Chapter 55
Chapter 55
batun kyauta ta." Maganganunsa sun sa kunyarsa ta dawo mata sabuwa ta rufe idanunta, ya banbare da kyar. Cikin shagaba tace "Don Allah ka rabu dani.". Yace "Ai kuwa baki isa ba, alkawari ki kai min wajibi ki cika sa." Tace "To me kake so?" Ya amsa "Sai kin kalleni zan fada miki." Tana kallonsa yace *Yourself* Hhhmmm wai don Allah da gaske ne da mutane ke cewa yawancin Doctors maza basa jin kunyar fadar magana? Saboda ita ga nata likitan nan Yana ta rikita mata kwanya da surutan da ko a mafarki bata yi zaton zai iya Fadi ba. Dr Haseeb da Rahima sun ci gaba da gudanar da rayuwar aurensu gwanin sha'awa, aka bar masu fadin ya za ayi wa ya auri matar kaninsa baki ya mutu sai sha'awar su suke. Sati biyu cif Dakta ya tabbatar da warkewar patient dinsa Hjy Fatima don haka ya rubuta musu sallama. Da kansa ya daukesu zuwa gidansa suka kwana guda sannan suka koma Maiduguri. Ba su tafi ba Saida suka tabbatar zumunci Mai karfi ya kullu tsakaninsu tareda da alkawarin ziyarar su day zaran ya samu sarari inji likitan, sun rabu suna begen junan Hutun da Rahima ta dauka ya kare sai batun komawa aiki, Daktan ya daka tsalle waje guda yace ba zata sabu ba Wai bindiga a ruwa, yadda ta shagwaba shi yana bukatar attention dinta sosai amma yace ta nemi sana'ar da zata yi don bai son ta zauna hannu sake tana jiran kullum sai anyi Mata. Ta nemi shawarar iyayenta suka amince, ita da 'yaruwarta Maryam suka hada jari suka aikawa Hjy Fatima ta fara turo musu turarukan wuta, na jiki, dana tufafi, har dasu lapayya. A sannu Ubangiji yasa musu albarka, kasuwanci ya habaka ya karbu wajen matan manya sai hamdala. Kwatsam Zuwaira ta tada fitinar sai dai a hade su gida daya saboda kullum cikin zargin mijinsu na mata rashin adalci take, kuma wai ma Rahimar bin malamai take a nata tunanin ba haka kawai miji ke rawar jiki da ita ba. 18/09/2020, 19:13 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 45 Tun daga Kan Hjy Kaltume, Maryam da Iyayenta babu wanda ya bata goyon bayan ta amince da bukatar Zuwaira ba balle shi kansa uban gayyar da yace duk abinda zata ce taje ta dade bata ba amma bai yarda tsarin ba sam. Rahima tace a bata kwana bakwai tayi istikhara ta roki Allah zabi tukunna. Sarai yasan halin gimbiyar tasa don haka yace Kar ma ta san ran zai canza ra'ayinsa ya riga ya yanke shawara. Ba Rahima bata amince da shawarwarin da aka bata bane, no bata san abinda gaba zata haifar ba, zaman nasu khairi ne ko sharri Allah kadai yasan gaibu, dalilinta kenan na dagewa tayi adduar saboda zuciyarta ta kasa tsayuwa waje guda. Bayan satin taji ta natsu ta amince da batun hadasu din sai dai ta dage da adduar neman tsari daga dukkan sharri da fitinar dare da rana. Tana tunkarar maigidan da maganar yai tsalle yace ba zai taba hadasu ba, ta kafe kan ra'ayinta ya kafe kan nasa taron taurin kai. Ranar tana zaune taji sallamar su Umma da Hjy Kaltume Daktan na biye dasu ta girgiza Kai ta tabbatar shi ya dauko su kan batun nan da yaki ci yaki cinyewa. Bayan ta gaishesu ta kawo musu abin motsa baki, bata bari sun fara magana ta tambayesu "Yaya karata ya kai ko?" Hajiya Kaltume ta gyada kai "Har yanzun kaina a daure yake Rahima, na rasa dalilin da yasa kike son dauko fitina da hannunki ki kawi cikin gidanki, me ye zafi haka? Ta sunkuyar da kai "Hajiya baku fahimce nu bane shiyasa kuke tunanin hakan." "Ina fa zamu fahimceki tunda ba muyi wayo da hankalinki ba." Ummanta ta fadi a fusace. Ta kalleta a raunane "Afwaan Umma haka nike nufi ba." Hajiya ta kalli Umma "Saurara mata tayi Mana bayani watakila ta fi mu gaskiya.". Sai a nan Haseeb ya tanka yace "In dai itace yanzun zata kashe miki jiki da lafuzanta ki amince da manufarta ko banza ba Kya ganin laifinta." Rahima ta kallesa "Shikenan Yaya bari in musu bayani idan basu amince ba wallahi na hakura, amma kafin nan ka fadu hujjojinka na rashin son hadamu din." Ya gyara zama "Hujjoji?, Halayyen Zuwaira ai ba boye suke ba, kuna nesa da juna ma ban tsira da korafinta na Ina rashin adalci tsakaninku ba, fitinar yau daban ta gobe daban Wanda da ina biye mata da tuni mun rabu." Rahima tace " Kuna jinsa ko? To ai ni abinda ban son ya faru kenan, da can din ai da halinta baka rabu da ita ba sai bayan aurena? Ko Ni ce zanyi zargin dalilin wata ka rabu dani, daga nan Kuma kulalliyar gaba ta kullu tsakanina da yaranka har abada saboda mai zurfin tunani ne zai gane cewan gajiya kayi da halinta ka Kai makura ne silar rabuwarku, batun danne hakkinta da take yi ma zaman mu a tare zai sa ta gani idan ana zaluntarta din, Kai kuma za a rage maka yawan zirga-zirga tunda iyakinka na natse waje daya hankalinka zai fi kwanciya." Umma ta daka mata harara "Ai ba dai iya magana ba 'yar ka iya, shi ba wadannan matsalolin suka dame sa ba." Yace "Ta fa san duk abinda nike gudu Umma." Hajiya tace "Rahima zaki iya zama da Zuwaira da halayyenta?" Ta gyara zama tace "Sai maganar halayye muke Hajiya amma bamu tsaya munyi nazarin shin wane irin hali Aunty Zuwaira ke dashi ba kamar yadda masu ilmin sanin halayyan dan Adam suka kasa halayyen mutum har kashi uku. Na farko akwai halayyen da basu gyaruwa kwata-kwata, misali irin halayyen da mutum ya gada daga iyaye ko aka haifesa dasu, to kowa yasan halayen Aunty Zuwaira ba gado ba ne don kowa ya shaidi martabatar iyayenta da sauran zuriyyarsu, ba kuma wadanda aka haifeta dasu bane. Na biyu shine halayyen mutum da ake iya gyarawa Amma sai an Sha wahala sosai wajen yin gyaran, irin wadannan halayyen mutum kan tsiri yinsu ne a kan da dole ma'ana wani dalili ya tilasta wajen adopting canza original halinda aka san mutum dashi. Misali irin yanzun da yawancin maza kan bar wa mace takakihun hidimar gida, yau da gobe darajar sa na iya zubewa a idonta, ta daina ganin girmansa sabanin yadda take mutuntashi da can. Na uku mutum Kan dauki halayyan da ba nasa ba da rana tsaka ko dalilin hulda da abokan banza, ko haka kawai ya halin wani ya rinka burgesa, irin wadannan gyara kawai suke bukata ba kuma za a wahala wajen gyarawan ba. Ya kada kai yace "To munji mai falsafa cikin wadannan kashin da kika zano da wanne kika danganta Zuwaira dashi har kike shaawar zamanku tare? Kenan kina ganin zaki iya gyara halayyenta? Rahima ta nisa "Sanin gaibu sai Lillahi, Ina adduar sanadiyyar zaman tare ta canza halayen nata." Hjy Kaltume tace "Da kyau Rahima haka ake son musulmin kwarai ya sowa kansa abinda yake so wa kansa, kin burgeni." Umma tace "Hakane Hajiya nima banki naki ba, tashin hankaline nike gudu." Rahima tayi murmushi "Kamar kin manta da halin diyar taki Umma, fitina ta kan kare ne Kan Wanda ya jawota, Ni dai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66