Chapter 30
Chapter 30
Yana zuwa ya durkusa gaida Alhajin amma ya mika masa hannu su gaisa, ya dan tsaya saboda jin nauyi, Alh. Muhammad ya riko hannunsa Yana dariya, ya tambayi sunansa ya fada masa, ya sake tambayar dalilinsa na yawo da littafai Yana aiki ya bashi amsa da "Ina neman na kaina ne." Ya sake tambayarsa wanene mahaifinsa ya fada, nan da Nan ya gane don shi din sanannan mutum ne, Alh Muhd yai mamakin jin sunan mahaifinsa da yadda ya bar dansa na kwadigo bayan Allah yai masa rufun asirin da zai taimaki wani ma ba dansa kadai ba. Yana son jun ainihin tarihin yaron nan don haka ya mika masa katinsa yace ta samesa a gidansa a ranar, ya karba yana mamakinsa dalilin da yasa yake son ganinsa tareda alkawarin zuwa da dare. Karfe takwas na dareya isa gidan Alh Muhammad, da alamun an bada labarin zuwansa domin yadda maigadi ya tarbesa yai masa jagora har falon maigidan. Alh. Ya mike ya sake Mika masa hannu suka gaisa kana ya bashi umurnin ya zauna ya zabi abinda zai ci cikin nau'ikan abincin da aka baza a tsakiyar falon. Yasha lemu kawai yace ya koshi, Alh ya jima yana kallon yaron da ya shiga zuciyarsa farad daya ki domin baida da namijine ohom. Yaso yaji dukkan labarinsa but Abdul Haseeb ba haka yake ba, bayan miskillanci yanada rike sirrinsa domin ba ayi ciki don tuwo kadai ba, to ma haka kawai ne daga haduwa da mutum bai San kowanne irine bane zai zayyane masa sirrinsa, no bai san abinda zaije ya komo ba, bai san me mutumin ke nufi dashi ba. Alh Muhd ya tabbatar da ba zai Kara jin komi daga bakin bakonsa ba ya hakura ba don ya gamsu ba sabida har zuwa lokacin Yana mamakin uban da zai samu hazikin yaro kamilalle irin Haseeb yai biris da al'amarin neman ilminsa, da daure kai sosai amma tunda yaron ya dage kan cewan Yana kwadagon don ya taimaki kansa ne ya kyalesa a haka yai masa taimakon da zai iya yi masa. 09/09/2020, 23:56 - Anty saliha: ..ˆRAHIMA ...doc by jami 22 A ranar yaiwa Haseeb albishir din cewan saboda ya yaba dashi matuka gaya zai taimaka masa Kan harkar neman ilminsa tun daga kasarmu zuwa kasashen ketare har ya cimma burinsa. Yace Yana son ya dau masa alkawarin zai amince ya zama dansa saboda shi bai taba haihuwar da namiji ba, 'ya'yansa takwas duk matane. Bai yi saurin amincewan ba ya nemi ya bashi kwanaki uku yaje yai shawara tukunna, Alh.Muhd ya amince ya kawo kudi ya bashi yace yai kudin mota. Ya amsa yai godiya ya tafi. A ranar ya sallama gidan mijin mahaifiyarsa Yana kiransa Baffa, ya shaida musu duk abinda ya faru, Kaltume ta tsaya shiru ta rasa ta cewa, maigidanta yace mishi "Kaje ka amshi taimakon nan da hannu biyu ka rikesa da zuciya guda bisa amana tareda adduar Allah ya taimakeka bukatarka ta biya." Kaltume ta nisa "Anya? Ina jinjina batun mutumin nan Malam, kana ganin za'a kwashe lafiya, ka fa san halin mutanen zamanin nan na mu." Mal. Sunusi yace "Insha Allah na komi, Ubangiji fa ba yadda bai iya tsara al'amarinsa ba, idan cikin hikima da basirarsa ya kaddaro Alh. Muhammadu ya taimaki yaron nan ba makawa, ai shine kaddarar, zaki ga wani mutumin ba ko a mafarki tunani bai taba kaika cewan zaku hadu ba sai kwatsam Allah ya hadaku a shiga cin gajiyar juna. Kai dai har kullum gargadina gareku shine Wanda duk Allah ya hadaku dasu ku zauna dasu tsakani da Allah da zuciya daya, banda hassada ko kyashi, Banda biyewa zuciya ko mutanen duniya 'yan Kai kawo su shiga tsakaninku, banda daukar jita-jita. Ka sani daukaka Allah ke yiwa mutum ba kowa ba, idan ya so ka daukaka iya hassadar makiya basu isa su hana ba, kazalika in baiyi nufu ba ba Wanda ya isa ya kaika inda Allah bai Kai ka ba. Banda wulakanta mutum da kowacce irin halitta, banda kwadayi don yana janyowa mutum wulakanci da kaskanci, kayi imanin komi ya same ka cikin rayuwarka rubutacce ne daga Allah, wani ko wata, mutum da aljan basu isa suyi maka abinda ba Allah ya rubuto zai faru dakai cikin *Lauhul Mahfuz* ba. Ka riki gaskiya duk inda ka tsinci kanka cikin kowanne yanayi, Ina gargadinka daka rike addininka hannu biyu, ko da Allah zai daukaka nan gaba ta azurtaka karka butulce masa son duniya ya shagaltar dakai bauta masa gwargwadon iyawarka... Ka rike mutumin daya taimakeka da hannu biyu, ko da ace baiyi maka komi ba kaunar daya nuna maka ta isa domin duk Wanda ya kaunaceka irin haka, ba don wani Abu naka ba sai domin Allah ya gama maka komi, karka sake samun duniya ma'ana dukiya ta hadaka dashi, Kar ka zame masa mutum mugun icce. Da wadannan nasihohi masu mugun shiga jiki Abdul-Haseeb da mahaifiyarsa suka yi na'am da Alh. Muhd. Shi kuma can ya kosa yaron ya dawo yaji ta bakinsa domin har ya nemi alfarmar gwamna cewan yana da d'a idan mai girma gwamna zai tura hazikan dalibai karatu kasashen waje a saka sunansa. Gwamna ya amsa da alkawarin idan lokaci yayi nan da watanni uku zai sanar dashi. Lokacin da Abdul Haseeb ya koma gidan Alh Haseeb kansa ya daure, an nuna masa ya riga ya zama dan gida, kowa sai ji dashi yake kamar daman a gidan yake tafiya yayi ya dawo, hidimomi salamu Alaikum. Kaltume da maigidanta musamman Abdul Haseeb ya kaisu yi masa godiya shi da iyalinsa. Kafin watanni ukun Alh Muhd yaja Haseeb a jikinsa sosai ya Kuma bashi labarinsa tas, shima yace ya taso cikin wahala sakamakon iyayensa sun rasu tun Yana karami amma daga dangin uwa har na uba aka rasa Mai daukar nauyin karatunsa, nan ya shiga neman abinda zai hucewa kansa takaici, ya fara da yiwa wani attajiri kiwon doki, ya kanje ya yanko ciyawa ya share turkensa ya kula da dawakin ana biyansa, daga nan ya koma sayar da sigari, da goro, minti ashana da sauran tarkacce a tire a tashar mota, daga nan Allsh ta tarfawa garinsa nono,ya kafa dan tebur daga nan sai shagon kayan masarufi, daga nan Allah ya daga shi sannu-sannu ya fara kwangila tareda taimakon Allah, Ubangiji ya daga har ya Kai matsayin da yake ciki yanzun. Ya auri mata uku bai Sami haihuwa da wuri ba, da ya samun sai Allah ya azurta shi da diya Mata. Alkawarin da yayi suna gama sakandire zai aurad dasu, Amma duk ranar da Allah ya bashi d'a namiji sai inda karfinsa ya kare.. Zuwaira ce diyarsa ta biyu, Mai bala'in kama dashi saboda hakane yake sonta kwarai da gaske, irin son da ya janyo mata sangarcewar. A lokacin da ya hadu da Haseeb duk suna makaranta, Zuwaira na aji uku kacal. Duk wani takalihunsa ya koma hannun Alh Muhd, duk da haka bai saki jiki ya daina buga-bugan sa ba. A hankali ya fara koyon hanyoyin kasuwanci ya rinka aiwatar da abinda ya saukaka a garesa. Yayin da gwamnatin jihar Kanota dauki nauyin fitarsu zuwa kasar *Neatherlands* domin zama kwararren likita. Abdul Haseeb ya zama *Neurologist* ya zamewa uwa da uba dashi kansa Alh Muhd din d'a daya tamkar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66