Chapter 35
Chapter 35
kallonsa ya shiga mota ya tafi. Sun dade ba tareda cewa juna kanzil ba, ta tuna gida zata tafi, ta juya tace 'Nagode, ta fara tafiya... Ya bita da kallo "Na yiwa Hajiya alkawarin kai ki so ki shiga mota mu tafi or are you ready for that kind of attention irin Wanda ya faru yanzun?" Cikin siriryar murya tace "Ni bani na kirashi ba.. "Ba zarginki nayi ba, mu tafi ko?" Tare suka shiga motar yaja suka isa cikin minti goma kacal. Motar na tsayawa ta bude kofar ta fito tace "Nagode a gaida su Aunty" Ya waigo "Magana nike dauke da ita ko kina jin barci gobe na dawo?" Ta girgiza Kai "Ba damuwa, mu shiga daga soro ko?" Ya fito ta rufe motar yana biye da ita, suna shiga tace "Zan amso key din dakin baki. Ta wuce cikin gida ta shaidawa Umman tana tareda bakone, Umman cikin farin ciki take wanda bai misaltuwa don ta gane waye ta Rahima ta kira bako. Har zata fita tace "Haka ake tarbon bakon ko ruwa ba zaki Kai masa ba balle lemu? Ban sanki da rowa ba Rahima." Ba tareda da tanka ba ta bude fridge ta dauko gorar ruwa da lemo da cup ta dora bisa faranti ta koma soron, Yana ganinta ya mika hannu ya amshi kayan ta bude kofar tace "Bismillah." Bayan sun shiga ciki ya ajiye farantin ya zauna kan kujera, Saida ta durkusa ta zuba lemun a cup ta ajiye sannan ta zauna gefen tabarma. Ya dan kurbi lemun kadan ya mayar ya ajiye yana kallonta ta cikin dark glasses dinsa yace "Ina Abdul dina ne ko har yayi barci?". Ta daga Kai "Ya riga yayi barci." Yace "Yaron dana san yana kai wajen sha daya bai kwanta ba sai anyi ta fama dashi?" Tace "Ban da yanzun kuwa ko don bai jin dadi ne oho." Ya bude baki cikin mamaki "Ya akayi ban sani ba, baki aiko min ba ko Hajiya?" Can kasa tace "Don naga ba it's not that serious.".. "Ya akayi kika San hakan?" Yai tambayar a fusace. Ta sunkuyar da Kai "An kai shi asibiti sunce malaria ne sun bada treatment shi yasa naga ba sai na aiko ba." Ya gyara zama "Daga yau karki sake min haka, duk abinda ya shafesa wajibi a sanar dani komin kankantarsa do you get me?" Ta daga kai alamar amsa. Ya kalleta sai Kuma ta bashi tausayi, ya sassauta murya yace "Look why not a daura auren nan this week mu ragewa kanmu jidali tunda Allah ya kaddaro mana haka, daman shawarar dana zo mu hadu mu yanke kenan. Mu ba yara bane, mun San ciwon kanmu naga zaifi dacewa ayi abinda iyaye keso zai fi mana sauki... Rahima tayi shiru yaci gaba "Ko Hajiya abinda ke damunta kenan saboda ta sanya abin a ranta." Ta dai kyalesa ya shirya mai yuwwa tana saurarensa yayi ya gama, ya mike zai tafi ya mika mata rafar kudi tareda tsadaddar handset. Cikin kwanaki uku kacal aka gama tsarawa da shirya komi. Daktan ya aika kayan aurensa akwatuna biyar, ya shaida mata ba zai ajiyesu gida daya da Zuwaira ba ya nemi amincewar yazo su tafi taga gidan da ya saya inda zai ajiyeta a dorayi, tace ba sai taje ba. Bata da niyyar yin kowanne irin shiri kan auren, Maryam tayi surutunta ta gaji ta kyale, ba tareda saninta ba sun shirya abinda ya dace game da gyaran gidan amarya sun Kuma nemi angon yasa an kaisu suka tsara shi yadda ya kamata amaryar data hadu a ga gidanta. Ranar da za'a daura aurensu tunda asubah aka nemi Daktan ya taimaka ya nufi Riyadh dubo maras lafiyan Nan, wannan karon ba gardama, aikinsa ceto rayuwar dake neman agajinsa da taimakon Allah in yai nufin patient din ya tashi, in Kuma lokacinsa yayi ba makawa. Yana gab da tashi ya kira Rahima ya bata hakurin rashin samun daman halatar daurin aurensu, tace ba komi Allah ya kai shi lafiya ya dawo dashi cikin amincinsa, tayi masa adduar Ubangiji ya bashi sa'a yayi nasaran shawo Kan ciwon da yai tafiyar dominsa. Karfe bakwai daidai na agogon Nigeria jirginsu ya daga suka nufi kasar Saudiyya kan hanyarsu ta isa babban birnin kasar Saudiyya, Riyadh. 10/09/2020, 22:44 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 26 Abin sha'awa iyaye, 'yanuwa, da abokan arziki ne suka tsaya aka daura auren Abdul-Haseeb da Rahima. Kafin ayi haka labari ya baza gari, jama'a suka shiga fadin albarkaci bakinsu wasu suka ce yaci amanar Rabiu, wasu suce daman can da kulalliya tsakaninsu, surutai dai gasu nan barkatai masu matukar daga hankali musamman ga wadanda abin ta shafa, da yake shi angon yai nisar kiwo sai damuwar ta tattara kan amaryar kadai daman cu cikinta take. Ta yini babu karsashi ba walwala ba wani kwalliya, bata gayyaci kowa ba hatta collegues dinta basu sani ba, to abu ya taras da miskillancin tsiya, ita Sam bata damu tayi kawa ba a tunaninta Maryam ce kawarta, aminiyarta Kuma 'yaruwa rabin jikinta. Umman da Maryam sunce ba za suyi taron buki tamkar ana zaman makoki ba don haka suka gayyaci dimbin jamaa bayan 'yanuwa wajen yinin bukin da suka shirya. Taro yayi kyau, an ci an sha an koshi, bayan azahar masu wa'azi suka dasa tasu nasihohin suka rinka fassara ayar Allah suna fassarawa. Suka fara da fadakarwa kan masu ganin auren wa ta auri matan kani jahilci ne suka yi kaca-kaca da masu kafa tsirku kan fadin Allah, suka dawo suka yiwa amarya nasiha kan hakkokin mijinta da suka rataya a kanta, suka hangaro na tarbiyyar diyanmu kana daga karshe suka rufe da matsalar data fi addaban Mata yanzun 'kishi' Wa'azine masu ratsa zuciya da shiga jiki ga wadanda keda sauran imani sun kudurta gyaran kurakurensu, ga wadanda suka yi nisa Kuma sai ido . Karfe biyar na la'asra Jamila da Haulatu suka jagoranci tawagar sauran matan kannin Daktan suka taho, a nan drama ta tashi Rahima na kiransu Aunty a matsayinki na matan wan mijinta, yau kuwa reshe ya juye da mujiya, ita ta koma Auntyn tasu a sabon matsayin da Allah ya bata matar babban Yaya. A can ainihin gidan Daktan uwargidan amarya ta gayyato kawayenta marasu mutunci sun cika gida makil, hatta 'yanuwanta komawa gefe suka yi suna kallonsu .. Kawayen sun gama zugata da bata shawarwarin da ba zasu amfaneta ba, harda shirya mata abinda zata yiwa amaryar don tasan ba wurin zamanta bane. Shashashar ma ashe bata san ma cewan ba gida daya zasu zauna ba, Saida ta aika gidan Hajiya a dubo ko tana can ne aka fada mata dorayi aka kaita. Ta dakawa Dan sakon tsawa "Dorayi wane gida? Jeka dubo min ka dawo yanzun." Suna ta yi mata famfo tana hauka cewan ai kamarta raunin hankaline ma ace mijinta yai mata kishiya ko wane dabiun kwarai take dasu da zai hana ayi mata oho. 12/09/2020, 13:05 - Anty saliha: 🦈🦈RAHIMA🦈🦈 28 Ta sauki mintoci heart beat bai koma normal ba, watau a takaice so da kaunar Ya Haseeb na neman mamaye mata ruhinta, ta girgiza Kai wannan ma ai shine abin kunyar, hhmmm da zai fahimci haka ya zai dauketa, maras tunani ko maras matunci? In kuwa hakane gara ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66