Chapter 40
Chapter 40
suma suka bi suka kwanta ya gama shirunsa tsaf ya juya ya kalli Zuwaira dake zaune gefen gado yace "Ni zan tafi ba wani abu?" Ta kallesa ta watsar bata tanka ba. Yai ajiyar zuciya ya mike tsam ya nufi kofa kafin ya isa ta rigashi ta taresa "Kana nufin can Dorayi zaka tafi yanzun ka kwana can?" Ya kura mata ido ta cikin glass dinsa yace "Me kike so inyi miki ne Zuwaira,tunda na shigo gidan nan kike neman ffitina, me kike so?" Ta Kara tare kofa "Me nake so? Ya za kayi min wannan shegiyar tambayar bayan wani gida kayi niyyar tafiya ka kwana, bani da right da zan tuhumeka?" Ya girgiza Kai "Ki tuhumeni for what reason? Look Zuwaira ki gane addini yaba magidanci damar sauka duk inda yaso in ya dawo daga tafiya in har ya mallaki mace fiye da daya, amma ga mai son kyautatawa sai ya sauka wajen uwargidansa ko wace take da girki a ranar, a al'adance. To ke na kyautata miki, na dawo na sauka a nan,tsawon lokacin dana dauka tare dake kika nuna tamkar baki san daga inda na fito ba, babu maraban arziki balle nuna jin dadi da hamdallah ga Allah cewan naje na dawo lafiya, banyi fushi ba na zauna tare dake har zuwa yanzun duba time karfe nawa ne, sai kuma zan fita ki taso ki dasa min wasu tambayoyin da basu dace ba? Me ma kike nufin da wai can zan kwana? To yes can zan kwana, idan kin manta ne in tuna miki yanzu ku biyu na mallaka matsayin mata ne, hakkin Rahima ma ya rayata a kaina yadda naki hakkin yake a kaina, wajibi ne in sauke nauyin da Allsh ya dora min nata, tunda an daura ba na Nan, kwana uku zanyi a gidanta, kana in dawo ku ci gaba da raba kwana yadda kuke so wace ban kwana gidanta ba wajibi in lekata da safe don ganin lafiyarta, Ina fatar kin fahimceni, bani hanya in wuce." Wai saita saka kukan kissa ta kama shi gam ta rike "Sabida Allah nu kadai zaka barni in kwana cikin katon gidan nan?" Ya girgiza Kai "Yau aka fara hakan? Idan ban barki kin kwana ke kadai ba ai ke kya barni ki tafi balaguronki ko, to meye na damuwa yau keda kike alla-alla ki samu kafar yawo?" Taci gaba da kuka wanda a zahiri tana yine don bata masa lokaci, ya dago manufarta, ya yakiceta ya raba daga gefenta ya fita, ta bisa har waje yayinda direbansa ya taso ya bude masa mota, yace Mata "Saida safe." Ya shige mota abinsa suka tafi. 13/09/2020, 23:21 - Anty saliha: ...ˆRAHIMA..doc by jami 31 Mal. Hassan ya dagewa direba murfin gate ya wuce harabar da aka tanada domin aje motocin. Uwale ce ta fara hango Maigidan ta tagar kicin yana gaisawa dasu Mal. Hassan bayan fitowarsa daga mota, direban ya bude boot yana fito da kayan dake ciki suka fara shiga dasu cikin gida. Rahima na can cikin bedroom dinta bata San bidirin da ake yi ba, kwance take rigingine ta kifa littafin da tsananin tunani ya hana mata karantawa a fuskarta kamar tana barci, zurfin tunanin da take yi ya hana jin sallamar da Dr Haseeb yayi. Ya dauka barci take ya Kara sallama har sau uku bata motsa ba, ya matsa ya shiga cikin dakin, taushin rug din ya hana mata jin takunsa, saida ya kai daf da gadon da take kwance, yaji sautin wata waka dake fita a wayarta, ta wasu samari da su Kai masa suna *I don't care who you're* Ya tsaya bisa kanta yai mata kallon tsaf cikin dakikoki...... Jikinta ya bata lalle ana kallonta, daidai lokacin ya duka ya kai hannunsa ya cire book din data kare fuskarta, daidai lokacin suka shaki kamshin juna, Rahima ta kai hannunta zata cire book din, already nasa hannun ya sauka a kafadarta. Ganin wanda yake tsaye kanta ta yunkuro ta tashi zaune a tsorace. Ba tareda yayi magana ba ya maidata kwance ganin yadda ta razana, tana ta kokarin fahimtar what's happening is real ba mafarki ne ba, tayi kokarin magana but shock ya hanata, shima a kidime yake don da za a auna jininsa a lokacin za a ga ya hau saboda bugun da zuciyarsa keyi very fast. Ya gyara muryar da zama very low yace "Sorry I didn't mean to scare you.' Ta saki ajiyar zuciya yayinda ta sake yunkurin tashi ta zamo kafafunta yaja da baya kadan still yana kallonta, ta cije tace "Sannu da zuwa, afwaan ban ji shigowarka ba, ya hanya?" Ya amsa "Alhamdulillah ya gida? Idanuwansa na kanta ya lura da kananan kitson da aka tsarawa sumanta da suka sauka har bayan keyarta kafin ta lalubi dankwalinta ta rufe kanta. Yana tsaye yana ci gaba da yi mata kallon kurilla harta mike ta gyara rigarta ta lalubi mayafi ta rufa kana ta fara kame-kame tace "Abinci na can dining ko sai kayi Sallah ka huta tukunna?" Ya bi da kallo ya share tambayar bai amsa ba saboda ya fahimci so tayi ya juya ya bar badroom din shi Kuma kamshin dake fita a hankali ya haifar masa da wani irin natsuwar da yasa yaji yana son zama cikinsa. Amma tunda yaga a rude take, bari ya hakura har ta samu natsuwa. Ya kalleta "Zan shiga dakina for now inada wasu calls before magrib." Rahima ta nufi kicin ta taradda Uwale da Haladu nata shirya kayayakin da ya taho dasu, sun aje komi a mazaunin da ya dace, suna gamawa Uwalen tace "Hajiya zamu sake dafa wani abincin ne?" Ta kada Kai "Ah wadanda muka yi suna cikin warmers ai ba abinda suka yi." "To ke fa? Naga kina son tuwo har na dora ruwan zafi?" Ta girgiza Kai "Ba Zan ci ba gaskiya sai dai ko ke, amma nagode da kokari." Uwale ta dafa cikinta "Ai nima din a koshen nike alhamdulillah." Rahima tace Shikenan "Zan shiga inyi sallar magrib sai anjima kenan." Ta bude baki "Saida safe dai Hajiya, maigida ya dawo wane hira za muyi yau?" Ta girgiza Kai "Uwale kina son shige mun hanci amma zan fyato ki." Tayi saurin durkusawa "Wace Ni uwar dakina, yafe min, amma kinsan gaskiya na Fadi." Ta shiga tana dariya "Hhhmm naso in ganki da kuriyarki Uwale, kin cika ban dariya. Wasu masu shigowa gidan Rahima suna korafin wai tana sakewa da 'yar aikinta da yawa, ita kuwa mace ce mai ba kowanne irin mutum darajarsa, ta Kan dauki kanta ita ba wata tsiya bace, bata wulakanta na kasa da ita saboda sanin kowacce halitta da irin darajar da Allah yai Mata, tsakaninta da masu aikin gidanta,, mutunci ne da girmama juna. Ta dade da idar da sallar isha'i amma ta kasa tashi daga sallayarta. Kamar yadda yaji kamshin dakinta hakan ya cika nashi dakin tun daga falonsa zuwa bedroom, komi ya Burgesa, tsarin yai masa daidai. Hhhmmm ya kasa zama sai tunani, shi bai ma san yadda zai bullowa wannan auren nasu ba duk da ya rungumi auren nan da hannu biyu. To ai ba nan gizo ke sakar ba, ganin irin dari-darin da ta fara yi dashi, to ai shi din ma bai saki jiki da ita
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66