Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 56

Chapter 56

Rahima Book 1 Complete Hausa Novel 1,205 words 0 views Progress saved
Download Book

goyon bayanku nike bukata sannan ku tayamu addua." Hjy Kaltume tace "Shikenan Allah yai miki albarka ya cika burunki na alkhairi. Daktan ya wani kalleta yace "Naji duk kun goyi bayanta ne, to ni kam ina nan kan bakana, idan Kuma kun matsa na amince to Kar ayi kuka dani idan wani abu ya taso nan gaba " Mahaifiyarsa tace "Wannan ne baka isa ba, ka tara 'ya'yan mutane kace ba ruwanka.". Rahima tace "Rabu dashi Hajiya naji sharadinsa na dauka Allah ya kama mana." Ya sake kallonta a fusace yace "Yanzun sai ki fadi inda kuke son ku zauna tsakanin Dorayi da Galadancin." Ta girgiza Kai "Ba ni da wannan matsayin, Kai da Aunty Zuwaira kuyi deciding Ni 'yar amshin shata ce.". Ya juya gasu Hajiya "Kunji amsar ta ko?" Hajiya ta gyada Kai "Laifi kake son Dora mata dai amma gaskiya ta fada, tabbas zabi na gareku, ta ba Zuwaira girmanta da Kai kanka." Da yaga ba zai samu goyon bayan da ya zata ba dai ya amince cike da fargaba. Yayi deciding kara gyara gidan da Rahima take saboda akwai filin da za a dora wani ginin sosai. Ba bata lokaci aka fara aikin sake tsara gidan Daktan don zaman iyalinsa. 19/09/2020, 13:57 - Anty saliha: ...ˆRAHIMA..doc by jami 46 An kammala komi na gidan Dakta har gashi Uwargida Zuwaira da tawagarta sun rakata tarewa a nata bangaren. Yanuwanta da suka san mutunci sun shiga sun gaisa da Rahima aka taba barkwanci suka musu addua suka tafi, kawayenta kuwa sai shirmen da suka saba, hatta da falon Zuwaira Saida suka leko yanayin tsarin da Rahima ta yiwa nata suka dawo suka kwatanta irinsa, suna yo suna yar da maganganu don dai neman jidali. Bata kula ba balle tasan Allah yai ruwan tsironsu, to Rahima a banza take miskila? A wannan ranar Zuwairar ke da maigidan yadda ta shirya saboda Wai ta nunawa Rahimar ita ke da gida da maigidan ma gaba daya, to wace take yi dominta bata san arziki na bori ba. To idan ba shiririta da neman zubar da aji irin na Zuwaira ba, kowaccensu sashen daban, sai ma kaso sanin halinda yaruwa ke ciki ne zaka leka inda take, sai kuwa idan sun hadu a general parlour na gidan, kowacce tana da masu aikinta to me ye na hana Kai sukuni? Dawowar su Zuwaira yasa yaranta suka Kara shakuwa sa Rahima saboda tana jansu sosai a jikinta, ta hanyar kulawa da duk bukatocinsu ba gajiyawa, ga kokarin tarbiyyarsu da take yi tareda danta, to jama'a ko yaro yasan mai son shi. Zuwaira bata kaunar kusancin yaranta da Rahima ko miskala zarratin, da taga tayi kokarin rabasu ya faskara sai ta shaidawa abokiyar shawarar nata. Husaina ta buga kirji tace "Zauna ki saki baki galala kamar wata sauna bayan ta mallake miki mijin ta hada da 'ya'yanki kina zaune sokoko ta mallake zuciyar yaranki tas, an fada miki da bakin hura wuta wannan yarinyar ke zaune a gidan Nan?" "Da alamun kamshin gaskiya a batunki Husaina, nima zargina kenan don wallahi ko kaffara ba zanyi ba, ba haka kawai Dakta ke rawar jiki da ita ba, ke baki ga yadda take juyashi ba fa, Daktan da bana ganin tsadadden murmushinsa sai na sha ruwan dala amma ko waya yake da ita haka zaki ga yana wani rausayar da Kai Yana zuba murmushi sai kace wani sick lover boy." Husaina ta kyalkyace da dariya tace "To ai ba murmushinsa kadai ba shi kanshi tsadadden ne Zuwaira, yanzun dai meye shawara?" "Kinji kuma, ke din dai nike saurare." Husaina tace "Ya zanyi dake yanzun,kince ke ba zaki shiga malamai ba, to ki zauna ta saki a tafin hannunta ta murza ta juya son ranta, mu dai idan da malamai da bokaye a duniya mun gi karfin tsara balle irin wancan da aka dauko miki, ke Kika yi sake tun farko amma ai ba ajinki ba ce." Zuwaira taja dogon numfashi "Ai yanzun dole mu san matakin dauka that's why na neme ki." "Karki samu damuwa 'yaruwa, kin yarda ko wane irin taimako na kawo miki zaki yi amfani dashi ko?" "Me zai hana kuwa Husaina shakkun me kike?" Husaina tace "Ai dole in jinjina kar kisa in kashe kudina a banza alhalin kin san samun su da wuya." Zuwaira tasha mur tace "Ke fa problem dinki kenan in dai batun kudi ya taso alhalin ni Ina kashe miki kowacce irin lalura ba tareda jin kyashin komi ba, ke kuwa in dai za ki yi min Abu sai kiji tamkar naman jikinki zaki diba." Nan take Husaina 'yar bariki ta share wannan batun cikin dabara tunda tasan gaskiya aminiyarta ta fadi tace "Wasa fa nike miki, amma da gaske kinsaj business din mu yaja baya Kuma mijina ba irin naki bane da yake sakar miki dala kina fantamawa yadda ranki ke so, nasa Dan banzan makon tsiya, hannun nan nasa a dunkule tamkar na "yan dambe." Zuwaira ta tuntsire da dariya "Oh sharri ma za kiyi masa Kuma? Ai kuwa Yana kokarinsa shima.".. Ta tabe baki. "Me Kika sani game da mugun halinsa, ke ni fa auren ma na gaji har na nemi ya sauwaka min, in gutsire igiyar auren in yi gaba in sami Wanda ya dace dani." Ta zaro idanu "Ke Husaina ki rufaea kanki asiri, Ina ke Ina wani rabuwa da mijinki yanzun, wa zai wani aureki yanzun bayan ga 'yan matan Nan ma suna yawo a titi a mashinshini?" Ta gyada Kai "Ai da kika ganni da agenda ta, na riga na shirya komi jiran lokaci nike in gabatar miki.." "Toh! Al"amarin ba sauki kenan to Allah ya nuna mana alkhairi." Tace Amin "Bari inyi azama Kar Malam ya fita sai kin ganni." Tsakanin matan Daktan biyu zama yaki dadi,ta kowanne bangare Zuwaira bata da dama. Matsalar farko da Rahims ta fara karo da ita daga uwargidan nata itace gasa, Zuwaira irin matan nan masu shegen gasa, duk abinda taga Rahimar tayi sai ta kwaikwaya, ko silifas ta lura Rahima ta canza itama saita saya, balle a kaiga su kayan jiki ko na gyaran gida. Wasan wasa rashin mafadi, gasa idan ba na nuna bajinta wajen bautar Allah bane ya zama shirme. A ka dawo Kan abinci, a kullum mai aikin Zuwaira na yaeon gulma sa sunan tana zuwa wajen Uwale ne amma su sun San yar leken asirin uwardakinta ne, duk abinda yazo taga ana girkawa a sashen Rahima zata nade taje ta fesawa uwardakinta musamman idan Daktan wajensu yake, ita Kuma ranar nata girkin saita wanke tukunya ta kwaiwayi irin Wanda su Rahimar suka yi ta sake dafawa. Sai ayi rashi dace, Wanda akayi dominshi ba zai ci ba, Zuwaira ta fara bala'in hatta abincin ta ya daina ci sai na Rahima. Tunanin bai kawo mata dalilin rashin cin bai rasa nasaba bai dade da cin irin nau'in abincin ba kazaliza method da aka hada ma ba guda ba. Rahima ta gaji ta yanke shawarar aikawa Zuwaira ko me ta dafa. Uwale ta kalleta galala tace "Ni fa kina bani mamaki, yaushe ne Zaki yarda da kishiya har dai wace bata kaunarki har da batun Kai Mata abinci? Kin san ba zata ci na saidai ayta asara kawai. Rahima tace "Uwale kenan

Table of Contents

Chapters

66 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66