Chapter 4
Chapter 4
Na gama zama dake ki tafi duk inda za kije mara mutunci." "Baba kiyi hakuri tsautsayine kin san dai tunda kike aike na banta'ba zubar miki da kudi ba wannan ma kaddara ce." Tace." Ban san kaddara ba na fada miki na gama zama dake ki tafi can gidan Ubanki duk abinda za su yi miki dama tausayi yasa nake rike dake to tunda kin zama munafuka zama na dake ya 'kare Kije duk abinda Talatu za tayi miki ba zai dameni ba. Ta durkushe a gurin tana kuka da rokonta tayi hakuri tayi kunnan uwar shegu da ita kicin ta shige ta barta a gurin, ta kalli Saliha da fadin." Ki sanya baki tayi hakuri kinji." Ko kallonta ba tayi ba ta cigaba da abinda take, A fusace! ta fito daga kicin din ta nufi dakin sai gata ta fito da bulala a hannunta ta riga ta san idan tazo babu abinda zai hana ta doke ta. dan haka da gudu ta ruga a guje ta fita daga gidan tana jin lokacin da ta sanya sakata ta koma ciki tana surutai. Babu yanda ta iya haka ta kama hanya domin tafiya gidan mahaifinta dake can Ja'in Tafiyar 'kafa za ta yi tunda babu kud'i a hannunta gashi akwai tazara mai tsayi tsakanin Gadar salga da Ja'in. Koda ta fito bakin titin hankalinta na gurin zamansa, babu shi a gurin sai tarin tarkacensa , sai ta tsinci kainta da kasa tafiya har sai da ya dawo da ledar biredi a hannunsa taga ya shige karkashin motar ya zauna. Ajiyar zuciya ta sauke cikin zuciyata Tace."Watakila wani ne ya tausaya masa ya siya masa biredin. Sai da taje Sabon titi na gidan 'kankara a kasa kafin ta samu wani d'an kirki ya taimaka mata ya rage mata hanya. *MAJANUNI!* (The Unknown Rich Man) NA *BINTA UMAR ABBALE🍒* MANAZARTA WRITES ASSO.. ____ Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K7QH4idftZS5fSw7m2Rueb Kuyi join domin samun damar karanta littafi na d'aya. _Gaisuwa ta karamci zuwa ga iyaye na biyu._💯 *FATIMA MUSA (MOMY NIJAR)* Tare da *USAINA ABDUL-MALIK KAITA (HAJIYA BABBA)* *5&6* Ta zo shiga gidan kenan ta yi karo da 'karamar k'anwarsu Walida tana d'auke da markad'an awara a kanta. kallon juna su ka yi sai kawai yarinyar taja tsaki ta wuce ba tare da tayi mata magana ba. Idan da sabo ta riga ta saba da irin wannan wulakanci da 'kas'kancin da 'yan uwanta suke mata duk da cewa itace babba a cikinsu amma mutum d'aya ce take ganin girmanta. Gabanta na fad'uwa tayi sallama cikin gidan. Talatu tana kicin ta baza kwanuka tana rabon abinci yayin da Hadiza babbar 'yarta ke yanka musu salak da tumatur. ita kuma Jamila tana shanya kayan makarantarta akan igiya. Itace ta amsa sallamar fuska a sake tace."Auntymu kece ki ke tafe da wannan ranar.?" Hadiza ta kalleta a watse ta mayar da kanta kasa tana cigaba da gyara salak din dake gabanta. Jamila tace."Talatu ga fa Aunty Shahida tazo." Ba tare da ta juyo ba tace."To Ubanta zan yi mata kome?" Jamila ta girgiza kanta ba tace komai ba taja hannunta suka shiga daki tana 'kokarin kawar da 'bacin ran dake damunta, ta tsani halin ko in kulan da mahaifiyarsu take mata a ganinta Shahida abar tausayi ce duba da maraicin da take ciki bayan haka kuma akwai nakasu na rashin ji a tattare da ita, babban damuwa yanda mahaifinsu yayi shakulatun 'bangaro da lamarinta da kuma lalurarta a matsayinsa na mahaifinta baya taimaka mata da komai gabad'aya ya sakarwa kakarta wacce ta haifi uwarta ragamar rayuwarta, bai san ci da sha da sutturarta ba, Uwa uba karatunta duk be san wannan ba, ta wannan fanni dole a jinjinawa Baba Asabe domin ita d'in maca ce mai kamar maza duk da nauyin ba akanta yake ba amma ta d'auka tana iyakacin 'bakin 'ko:karinta akan yarinyar. Tsaf Talatu ta gama rabon abinci amma babu rabon Shahida a ciki duk da cewar lokacin da ta zo gidan bata gama rabon abincin ba idan da ta yi niyyar sanya mata kwano zata san yanda tayi ta fitar mata da rabonta amma k'emagadas! tayi mirsisi ta rabe abincin kaf ta kira kowa ya d'auki nasa. Jamila a sanyaye ta nufi dakin da nata kason a hannunta. Kamar ta san niyyarta sai ta kira sunanta, taja ta tsaya tana kallonta, fuska a tsuke tace." Ki ka shiga da abincin nan ku ka ci tare sai na tsine miki albarka." Dama sarar ta kenan daga zarar 'ya'yanta sunyi mata laifi sai tace zata tsine musu. A marairaice tace."To yanzu ita Shahidan haka zata zauna Talatu kada fa ki manta itama tana da hakki a gidan nan tunda duk ubanmu d'aya." Ta ciko hannu da shinkafa 'yar manja wacce taji salak da yaji ta watsa a bakinta tana taunawa ta ce." Kafin ki san haka na rigaki sani ban yi niyyar bata abincin ba shiyasa nayi rabo babu ita idan kuma ki kayi wasa wannan na hannun naki zan k'wace na bawa almajirai kema kiyi asara." Hadiza ta kalleta da fadin." Banza mara kishin uwarta shin har kin manta labarin da Talatu ta ba mu a lokacin da suka zauna tare da mahaifiyarta yanda ta azabtar da ita amma shine saboda rashin kamun kai kike tausayin abinda ta tafi ta bari ai wallahi ni da wannan kurmar yarinyar har abadah." Jamila ta girgiza kanta da fadin." Ke Hadiza jahilci ne yake damunki wallahi ni ina ruwana da irin zaman da su ka yi kawai 'yar uwata na sani saboda duk rintsi ba'a sanjawa towo suna Shahida 'yar uwarmu ce dole ko mun 'ki ko mun so." Hadiza ta fusata! ta hau d'ura mata ashar wai ta kira ta da jahila. 'Kokarin tashi take taje inda take tsaye ta doke ta uwar ta hana ta. Sallama ya yi cikin gidan yana sanye da manya kaya sabuwar shadda mai uban surfani, kansa sanye da hula zanna bukar idan ka ganshi sai ka dau'ka wani hamsha'kin mai kud'i ne nan kuwa tsabar 'karya ce da fafar tsiya Jamilu kenan wanda abokansa suke kiransa da Ya hajuj! tsabar 'karya da nuna shi wani ne. ya sanya sunanshi ya 'bata a ko'ina ake kiransa da Hujaj! Ya kallesu da fuskar shannu "Menene na ganku a tsaye ke Jamila ya akayi?" Da sauri tace." Baba ka ga Aunty Shahida ce tazo shine Talatu ta raba abinci babu ita wai don na d'auki nawa zamu ci tare shine fa suka had'u suke zagina. Ya gyara zaman babbar rigarshi da fadin." Ina Shahidan take? Tace."Tana daki a zaune.'' Tsaki yaja da fadin." Shige ki je kuci abincin tare." da sauri ta shige dakin. Talatu ta kalleshi da fadin.'' Yau kuma? ba tare da yace mata komai ba ya bude dakinsa ya shiga ya turo k'ofa. Kasan kafet ya zauna ya cire babbar rigar jikinsa, hannu yasa cikin aljihu ya shiga fito da kudi daure da kyaure bandir biyar ne ya zube a gabansa yana wani irin murmushi babu shakka yau kura tayi nama ya tashi da Sa'a ko da yake dama sana'ar tasu ta gaji haka yau kai gobe wanin ka da yake shi akwai nasibi duk ranar da suka buga wasa baya fad'uwa, wasan yau yafi na kullum domin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50