Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 45

Chapter 45

Rahima Book 1 Complete Hausa Novel 1,212 words 0 views Progress saved
Download Book

cikin zafin naman nan nasa "Ki dai tayamu addua please, sai na dawo." Zuwa karfe 12: am Dr Haseeb da sauran likitoci hudun da yake jagoranta sunyi nisa da binciken kwakwalwar patient din, sun Kara daukar awa uku cur kafin su ciwo kan problem din a inda ya yanke shawarar ba sai yayi mata surgery ba, abubuwan da suka yi mata zai taimaka jinin ya rinka gangarowa ta hancinta ana zukewa har yayi clearing. Bayan nurses sun Kai patient din dakin jinyar kuma ya shiga ya dafa kanta ya dade yana karanto adduoin samun shifaa gareta, wannan al'adarsa ce ga patients din sa Kuma Ubangiji na amsar adduoinsa yasa a samu waraka ko da an yanke teammanin samun waraka. Mijin maras lafiyar ya rasa irin godiyar da zai yiwa Dr Haseeb tunda ya shaida masa she's out of danger. Kwarai Alh.Ahmad Sharif ya yaba da kwazon gwarzon likitan musamman ganin irin dedication dinsa kan aikinsa, gaskiya he's very committed to his job.Dr Haseeb ya maida kansa bawa wajen geagwarmaryar ceton rai ko neman lafiyar duk maras lafiyar da aka kawo asibitinsa. Wata damuwa da Alh Shatif ya gabatarwa Daktan shine cewan basu San kowa a garin Kano ba labarin asibitin kawai suka ji ya dauko matarsa suka yo gaba, tunda satinta biyu da yin hadarin, bayan kukkujewa da tayi nan da can ne sai ta fara sumbatu Kuma, barci yai kaura daga idanunta, sai anga sauki abu ya dawo, so wasu ne suka basu shawarar su kawota wajensa. Daktan yace ksr ta Sami damuwa harkar accommodation, asibitin sunyi tanadin guest house dab da asibitin saboda irin hakan.Batun hidimar abinci kuma zaisa matarsa ta aiko. Alh Ahmad Shariff ya fara zuba godiya Daktan ya katse shi cewan musulmi duk inda yake danuwan musulmi ne, Kuma shima an taba taimakonsa. 15/09/2020, 18:50 - Anty saliha: ...RAHIMA..doc by jami 36 Rahima ta kalli agogon dake manne a bangon dakinta, dare ya fara tsalawa, karfe daya harda wasu mintoci amma shiru maigidan bai dawo ba.Ta saki ajiyar zuciya auren likitan kenan, wata rana ma can zai kwana that's why ake son matansu su kasance masu hakuri da dangana. Ta juya gefe, ita ta rasa dalilin da idanunta suka kekashe ta kasa barci bayan na tattare da gajiya. To me ya hanata barci kuwa illa tunanin da ace maigidan bai fita da yanzun suna tare watakila ma a shimfidarta? Oh ni Rahima, shin Ina kunyar Ya Haseeb ya tafi ne har nike irin wannan tunanin?Anya kaunar da nike masa zata boyu kuwa? Barci ya fara fisgarta tana kokarin bude idanu amma ina! Sarkin karfin ya dauketa... Har ya shigo cikin gidan ya shiga dakinta bata sani ba, barcinta yai nisa, yayi kamar ya tasheta ya fasa. Duk da barci take ta Kara yi masa kyau da kwarjini, bai iya tantance tsananin bugawar da zuciyarsa keyi, shin dalilin matsanancin sha'awarta ce ko kuwa so ne ya fara surfafar zuciyar? Tunda baida amsa a lokacin, ya matsa kusa yasa hannu ya gyara mata hannunta data lankwashe tareda shafa kanta a hankali. Jikinta yai dumi amma ba na rashin lafiya ba, duk yadda yaso ya daure abu ya faskara ya duka yai kissing chicks dinta, ta dan motsa kadan taci gaba da barcinta kan dole ya cije ya nufi dakinsa ya kwanta. Qira'ar qur'anin da take yi ya bashi tabbacin ta jima da tashi, shima sai da ya kare nasa ya nufo dakinta yai zaune bakin gadonta yana jiran har ta kammala ta shafa adduointa sannan ta mike cikin natsuwa ta isa dab dashi ta tsugunna. "Ina kwana, ya kaga mai jinyar?" Ta fadi a hankali. "Lafiya lau, jiya ban dawo ba sai muka tabbatar bata cikin wani hadari, insha Allahu zata sami sauki." "Ubangiji ya amince ya bata lafiya, nima da har na tsaya jiran dawowarka unfortunately, barci barawo ya dauke Ni ban farka ba sai asubah." "Yes ai ma shigo na samu kinyi nisa sai na kasa tashinki saboda you were sleeping like a baby, looking so beautiful and innocent, naji kamar in zauna kawai in yita kallonki." Kunya ya kamata "Lah daka sani ka tashe Ni... Ba wani jin kunya ya kalleta yace "Kinsan abinda zai faru da na tashe ki?" Ta mutu a zaune.. Wai me ke damun Ya Haseeb ne yake zaro zancen da bai dace ba? Nauyin jin kalamansa yasa ta kasa dagowa. Ya girgiza Kai yana murmushi yace "Ba ni da amsar maganata kenan?" Ta daga kai alamun amsar sa. Yace "Hhmmm ashe zan zo in fara adduar Allah ya rage miki jin kunyar saboda idan baki saki jikinki dani ba ya za muyi zaman auren kenan?, I mean if you're not free with me ya Zaki lakanci halina, in san naki Kuma?" Tace "I will try my best." "Yauwa haka ya kamata, yanzun taimakonki nike nema kan patient din da aka kawo jiya.... Ya zayyane Mata halinda suke ciki da irin taimakon da yake son yi musu." Rahima tace "Ba damuwa Allah na taimakon Wanda ya taimaki wani. Bari inje mu shirya musu breakfast sai in shirya mu tafi tare?". Ya amsa "Okay, godiya nike." Sun isa asibitin kenan Allah ya nufi Hjy Fatima da farkowa daga barci daidai maigidanta Alh. Ahmad ya shigo cikin asibitin suka hadu da babban likita a nurses station, ya mikawa likitan hannu suka gaisa, Daktan ya tambayesa "Ya kwanan patient din tamu?" Alh. Ahmad ya washe baki yace "Ai naga abin mamaki jiya kamar wani magic wallahi tunda kuka gama dubata baiwar Allah nan ta samu natsuwa tayi barcinta lafiya, ba buge,-buge, ba wasu 'yan surutai da take yi a can inda aka fara dubata. Dr Haseeb yace "Alhamdulillah, yanzun tunda mun samu tayi barcin fiye da awa shidda, brain din ta zama relaxed, yau zamu sake sakata cikin na'ura mu bincika sosai ko da wata matsala a San matakin da zamu dauka, idan iyakar problem din da muka riga muka gani jiyane kawai, mun shawo kanta tun jiya din ma said mu jira karin samun sauki, Allah yasa mu dace." Ya amsa "Ameen Dakta, muna fa godiya sosai Allah ya Kara hasken ilmi." Yana magana ya kalli Rahima yace "Ikon Allah ga wata kamar 'yaruwa." Dr Haseeb ya kalli matarsa, ba shakka irin shigar nata ce tayi ta nannada lapayya, tayi kama da bare-barin, shi ko bata saka shi ba takan yi masa kama da matar kasar Chad. Ya sake bin ta da ido, ya juya yaga yadda Alh.Ahmad ke wani washe baki, kishi ya turnukoshi har yaji mamakin kansa, ya gyara murya yace "Wannan amaryata ce Alhaji ta shigo wajen ita patient din ce at least taji ko akwai abinda suke so tunda ku baki ne." Alhajin ya gintse dariyarsa har dai daya lura da canjin fuskar Daktan, ya gyara tsayuwarsa yace "Masha Allah, Allah ya sanya alkhairi da albarka cikin auren, sannu Hajiya." Ta amsa a darare saboda itama taga yadda mijin nata ya hade gira, miskillancin ya taso kenan ta fadi a zucci. "Ina dakin da pateint din take?" Ta tambaya aka nuna mata. Soyayya gamon jini, haka Allah shi ke hada mutaneya sanya kauna tsakaninsu. Mintoci kalilan da shiga Rahima wajen Hjy Fatima Allah ya hada jininsu,bayan sun gaisa suka Dan fara hira a hankali kafin su saki jiki

Table of Contents

Chapters

66 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66