya baki,, ai tana taunawa Saida ta lumshe ido saboda dadin naman, Maggi da gishi sun kama radam... Kallon reaction dinta yake yana murmushin nan nasa, sai da yaga ta sake taunawa ta hadiye yace "Yaya, yayi dadi?" Ta gyada Kai "Don Allah a ina aka samo ne?" Ya girgiza Kai "Sai mun cinye za kiji." Ta zage taci naman nan har ta fi shi, ya zuba mata madarar ta shanye tayi gyatsa tayu hamdallah harda sude hannu. Suna karewa ta yunkura zata kwashe kayan, ya dakatar da ita da "No yau aikina ne, bari in Kai in dawo in baki labarin inda na samo naman." Ya fita ta bi bayansa da kallo tayi zugum. 'Anya wannan rawar jikin da Ya Haseeb keyi yau baids wata manufa can karkashin zuciyarsa kuwa? Ah to ta gane mana, cin nama banza ne da dare balle ga ango da amarya?" Ba'a jima ba aka dauke wutar lantarki sakamakon kakkarfar iskar data taso hade da saukar ruwa mai karfin gaske hade da tsawa mai firgitarwa, ga walkiya na gilmowa har ta cikin window dakinta.. Rahima ta tsorata ba shiri ta haye bisa gado ta kudundune kanta cikin pillow tana salati. Dakta ya dawo dauke da wata 'yar torchlight a hannu yana haskawa, yana shigowa ya maida kofa ya rufe, ya Kara tabbatar da duk windows ma rufe suke sai yan ragar da iska ke shigowa tunda ba kura, yace "Yanzun Malam Hassan zai kunna gen gidan yayi duhu ko?" Ba amsa, ya haska ya ganta a kudundune, ya karisa yace "Rahima mene kuma ke damunki yanzun?" Bata dago ba ta amsa "Wallahi Allah ya hakicce ni da tsoron tsawa sa wal .. bata karisa ba, aka buga wata tsawar ratsa--tsa-tsa...walkiyar ta gilmo cikin dakin, ta saki pillow ta cakumeshi ta rike gam tana makyarkyata... Dariya ta kama shi "Ni ban taba ganin matsoraciya irinki ba, maimakon ki rinka karanto adduoi sai ki rinka boye fuska?" Ta Kara cusa kanta a kirjinsa tace "Me zan karanta?" "Ya kwantar da ita tukunna ya fara rada mata "Cewa za kiyi *tsarki ya tabbata ga Allah Wanda tsawa take tsarkake shi da yabonsa da mala'iku don jin tsoronsa* A hankali ta rinka maimaitawa har taji tsoron ya gushe, to sai Kuma me? Sai fahimtar halinda take ciki, gaba daya jikinsu manne suke, kunya ta rufeta, ta nemi juyawa ya rada mata *Kin San hukuncin matar data juyawa miji baya ko* Bakinta ya mutu, magana ta gagara sabida yanayin data tsinci kanta ciki, jikinta yayi likis, kasala ta rufeta, tunda ya gane ta bada kai bori ya hau, daman ya riga ya hau tudu, gangara kawai yake nema, sun hade su n manne da juna, sun shiga rudani, gaba daya ji sukai tamkar basu taba wani rayuwar aure da kowa ba sai yanzun. Suna cikin yanayin ana ci gaba da zabga ruwan sama, tuni Rahima ta manta tsoron tsawa da walkiya, shi kuwa addua yake yana kara godewa Allah daya nufesa da auren daya daga cikin matan da ake Kira *SA'IDA* Lokacin da ruwan ya tsagaita barci ya rinka fisgarta ta rinka mashalo ita ba barci Mai nauyi na ita ba a farke ba yayinda ya rinka kallonta cike da so da kauna maras misaltuwa. Cikin dan barcin daya sure ta tayi mafarkin tana tsaye bisa wani tsauni tareda Haseeb da Rabi,'u, zuciyarta ta cika da murna da farin cikin ganinsa, ta matsa da hanzari domin ta kamo shi amma tana isa kusa yaja da baya, ta sake bin sa, ya tsaya ya riko hannunta ya matsa kusa da Haseeb shima ya rike hannunsa ya hada da nata ya manne yace "nagode daka rike amanar dana baka, ka rike matarka da kyau...ya juya gareta yace 'Ke Kuma ki bi mijinki zaku kasance cikin amintattun masoya da suka samu ingancin aure.. Mamaki ya hanata magana sai kokarin riko shi take yana ja baya har ya bace daga nan wani mashahurin haske ya lullubesu ita da Haseeb .. Ta farka babu inda jikinta bai kyarma saboda gigita, tunda ya rasu bata yi mafarkinsa ba sai yau, ta rumtse ido ta karanto *Allahumma innee a'uzu bika min sharri maa ra'ayta fee manaamee wala yadhuru nee fee deeni wa dunyayaa* Nan

Table of Contents

Chapters

66 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66