Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 33

Chapter 33

Rahima Book 1 Complete Hausa Novel 1,205 words 0 views Progress saved
Download Book

tana kwanciya miki a dak?" Hjy Lami ta kada Kai "Yadda ka ganta hakan na ganta ko gaisawa ba muyi ba." Yace "Mutumiyar banza kina nufin kin kwaso kafafunki ne kinzo muyi miki mene, mu hana sa aure? Wallahi Mamana (haka yake kiranta saboda sunan mahaifiyarsa yasa mata) kin ban kunya, ban taba tunanin ba zaki zauna gidan aureki cikin mutunci ba,yarinya kin zama sai kace goyon arna?" Hjy Lami tace "Ya za ayi mijinki ya kalleki da mutunci bayan kin zama tamkar maras mafadi?" Ta saka kuka "Wallahi Mama Haseeb kazafi yake mini." Alh Muhd ya sake daka mata tsawa "Rufa min baki ko in tashi in tattakaki, wallahi muddin baki canza dabi''unki ba daga yau mun sa kafar wando daya ni dake, bar ganin na sake miki ina ksunarki, zata koma kiyayya tsakaninmu Kuma kin sanni sarai kamar yunwar cikinki, wallahi ko ke kadai na haifa ina iya yafeki har abada don banga amfaninki ba." Hjy Lami ta kalleta cikin bacin rai tace "Dubeki yarinyarki dake kin bata rayuwarki da kanki ga kinan duk kin jeme kin lalace, Kuma da kike cewa kazafi likitan ke miki su mutanen duniya da kike mu'amala da kawayen banzan da kike hulda dasu duk kazafin ne? Duk inda kika shiga ana ga 'yar wance da wane." Alh Muhd yace "Dalili kenan da muka bashi goyon bayan ya auro mai mutunci tunda ke kin zubar da naki, idan kinga ba Zaki iya zama dashi ba ga hanya nan bude to banga amfanin zama da igigiyar aurensa a kanki ba, sai kije kiji da zunubi daya." Uwar ta fashe sa kuka "Alhaji kalli yarinyar nan ka gani ba abinda ta sawa gaba sai burin duniya da kyale-kyale, dan rayuwar da take takaitatta. Wai don Allah wane irin gata ne ba a nuna miki ba? Me kika nema kika rasa a gidanku ko na mijinki? Allah ya hore dukiyar da ake taimakawa wasu ma, to me kike nema ne?" Maimakon ta nuna alamun nadama sai ta dauko wani zancen da bai danganci fadar da ake Mata "Mama ni gaskiya ba Zan zauna da kishiya ba, kishiyar ma yarinyar data san sirrina, bayan duk wata takama da Haseeb ke yi da wani ji da kai, mahaifina ne silar duk abinda ya samu, duk abinda yake takama dashi Kai dinnan Baba kaine sanadin, ko yana nufin anci moriyar ganga ne za a yarda kaurenta, to gaskiya Baba da sake... Bata ga mikewarsa ba, ji tayi kawai an dauketa da tafi ta kifa kasa, ya bita ya taka yana zagi, uwar ma ta rufeta da duka, Nan ta fara kwarma ihu sauran matan gidan suka taru don cetonta.. Da kyar da rarrashi aka kwaceta, ko kafin ayi haka fuska ta kumbura jiki ya murzu da duka. Alh Muhd ya fara haki, jiri ya kwashe shi, matan suka tareshi, akayi hanzarin dauko masa maganin hawan jininsa aka bashi yasha kana suka kamashi ya koma daki ya kwanta. Hjy Lami ta dawo dakinta ta cimma 'yar nata kuka tace "Ya jikin Baban?" Ta kalleta ta watsar "Tashi ki bace min da gani, ina ruwanki da jikinsa? Ai kinsan yanada hawan jinin don kece sanadi, to ki dage ki zama kece ajalinsa." Ta Kara fashewa da kuka "Don Allah Mama ku yafe min, Allah zan daina komi, bacin raine yasa Ni fadin wannan maganar." "Da gangar kika yi tunda an Sha gargadinki kan furucin da kike yi, yau kika yiwa mijinki gorin? Maras tunani, da kike fadin ubanki ne silar arzikinsa yanzun hidimar da yake mana ya zama ke Kika sa shi? Yarone dan halas da yasan darajar iyayensa da naki." Ta daga kai "To Ni Mama so kuke in zura masa ido Kan batun aurensa?" "Ah ah kike kiyi abinda zaki iya kinji zabin da muka baki ai. Ni tashi ki fita min a daki, ki Kuma dauki yaranki ki maida gidan ubansu tunda baki San ciwon kanki ba, albasa bata yi halin ruwa ba." 10/09/2020, 18:03 - Anty saliha: ....RAHIMA...doc by jami 25 Zuwaira ta tabbatar wa kanta ba zata sami yadda take so wajen iyayenta ba, saita canza shawara ta tuntubi Husaina daya daga cikin kawayenta a tunaninta ita din ce kadai zata iya taimaka mata warware matsalarta. Tafiya mikakkiya ta isa gidan Husaina dake gadon albasa, Sha daya saura na safe ta matsa kararrawa, saurayin dake mata wanki da guga ne ya bude mata kofar ta shiga yana gaisheta ta tambayesa "Ina Hajiyar?' "Tana ciki." Ya amsa. Kai tsaye ta wuce bedroom din Husaina ta taras da ita a kwance "Lalle kina jin dadinki, ni ina ga time din barcin safe?" Tayi Mika tace "Zuwaira Wai Ina kika shigane tun safe nike neman wayarki?" Zuwaira ta zauna bakin gado "Kinga ni yunwa nike ji bari in ci abinci tukunna kisha newa." Husaina ta dago ta kalli yanayin fuskarta ta saka salati ,"Ke ya aka yi haka?" Tace "Labarine mai tsawo bari in koshi jikina har rawa yake, rabona da abinci tun jiya wajen bukin nan." Cikin hanzari ta kira yaron gidanta ta umurcesa yaje ya hado musu breakfast, ya fita da sauri." Zuwaira ta kalleta sama da kasa "Haba Husaina dubi shigarki fa sannan kika yaron gidanki har cikin bedroom dinki?" "Look Zuwaira nu dake duk kanwar ja ce fa, jirgi daya ya kwaso mu, ya saba shigowa sai me?" Ta gyada Kai "No duk rashin da'ata ba zan bar wani kato ya shigo min cikin dakin barcinmu ba don na dauke shi matsayin *sacred secret place* "Hhhmmm ba dai kin koshi ba? Mu bar zancen mu koma na dalilin nemanki, shin ina Alhajin da yaso like miki wajen bukin nan, ya dameni in bashi lambar wayarki, ya isheni da naci that's why na kiraki tunda safe, me ye ra'ayinki?" Tayi saurin girgiza Kai "Raba da wuya kinji, in don kayan da muka ce muna so ne zamu sara ya taimaka mana ya bar abinsa, irinsu sun cika mita kawai ya hana min sikit.. Ni dai yanzun Kinga fuskata ko? Wallahi aikin Baba da Mama ne suka taru sukai min sukuwar Sallah don nace ban amince Haseeb yai aure ba." Ta furzar da ruwan da sanyin data kurba ta bugi kirji cikin tsoro "Dr Haseeb zai yi aure? Wonderful... "Kin ganni nan fa cikin tashi hankali nike, that's na garzayo bidan shawarki don iyayena sun bashi go ahead." "Yo inya sakeki ba kin huta ba, ga masu sonki ido rufe?" Tace "Sakin bai dameni ba, hakan nike so Amma wallahi ba zan bar gidansa kafin aurensa ba wannan yarinyar ta dauka ta isa ta koreni, sai tazo ta zauna na nuna mata ruwa ba sa'an kwando bane, wutsiyar rakumi tayi nisa da kasa." Husaina tace "A ina ya samu matar ne?" Ta amsa "Matar kaninsa daya rasu dinnan nan, shine iyayenta suka cusa mata ita don sun ga da maiko." "Tashin hankali inji Husaina ta Fadi cikin karaji "Yarinyar dake teaching makarantar kurame?" "Yes ita, wani abu ne?" Ta kada Kai "Yadda nike ji yarinyar nada kamun Kai da rike addininta, Kinga ko nan an samu difference. "Wannan lalurar tace Husaina ta Fadi tana daga kafada irin bai dameta ba dinnan, fada min meye shawara yanzun? Tayi shiru tukunna kafin tace " yanzun Kam kwantar bauna za

Table of Contents

Chapters

66 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66