Chapter 38
Chapter 38
kyau tun laraba ake ganeta, wallahi haka nake son namiji yasan mutuncin 'ya mace. Rahima tayi dariya "Ai ko mazan namu ana samun wadanda basu San darajar macen ba, da na dauka jahilci ne yasa wasu mazan ke maida matansu tamkar jakuna ashe ba hakan bane, ko a birnin haka wasu mazan suke, kiga namiji bai san mutunci da darajar matansa ba, mace bata isa yai shawara da ita ba, don a ganinsa shirme ne, ke wani fa ya dau mace tamkar Mai karamar kwanya ce don haka baki Kai matsayin da zai fada miki wasu sirrinsa ba, sai kiji wani na kiran matarsa Wai dabba ko jaka don rashin sanin kimarta da rainin hankali, amma bai hana ya nemi biyan bukatarsa, bayan haka sukan manta mace dai ta haifesu suke mata isgillancinka bayan Allah ya daukaka darajar martabarta, saboda duk inda namiji ya Kai da mukaminsa, sarauta, jin Kai dole macen yake dawowa. Uwale tace ai baki ma san wani abu ba, mijina madokine, kina masa laifi komin kankantarsa sai ya jibgeki, shi bai kyautata yadda Allah yace ba, bai baki isashshen abinci ba, ba suturarsa fa sai an bamu kwance nida yara, ya rinka hura hanci yana tafe yana busar iska da shan kamshi sai kace Wanda aka kadawa tambari, dare nayi yaje gashi nan bisa kanki, kina gardamawa ya kile ki yayi abinda yake so, ya barki da tsamin jiki ga yunwa dake kwakularki tunda ba ki ci abinci ya isheki da daren ba, gari na wayewa ki shiga fafutukar nemawa yara kalaci. Rahima ta kyalkyace da dariya tace "Uwale Kar kisa cikina ciwo don Allah don Allah ki daina maganar mamaci haka, ki yafe masa tunda ma ai kusan lefinki ne, wa yace ki rinka gardama bayan ance idan baki amince ba kuka kwana yana fushi dake mala'ikun rahama tsine miki za suyi, Allah yai fushi dake." "Hhmmm Hajiya na sani amma sai aka ce suma kar su kyautata mana su sauke hakkokinmu a kansu, kullum ko wa'azi aka tashi sai dai kiji ana fadin mu mata mu sauke hakkokin mazajenmu, su Kuma su rinka tinkaho suna gadarar aljannar mu na karkashin duga-duginsu, suna takamar tunda ance matarka gonarka ce ka zo mata duk lokacin daka so, ko a saman rakumi ne." Rahima ta Kara kyalkyacewa da dariya "Shin Uwale zaki bari mu karya mu kimtsa ko sai kinsa cikina ya cika da dariya tukunna?" Uwale ta kece da dariya itama "Da takaici ne Hajiya.". Tace "Kuma na yarda da batunki, ya dace maza su rinka bamu darajarmu da Allah ya bamu su daina raina hankali da tunaninmu, mu ma muna da kaifin hankali da zurfin tunaninmu, mu ba dabbobi bane mun san ciwon kanmu mun san ya kamata, mun san hakkinmu, mun san nasu, ya dace ace yadda muke kokarin kyautata musu suma su kyautata mana don mu kara ingantuwar zamantakewar aurenmu. Uwale tace "Hakane wallahi,idan muna kokartawa zamu rinka ganin canji, Allah ya taimakemu. Bayan sun kammala kalacin safe, Rahima tayi wanka ta tsala kana ta rinka zagaye sabon gidan nata. 29 Gidan Rahima sashe-sashi biyu ne sai fili daga can gaba, ginin kansa ya tsaru sosai, ga furanni masu fitar da kamshi daban-daban, tun kafin ta tare saida aka yi mata saukar qur'ani da adduoin neman tsari da albarkar zaman baki daya.. Sun gaisa da maigadin Mai suna Mal. Hassan yayinda dansa Haladu ne zai rinka yi musu wanki da guga da share-sharen waje da gyaran shukoki. Sha daya amaryar ta fara baki, zuwa azahar sai ga uwargida Zuwaira da tawagarta sun danno mata baya, suna mata kirari "Sai ke uwargidan likitan likitoci.. Tayi musu maraba cikin ladabi, ta gaishesu suka share, tasa Uwale ta kawo musu kayan motsa baki dasu lemu shima ko kallo balle su dandana sai sakin magana suke. Ba inda Rahima ta burge kowa sai da taki kulasu tayi tamkar bada ita suke maganar ba don ta lura so suke ta tanka su ci mutuncinta, da taga haka maimakon suyi tafiyarsu sai ta mike tace su biyota wai suga cikin gidan, kawayen Zuwaira su bakwai suka bita duu tana gaba suna biye, Saida suka gama zagaye ko'ina kana suka dawo falo ta tsaya a gaban Rahima tace "Miko min key din dakin Dakta sabida Nan ne kadai ban shiga ba." Cikin natsuwa Rahima tace "Kin dai shiga inda suka dace ki gani, inda kike batu yanzun kuwa sai ki jira amincewar mai dakin tukunna in ya dawo." Kawar Zuwaira Hussaina ta girgiza Kai "Lalle yarinyar nan taga gadon barcinki ta rainaki wallahi." Wata cikinsu kuma tace "Ya dace ji nuna mata da gidan da maigidan dyk mallakin kine." Tana wani jijjiga jiki kamar Mai shirin hawa bori tace "Ki kiyayeni wallahi, zaki bani ko sai rayuka sun baci tukunna?" Rahima ta yunkura ta mike tsaye ta bisu da ido tace "Kin ban mamaki Aunty Zuwaira da zaki tsaya kadangarun bariki na hura miki m wuta a gidanki. Da akwai girma da arziki watakila in daure in baki keys that's in ke kadai ce ma, amma yanzun ba Zan iya ba, kiyi iko da naki gidan inyi da nawa, abu na karshe Ina rokon don Allah ki kwashe tarkacenki gayyar na ayya kuyi gaba. Daga yau idan ba girma da arziki zai kawo ki ba please Kar ki sake zuwa min gida, nagode da ziyara, Kuma a rinka taka tsantsan da duniyar nan tamu mai halin Dan mangwaro, sai kana shansa dadi ya fara tsumaka ya subuce maka, hakan nan ita din rawar 'yan mata ce, na gaba Kan koma baya... "Tafdijan! Lalle wuyar yarinyar nan ya isa yanka, to ke Kyaleta za kiyi Zuwaira ta rainaki a gabanmu?" "Zuwaira ta cika tayi fam tace "Wai ita 'yar gani lasheni.. Daya kawar tace "Ba ki sharara mata mari ta gane banbancin aya da tsakuwa?" Kamar go ahead kawai take jira ta daga hannu zata kaiwa Rahima mati, tayi wuf ta rike hannun cikin sa'a tana girgiza kai "No Aunty Zuwaira Kar ki fara, duk haukar da za kiyi zan kyale but Kar kiyi mistake din hannunki ya Kai ga jikina, don ni din Dan hakin daka raina ne, Ina iya tsone idanunki." Zuwaira tayi kokarin kwace hannunta ta kasa, kawayen nata na ganin haka suka tasowa Rahima haikan, ta kallesu a wulakance tace "Duk wace ta matso kusa dani sai buzunta." Suna cikin haka tawagar iyalan gidansu Haseeb dana bangaren su Haj. Kaltume suka shigo, kanwar Hjy Kaltume mai suna Hjy Iya ta rafka salati sauran jama'aa suka dauka suma "Me zan gani Rahima? Ta saki hannun Zuwaira tace "Tambayi Aunty Zuwaira... Ta juya wajen Zuwairan tace "Ya kike son zubar da girmanki, anyi bukin nan an watse lafiya, meye na tayar da husuma, tunda Allah ya hadaku zaman tare ba sai kuyi hakuri da juna ba, mijinku na can na nema muku abin rufin asiri, ku kuna nan gaban jama'a kuna zubda mutuncinku, ina amfaninsa. Zuwaira ta figi gyalenta ba tareda Kara cewa komi tace wa mutanenta "Mu tafi, ai zamu sake dawowa." Suna fita mutane suka shiga tseguminsu, Rahima ta katse su "Ni dai ku daina cin namansu din Allah, kuyi musu adduar shiriya idan zaku iya, idan ba zaku iya ba kuyi shiru." Da dare ne Maryam
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66