Chapter 52
Chapter 52
kaina ya dau zafi already." Ta sadda kanta kasa "Zuwa nayi in baka hakuri, don Allah da Annabinsa ka yafe min." Yace "Idan nayi hakurin na yau, sai kuma na yaushe, anjima, gobe ko jibi? Kuma ma hakurin me kike bani, mun riga mun saba, zaman auren kawai muke tamkar wasu jahilai." Ta muskutta "Ni dai nace ka yafe min ba don halina ba." "Me Kika yi da kike neman yafiyata, Ni a was Nike a rayuwarki don ban san matsayin da kika ajeni ba." Ta dago cikin hanzari "Ya zaka ce haka, matsayin mijina mana." Yace "To su Kuma abokan da kike dasu na waje matsayin me suke a gareki?" Ta fara kuka" Ni fa wallahi tallahi ban taba tarayya da kowanne namiji ba, wadanda muke huldar business dinmu kadai ne muke communicating dasu." "Ni ban tambayeki kuka ba, to su din kuma muharramanki ne? Zuwaira ki ji tsoron Allah, ki sani komin dadewarki a duniya Zaki tafi lahira, Allah zai tuhumeki abubuwan da kika aikata a duniya. To wai tsaya ma tun farkon aurenmu nasan ke din mace harija, duk kokarin sauke hakkinki ki kan nuna ke ba a gamsar dake ba, tun a nan na fara tausayinki, bayan wannan ke din nan fa ban aureki cikakkiyar mace ba, for whatever reason hakan ya kasance gareki ban sani ba, that's why ganin yadda kike huladarki da abokan naki yasa ni zargin. A wancan lokacin mutuncin dake tsakanina da mahaifinki yasa na share, na danne zuciyata har addua na rinka yi kar Allah yasa in rinka ganin bakinki ko rashin martabarki, ba don haka ba da tuni mutuncinki ya gama zubewa a idona, ke kinsan *virginity* darajar diya mace ce amma na ci gaba da zama dake da halayenki na rashin da'a amma kawaicina da hakuri bai sa kin gyara ba, sai kika kara shiga harkar kawaye masu zugaki kina shiririta, kina zaton ba don su Khalifa sunyi kama dani ba Zan karbesu ne a matsayin 'ya'yana? Nace idan ma halink ne yau da gobe bata bar komi ba ai. Daga nan saboda daurewa yawon gindi kika je kika daure mahaifa wai ke karki haihu ki tsufa da wuri, kika kara samun lasisin yawon. Kullum cikin nasiha nike a gareki amma ko a jikinki, Zuwaira ban rageki da komi ba, ba rashin abinci ba sutura, ba rashin kudin kashewa, iyayenki na kokarinsu a kanki to ashe duk ba muyi miki gwaninta ba, kince kina son ki nemi na kanki na mara miki baya don nima ban son tauye hakkinki, kuma no matter how much muke baki, is good ki nemi na kanki din saboda halin yau da gobe, but sai kika zake in the process, ke kinsan wanene ni, ni ba mazinaci ba ne, Allah ya kaddaro min auren Rahima kin kasa kwantar da hankalinki sai shirme da hauka kike wadanda ba zasu hanani komi ba balle su sani illa ma ki Kara zubda mutuncinki a idona. But ki sani kin kaini makura, saura kiris in dau matakin da zai baki mamaki." Tayi kasake tana saurarensa, to me ya fadi Wanda ba gaskiya ba? Babu, tayi tsumi ta muzanta, to ai shi daman komi kake aikatawa Allah na ganinka da lokacin da zai kama ka a hannu... Amma Allah ya sani da zuciya daya ta auri mijinta don tana matukar son abinta, amma ba a a nan gizo ke sakar ba, tun kafin ta auri Haseeb kawarta a boarding school ta fara bata ta in the process of lesbianism, ta saba a haka har suka gama school, sai kuma wani tsinannan saurayinta ya nemeta ba tare da sanin kowa ba, har iyayenta, tun kafin taga Haseeb. A gaskiya tafi danganta lalacewarta da wadannan mutum biyun da suka taka rawa wajen gurbacewar tarbiyyarta duk ta taso da shagwabar nata, iyayenta sunyi kokarin gyara tarbiyyarta ta fandare ita ala dole yar gata, kuma yan uwanta kaf ba haka suke ba.. Ta kalli mijinta da wutsiyar ido taga latsar wayarsa kawai tunda ya gama mata magana, in banda sharrin shaidan wace mace ce zata sami miji irinsa tayi mishi rikon sakainar kashi? Wallahi ko personality dinsa kadai ya ishi mace jin sha'awarsa balle a Kai ga kyawawan halayensa, ba domin shawarwarin da Husaina ke bata ba da tuni ta daina abubuwan da take yi ta rungumi mijinta, to amma ko yanzun lokaci bai kure ba, but Kashi! Inda zata sami cikas dayane, wannan auren da dauko. Sai dai kuwa ta kadata tayi gaba ta bar mata mijinta idan kuma taking fita za taga sharri kala-kala, ba zuwa wajen boka balle Malam, Zuwaira bata bin malamai duk iya shegenta, wannan sai Husaina. Tasa hanni ta shafi lallausar suman kansa "Kayi barci ne?" Ya wani dago kamar wace ta cije shi, "Menene Kuma?" "Na rokeka gafara ne banji kace ka yafe min ba ." Na yafe miki Zuwaira Allah ya yafe mana gaba daya amma ki roki gafarar Ubanginki kan zunuban da kika dauka da niyyar ba zaki sake aikata kwatankwacin su ba, idan kuwa kinsan ba zaki bari ba, no need ma kiyi istigfarin don Allah ba abokin wasan kowa bane, ai kin gane?" Tace "Wallahi har ga Allah ba zan sake ba, don Allah ka tayani addu'a. Yace "Kullum cikinta muke, muma ajizai ne Allah ya yafe mana dukkan kurakurenmu." Tace "Ameen.' Ya juya baya domin turaren data fesa hawa kansa yake, karfinsa yai yawa har ji yake kamat zaiyi amai." Ba da son ransa ba ya rinka tuna sansanyar kamshin turaren Rahima Wanda ya kama jikinta radam, turarenta har wani kashe jiki yake...bai gajiya da shakarsa.. Ta matsa kusa dashi ta shafa bayansa ta kira sunansa "Dakta? Ya amsa "Ni kuwa haihuwa nike so." Wata sabuwa inji yan caca! Ba tareda ya waigo ba yace ",To Ni ke bada haihuwar, da can Kuma nina hanaki? Ai kin fini sanin abinyi sai ki hada da addua.". Ta kwantar da kanta a jikinsa ta sassauta murya "Ka taba ganin mace ta haihu ita kadai, yaushe rabon daka kusance Ni?" Haseeb ya dafe Kai! Allah wadaran naka ya lalace, shi bai taba ganin mace maras kunya irin zuwaira ba, duk da ya saba da halinta na rashin iya danne maitarta, yau abin yai masa wani iri, ko don 'yan kwanakin da yayi da Rahima ne, yana son mace mai kunya, yana jin dadin yadda take jin nauyinsa, mace mace mai kunya abin so ce, duk yadda taso da bukata sai an kai ga rarrashinta ta bar mijin da rawar jikin, Kai Allah ya shiryi Zuwaira, abinda akace kunya na daga cikin yankin imani. Da taji ya Kyaleta ta kuma Kara rungumarsa tace "Kasan dai hakkina na kanka ba mai sauke min shi sai kai, kuma zaka rantse da Allah kwanaki ukun da kayi a wancan gidan haka kayi salin alin ba abinda ya wakana tsakaninku sai Ni don na nemi hakkina ka ja min rai?" Cikin deadly voice yace "Nayi warning dinki daga yau idan zaki magana karki sake kawo min batun Rahima.. Ta marairaice ta narke a jikinsa "Afwaan ba zan sake ba. " Ya dago ya kalleta tun daga sama har kasa yaji shi kansa kyamar kansa yake ji but wajibi sauke nauyinta da Allah ya dora a kansa, ya tashi zaune
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66