Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 62

Chapter 62

Rahima Book 1 Complete Hausa Novel 1,207 words 0 views Progress saved
Download Book

Shafa'atu ta shigo gaisheta suna hira Zuwaira ta damu ta shiga Ina ka saka da kanwar nata don tunda suka shirya haka suke kaffa-kaffa da kulawa da juna musamman idan rashin lafiya ya shigo. Kasancewar Rahimar ce da aiki Zuwaira ta shigo sashenta ta tambayeta abinda zata dafawa maigidan tunda ita tana kwance. Tace Aunty akwai time table na nau'ikan abincin da muke dafawa kowacce rana Uwale ta nuna miki ko ki dafa duk abinda kika ga ya kamata, nagode." Zuwaira tayi dariya "Godiya Kuma tsakaninmu kanwata, in dai lalura ce yau gareka ne gobe ga danuwanka balle ance ko baka iya alkhairi ba ka yiwa mai maka, ni so nawa kika shigo Kika taimaka mini? Fatanmu dai Allah yasa murar alkhairi ce." Sallamar su Maryam yasa Rahima ta dafe kai tace "Aunty ga 'yan baka nan don Allah karki maimaita batun nan a gabanta." "Yaushe Kuma ai na riga naji, Hjy Zuwaira Allah ya amsa harda nan bangaren don naga sai wani sisi kike yara sun dade da zama samari." Zuwaira tayi dariya "Marhabin sannunku da zuwa, Aunty Maryam karki ga laifinmu a nan tuhumi Dakta, may be tsufa ne ta fara aikinta." Maryam da kawarta Ummul khair suka shiga ciki Zuwaira ta bisu aka gaisa kana tace "Komin tsufansa idan ba zaku tabuka ba sai mu sake darzo masa amarya.". Rahima tayi murmushi "Yo ta taho mana wa ke tsoronta?" Ummulkhair tace "Ai tsoron ba naku bane nata ne don duk wace tace zata shigo cikinku gaskiya sunanta sorry.' Maryam tace "Tabbas zamanku na burgeni, Allah ya Kara hada kanku." Zuwaira ta amsa "Ameen Bari in shiga kicin in dawo." Ummulkhair ta rike baki "Oh ina ma ace gidanmu ya dawo irin naku? Rahima tace "Wai har yanzun babu canji a yanayin zamanku?" Ta girgiza kai "Ai Rahima yanzun ne ma gidan ke Shirin zama sansanin fada sabida ga goron amaryarmu ta hudu na kawo muku." Rahima tace "Ikon Allah! Duk kwasar karar mahaukaciyar da akeyi a gidansa bai isa ba sai ya karo wata masifar?" Shafa'atu tace "Namiji ne fa,? Ai sun fi son su tara ayita bala'i da masifa a kansu." Maryam ta gyada Kai "Wannan idan Allah bai sa kun fahimci rashin alfanun rashin zaman lafiyar ba kenan. Muddin kuka yi hakuri da juna sai ku sami salama da kwanciyar hankali.". Ummukhair ta gyara "Dace da irin wadannan kishiyoyin da zasu fahumci zaman lafiyar yafi zama Dan sarki, su fahimci arziki bai samuwa saida hakuri Abu ne mai wuyan gaske a zamanin nan da muke ciki. Idan ba a samu mai shurin shigowa ra fishsheki ta tsigeki cikin yaranki ba za a samu Mai cewa ki shigo din ki gane kurenki tunda kin auri mijinta, sai kace kowanne namiji an lika masa lambar zama da mace guda ne a goshinsa, ku dai kunyi dace da kishiyoyin." Daidai Zuwaira ta leko tace " Hmmmm all the credit goes to Rahima, tambayeta ta baki sirrin." Tana juyawa Ummul khair ta kalleta "Da gaske?" Rahima ta danyi murmushi "Fada kawai take yi, yes ba shakka mun dan fuskanci problem tsakaninmu amma hakuri, kau da Kai, dogaro da kai wajen samun sana'ar da zata hana maka bata lokacinka kan al'amurran kishi, kyautatawa juna, girmama juna, tarbiyyar yaranmu tafarkin gaskiya, sanin hakkokin junanmu da yadda zamu sauke hakkin, danne zuciya daga saurin fushi, toshe kunnuwanmu daga kunji-kunji, rashin ganin kyashi da hassadar junanmu, tsayawa a matsayin da Allah ya ajemu, kyautata ibadarmu wajen bautar Ubangijinmu da mika dukkan al'amurranmu garesa suka shafe komi, suka kawar mana da dukkan fitunu dake tasowa ya mamaye cikin gida, sai kyautatawa shi kansa uban tafiyar Wanda sirri ne don kowacce da nata salon." Ummulkhair ta jinjina tace "A gaisheku da kokari, ko a nan kinga hannu guda ba zai dauki daki ba, Ni kadai ba zan ita gyaran al'amurran gidanmu muddin ba mataimaki." Rahima tace "Wajibi wata ciki tafi hakurin da kau da Kai saboda Allah bai halicci zuciyarmu iri daya ba, haka zurfin tunani da hangen nesa ba zai zo daya ba, abunda wata zata dauka a shekara wata ko na minti gudan ba zata iya dauka ba, to ana son idan an hadaku ita mai zafi ce ke sai ki yayyafawa kanki ruwan sanyi, tayi masifarta ta gaji baki tanka ba balle ku zama daya, ba Kuma za kiyi shirun don tsoro bane, no zaki nuna mata ke tarbiyyarki ta daban ce, sai ta gaji ta bari yau da gobe don kinsan akwai ciwo mutum ya takaleka baka kulashi ba." Ta gyara zama "Kin dai San mu uku ne, Ni ce karama, dukkanmu muna da Yara, na Uwargida sune mata manya sun girma sun isa aure, amma saboda mugun tarbiyyar da uwarsu tayi musu gaisuwa ta fatar baki bai hadani dasu dai dai kuji suna wake-wake da habaici har da zage-zage wata ran wai dani suke, in hanya ta hadamu su nemi bangajeni suce idan na isa in taka su karya banza.. "Tafdijan! Inji Shafa'atu me ya hana ki lallasata ki barta kwance ba kiga wa ya tsaya musu?" "Uwarsu mana tunda ita ke turosu suyi rashin mutunci, ai na taba daukar mataki na dake su da suka kaini makura sai uwarsu tazo taci dammara tace da ita zanyi itace kishiyata ba su ba, suka taso za suyi min taron dangi suka ga ba zasu ci riba ba don ba zan dau rainin da rashin kunyar da suke yiwa ta biyun mu ba sai suka canza salon rashin mutunci,idan nayi abinci babu mai ci, yarana cikin duka da kyara kullum, babu mai daukar musu, ko ciwo suke yi babu mai lekowa yace musu sannu daga su har uwar, ita wancan ce da suke yiwa cin Kashi ta kan Dan leko. Ga sata ga keta, komi na ajiye a sace, su bata na batawa su zubar da wasu, kullum Ni kenan boyon tarkace, ko wanke tufafina dana Yara nayi wajibi gareni in girke kujera in zauna jiran su bushe in kwashe karsu sa reza su kekketa min. Da suka ga ban nuna damuwa ba sai suka zuba min gishiri ko suka zunduma min ruwa yafi karfin sanwata,,sai su aza tukunya su dora wani su ci su koshi, ko su fita su sayo wani suci su koshi." Maryam tace ",To shi maigidan yana Ina ake badakala haka cikin gidansa?. Rahima tace ga abin damuwa nan gurbata tarbiyyar diya mata, ita wace irin uwace da zata saka 'ya'yanta mata a harkar kishi? Me take koyar dasu kenan, Shi Kuma uban ya Kyaleta tana la'anta tarbiyyar yaransa?" Tace "Ya Zama mijin tace ai. Ba ya iya kwabon yayansa Sam, nida nike kokarin kwabawa sunce na cika tsanani ne, nace a tafi haka. Kwanaki yaran nan suka shirya makurcin da Saida ya sakeni, ban San hawa da sauka ya shigo Yanata masifar wai na hana yayanshi abinci Wai bai auro matar da zata hanasu abinci ba, don ma na samu suna cin girkin nawa da ban iya ba? Har da cewa zai ita rabuwa da kowacce mace kan yayansa. Ban San dalilin masifarsa ba, ashe Wai sunce masa bana dafa u Isashshen abinci ranar girkina alhalin bai mana iyaka da store ba.Ba bincike ya shiga tsiya, Ni kuma zuciya ta kawo min wuya ba bata lokaci na

Table of Contents

Chapters

66 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66